29/09/2021
Kungiyar Karuwai Za Su Shiga Yajin Aikin Gama Gari
------
Shugabar kungiyar karuwai ta africa ta sanar da akwai yiwuwar tatafi yajin aiki na wani lokaci saboda take haqqin karuwai da akeyi a wasu kasashen africa ba dare ba rana.
Kungiyar wacce takeda shakwata a kenya tace a kowanne wata ana kashe mata membobi tsakanin mutum biyar 5 zuwa mutum goma 10 kasar kenya kadai to ina kuma idan ta bincika adadin wanda ake kashewa a kasashen africa.
Lamarin da shugabar gamayyar kungiyoyin ta karuwan mai suna grace kamau ta fassarashi da tauye haqqin kilakin.
Kungiyar ta sanar da zata shiga yajin aikin mako guda domin gargadi har sai andawo musu da martabar su.
Kakakin kungiyar wato dan daudu gideon yayi kira ga membobin na kungiyar karuwan da masu lasisi harda ma marar lasisin dasu kauracewa gidajen shakatawa, otel otel da duk wajajen cin abinci domin tafiya yajin aikin na mako daya domin ganin hakar wannan kungiya ya cimma ruwa.
Tuni dai rahoto yazo mana cewar kungiyar maza bata gari ta bukaci ganawa da shugabannin kungiyar ta karuwan domin ganin sun janye wannan kuduri nasu.