01/10/2025
*Tambaya Zuwa Ga Maza...*
Ba na goyon bayan mace ta tara samari, wallahi ko kaÉ—an...
Amma yallabai, waccan yarinyar da kake yawan kira da “sweetheart”, “baby”, ko “future wife” aurenta kake so kayi?
Wani shiri kake da shi akanta?
Kana da niyyar kare rayuwarka da ita, ko kuwa lokacinta kake kashewa don jin daÉ—in kanka?
Idan amsoshinka sune "Eh" to shin ta sani? Ka bata tabbaci da kwanciyar hankali kuwa?
Mata ba mu da buƙata mai yawa, so da tabbaci muke nema.
Amma idan muka rasa waÉ—annan biyu, komai na iya faruwa.
Ya kamata ku gane cewa rayuwar mace tana da takaitaccen lokaci a idon al’umma.
Kai namiji zaka iya jinkirta aure har shekara 40, kuma babu mai tambaya sai dai su ce “Lokacin ka ne baiyi ba” ko “Bai da lafiya ne.”
Amma mace fa? Tun da ga lokacin da ta kai shekara 20 ake fara kallonta da kallo biyu.
Ta ki aure? Hmm, me ke damunta? Rawan ido ne? Ko girman kai?
Idan ta haura shekara 30, an fara lakaba mata sunaye:
“Ƴar rainin hankali,” “bata da tarbiyya,” “mai yawan ta zubar,” har ma a ce “ƴar iska”.
Amma wai iskanci da wa take yi?
Da kanta take yi?
Ko da namijin da ya yaudareta da kalmomin "Zan aure ki," alhali cikin zuciyarsa ya san ba haka yake ba?
Wannan mugunta ce.
Ka san ba zaka aureta ba, amma baka janyewa, kuma baka barin wanda zai aure ta ya matso.
Sai ta ƙone da kai, ta ƙone da rayuwa gaba ɗaya.
Wallahi, idan kai kana cikin masu halin nan ka ji tsoron Allah, ka tuba.
Ka tuna fa: ita Ć´ar mutane ce.
Yayar wani ce.
Kanwar wani ce.
Uwar wani ce.
Kuma kai ma wata rana za ka haifi Ć´a mace.
Yaya zaka ji idan aka yi wa Ć´arka irin haka?
Ukty!
Ki ji tsoron Allah, ki rike mutuncinki.
Ke Ć´ace, halittar da Allah ya girmama.
Ya kiyaye ki daga haihuwa zuwa aure, kuma idan babu miji, to akwai yayu, Ć´aĆ´a, ko kanne da zasu tsaya miki.
Kar ki zubar da kanki sabida kalmar "Ina sonki zan aure ki"sai ki rasa komai.
In shaidan ya rinjaye ki sau É—aya, kada ki barshi ya maimaita.
Na farko kuskure ne.
Na biyu ganganci ne.
Na uku kuwa son zuciya ne.