26/02/2025
BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA MAI GIRMA SHUGABAN KASA, SANATA BOLA AHMED TINUBU
MAI GIRMA SHUGABAN KASA,
Ina gaisheka da girmamawa, a sunan Allah Madaukakin Sarki.
Bari in fara da taya ka murna kan tafiyar da ka yi zuwa yanzu. Ko da yake tafiyar ba ta kasance mai sauki ba, abin farin ciki ne ganin cewa har yanzu kana aiki tukuru domin jagorantar jirgin kasar Najeriya bisa tafarki mai kyau. Bisa wannan dalili ne na yanke shawarar raba tunanina da kai game da gwamnatinka. Na zaɓi rubuta wasika a fili domin hakan ne kadai hanyar da zan iya isar da sakona gare ka.
Mai Girma Shugaban Kasa, Ina ba ka shawarata ne saboda na yarda cewa kai dan dimokuradiyya ne. Ka san cewa kai da ni mun taɓa tafiya tare a yunkurin tabbatar da dimokuradiyya mai dorewa a Najeriya. A shekarar 1999, ka lashe zabe a matsayin gwamnan Jihar Legas karkashin jam’iyyar Alliance for Democracy (AD). A shekarar 2003, an sake zabeka a karo na biyu karkashin jam’iyyar. Haka nan, a shekarar 1999, ni ma na zama gwamnan Jihar Sakkwato karkashin jam’iyyar All Peoples Party (APP), sannan na sake samun wa’adi na biyu a 2003, karkashin sabuwar sunan jam’iyyar, All Nigeria Peoples Party (ANPP).
A 2007, ka koma jam’iyyar Action Congress (AC) domin ci gaba da tafiyarka ta siyasa, yayin da ni kuma na kafa jam’iyyar Democratic Peoples Party (DPP), inda na tsaya takarar shugabancin kasa a karkashin ta. A shekarar 2011, AC da DPP sun hada kai domin kafa jam’iyyar Action Congress of Nigeria (ACN). Daga nan, a 2014, muka hadu muka kafa jam’iyyar All Progressives Congress (APC), domin samun babbar jam’iyyar adawa da za ta iya kawar da jam’iyyar da ke mulki a wancan lokaci, wato Peoples Democratic Party (PDP). Duk a cikin wannan tafiya, gwamnati da hukumar zaɓe ta kasa (INEC) ba su hana mu kafa sabuwar jam’iyya ba.
Yau, kai ne wanda ka fi amfana daga wannan fafutuka da ’yan siyasar adawa s**a yi domin kafa dimokuradiyya mai karfi a Najeriya.
Baya ga dangantakar siyasa da muka taba yi, ina jin nauyin ja hankalinka ga hal