Ɗanja Times press

Ɗanja Times press Page Isma'eel Ɗanja wakilin
“Danja Times Press –
Muna kawo muku sahihan labarai, rahotanni, da abubuwan da ke faruwa a duniya
Gaskiya • Sahihanci • Ci gaba.”

20/08/2026

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Rabiu Muhammad, Abban Zakiya Nura, Mahade Cm Yahaya, Kabiru Adamu, Itz Mentor

🇳🇬 TARIHIN NAJERIYAKafin Najeriya ta zama ƙasa ɗaya, akwai manyan masarautu da dauloli kamar Kano, Katsina, Zazzau, Born...
15/08/2026

🇳🇬 TARIHIN NAJERIYA

Kafin Najeriya ta zama ƙasa ɗaya, akwai manyan masarautu da dauloli kamar Kano, Katsina, Zazzau, Borno da Oyo. Mutanensu suna da nasu tsarin mulki, kasuwanci da cibiyoyin ilimi.

A shekarar 1914, Birtaniya ta haɗa Arewaci da Kudancin Najeriya ƙarƙashin mulki guda.

Daga baya, Najeriya ta samu ’yancin kai a ranar 1 ga Oktoba, 1960.

Wannan shi ne farkon tafiyar mu cikin tarihin Najeriya. 🇳🇬
ku biyo ni rubutu na gaba
✍️Isma'eel Isah Idris

Sifaniya ta doke Argentina 1-0 bayan minti 120, inda Ferran Torres ya zura ƙwallon. Wannan ne karo na biyu da Sifaniya k...
19/07/2026

Sifaniya ta doke Argentina 1-0 bayan minti 120, inda Ferran Torres ya zura ƙwallon.

Wannan ne karo na biyu da Sifaniya ke lashe kofin a tarihinta, bayan lashewa a 2010.

Yaya kuka ga wasan?

🚨 : RAHOTO : Rahotanni daga wasu kafafen yaɗa labarai sun bayyana cewa, bisa ga bayanan wasu jami'an gwamnatin Amurka da...
19/07/2026

🚨 : RAHOTO : Rahotanni daga wasu kafafen yaɗa labarai sun bayyana cewa, bisa ga bayanan wasu jami'an gwamnatin Amurka da ba a bayyana sunayensu ba, an ce dakarun Iran sun kai hare-hare har sau huɗu kan wuraren da sojojin Amurka suke a ƙasar Jordan cikin kwanaki biyar.

Rahoton ya ce harin na baya-bayan nan da aka ruwaito ya faru ne a ranar Juma'a, inda aka ce sojojin Amurka biyu sun mutu, yayin da ake ci gaba da neman wani soja da ya ɓace.

An kuma ce hare-haren sun jikkata sojojin Amurka da dama tare da lalata wasu jiragen sama masu saukar ungulu na Black Hawk da ke ajiye a wasu sansanonin sojin Amurka a Jordan.

Bugu da ƙari, rahoton ya bayyana cewa wani harin makami mai linzami da aka kai a baya kan sansanin Muwaffaq Salti Air Base ya jikkata kimanin sojojin Amurka 20. Daga baya kuma, an ce harin da ya biyo baya ya yi sanadin mutuwar sojoji biyu tare da jikkata wasu huɗu.

A cewar jami'an da aka ambata a rahoton, waɗannan hare-haren na nuni da cewa Iran har yanzu tana da adadi mai yawa na makamai masu linzami. Sun kuma yi ikirarin cewa dakarun Iran suna ƙara samun nasara wajen ketare tsarin kariyar sararin samaniyar Amurka a hare-haren da suke kaiwa.

18/07/2026

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Salisu Bala, Lukman Zakariyya, Sirajo Adamu, Adam Idris

DANGANE DA IRAN.....Rahotanni sun ce hare-haren Amurka kan Iran sun ci gaba da aukuwa ba tare da tsayawa ba fiye da awa ...
16/07/2026

DANGANE DA IRAN.....

Rahotanni sun ce hare-haren Amurka kan Iran sun ci gaba da aukuwa ba tare da tsayawa ba fiye da awa guda, musamman ta wuraren Bandar Abbas, Ahvaz, Tsibirin Qeshm da Bushehr.

An ce hare-haren sun fi mayar da hankali kan muhimman ababen more rayuwa, musamman hanyoyin sadarwa da layukan wutar lantarki, lamarin da ya haddasa katsewar wuta a yankuna da dama tare da kawo cikas ga ayyukan wasu asibitoci.

A cewar rahotannin, mutane bakwai sun jikkata, ciki har da mutum uku daga iyali guda da s**a samu raunuka marasa tsanani, da kuma wasu jami'an tsaro. A Tsibirin Qeshm kaɗai, an ce an ji fashewa takwas, wasu daga cikinsu sun afku a yankunan da fararen hula ke zaune. Har yanzu ba a san ko wane wurare ne aka nufa kai tsaye ba, ko kuma fararen hula ne s**a faɗa cikin harin.

Rahotannin sun nuna cewa Amurka na ƙara faɗaɗa hare-harenta, kuma ana kallon lamarin a matsayin babban sauyi na yaƙin da aka shiga. A gefe guda, an ce jami'an tsaron Iran sun shiga cikin shirin ko-ta-kwana domin tunkarar duk wata barazana.

Ana kuma ganin cewa manufar hare-haren ita ce raunana muhimman ababen more rayuwa kafin duk wani yiwuwar farmakin ƙasa, kamar yadda s**ai a Gaza da Kudancin Lebanon, da taimakon larabawan Dubai, Kuwait, Bahrain, Qatar ake gudanar da waɗannan hare haren.

Baya ga haka, rahotanni sun ce hare-haren sun bazu zuwa wasu yankunan kudancin Iran. An ce jiragen yaƙin Amurka sun kai hari kan Filin Jirgin Sama na Iranshahr, inda mazauna yankin s**a ba da rahoton jin ƙarar fashewa uku masu ƙarfi, tare da bayyana harin a matsayin mai tsanani saboda ƙarar fashe fashe.

Haka kuma, an ce hare-haren saman Amurka sun lalata wata gada da ke Kahourestan a Bandar Abbas. Rahotanni sun kuma ce an sake kai hari a Bampur da Iranshahr, yayin da sansanonin jiragen sama da filayen jiragen sama a sassan Sistan da Baluchestan su ma s**a fuskanci hare-hare.

Kazalika, kafafen yaɗa labaran Iran sun ba da rahoton cewa an samu fashewa 11 a kusa da ƙauyen Mesen da ke Tsibirin Qeshm

Esmail Baghaei, mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, ya ce a wata hira da gidan talabijin na Yemen Al Mas...
16/07/2026

Esmail Baghaei, mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, ya ce a wata hira da gidan talabijin na Yemen Al Masirah cewa:

"Sojojin Iran suna cikin cikakkiyar shiri domin duk wani yanayi da zai iya faruwa, kuma an riga an tabbatar da wannan shirin a aikace.

Iran ba za ta tsaya tana kallon abubuwa suna faruwa ba. Rundunar sojin ƙasa, tsarin diflomasiyyar ƙasar, da al’ummar Iran za su kare tsaron ƙasar da dukkan ƙarfinsu.

Duk wani mataki na kai hari ko zalunci ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran zai fuskanci martani mai ƙarfi, kai tsaye, kuma ba tare da wata shakka ba.

Dangane da yarjejeniyar fahimtar juna (Memorandum of Understanding), matsayin Tehran ya kasance a bayyane tun farko. Har yanzu muna nan a kan ƙa’idar: ‘Alƙawari kan alƙawari’ (wato kowa ya cika nasa alƙawarin kafin a ci gaba)."

Karamar Hukumar Katsina Ta Bude Neman Gurbin Tallafin Karatun Manyan Makarantu na Shekarar 2026Karamar Hukumar Katsina, ...
16/07/2026

Karamar Hukumar Katsina Ta Bude Neman Gurbin Tallafin Karatun Manyan Makarantu na Shekarar 2026

Karamar Hukumar Katsina, karkashin jagorancin Shugabanta, Hon. Isah Miqdad AD Saude , ta bude neman gurbin Tallafin Karatun Manyan Makarantu na Shekarar 2026 domin bai wa matasan yankin damar samun ingantaccen ilimi.

Shirin zai bai wa dalibai 200 cikakken tallafin karatu, inda 100 za su yi karatu a Hassan Usman Katsina Polytechnic (HUK), yayin da sauran 100 za su amfana a Katsina State Institute of Technology and Management (KSITM).

Sharuddan Cancanta

Masu neman tallafin dole ne su:

Kasance 'yan asalin Karamar Hukumar Katsina.

Su ci aƙalla maki 140 a jarabawar UTME ta 2025 ko 2026.

Su kammala makarantar sakandaren gwamnati.

Su kasance tsakanin shekaru 18 zuwa 38.

Su mallaki aƙalla credit biyar (5) ciki har da Turanci da Lissafi a WAEC, NECO ko NABTEB.

Masu neman HND su kasance sun yi shekara guda na aikin IT (Industrial Training) bayan ND.

Ana karɓar buƙatun ne ta hanyar wannan shafi:

https://ggl.link/X7LA2YM

A lura: Za a rufe karɓar aikace-aikace cikin sa'o'i 48 masu zuwa.

Don haka, ana ƙarfafa duk masu cancanta su gaggauta cike da tura buƙatarsu kafin wa'adin ya cika.

Shirin na daga cikin ƙudirin Karamar Hukumar Katsina na bunƙasa ilimi da ƙarfafa matasa domin ci gaban al'umma.

Address

Maglobal Galadima
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ɗanja Times press posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share