Umar Gwaskwaram

  • Home
  • Umar Gwaskwaram

Umar  Gwaskwaram Only God can change the living status of country

26/07/2023

🌹NASIHAR MU TA YAU💐

Manzon Allah (sawa) Yace : "Wani Zamani Zai zo wa Muntane; acikin sa Mutane zasu Zama tamkar Kuraye! Kuma duk Wanda Bai Zama Kura ba! Toh, Kuraye zasu Cinye shi" !!! (Bihar Anwar ,mj 74,s318)

Wannan Hadisi ishara ne na lalacewa da gurbacewan wannan Zamanin! Za'a wayi Gari kowa damuwan sa da hankoran Sa itace duniya! A Wannan Zamanin Mutane za su Rika Musabakan Neman duniya ta hanyar fasadi da Zalinci da Kuma zubar da jinai ne ba tare da hakki ba !! K**ar yadda Kura takeyi !

Idan ka duba Kura acikin Garken dabbobi, barna takeyi, Wato ba shuwagabanni ba ba kuma talaka wa ba duk za'a zama tamkar kura a cikin garken awakai! Sai barna da shekar da jinanai!! Haka Mutane zasu kasance Marasa Gaskiya da Amana Babu tausayi ko jinkai a tsakanin su! A Wannan Zamanin Kowa Yana Neman yadda Zai Yi ya Samu duniya ta ko Yaya! Ta yin Karya ko cin Amana ko Kuma yayi Zalinci da danniya! Ko ta hanyar kisa!! A Wannan Zamanin Idan Kai baka Zama K**ar su ba, toh zasu yake ka ta kowani hanya Koda ya K**a suyi kisan Kai ne! Idan mutum ya Zama mabarnaci a rayuwar sa toh, ya Zama Kura kenan!

Amma Shi Mumini Wanda yayi Riko da Addini tare da Jajircewa Zai Zama tamkar yayi Riko ne da garwashin wuta! Don Haka Tsayuwa da Riko da Addini a irin Wannan Zamanin Sai Muminai, Mukh'lisai, Jajirtattu, Wanda S**a saki duniya S**a sayi Lahira...

Muna rokon Allah da Yayi Mana muwafaka da zamowa cikin bayin Sa Muminai Kuma Mukhlisai a Rayuwar mu tare da Jajircewa a tafarkin Sa.




26/07/2023

Humanity

12/07/2023

ANNABI MUHAMMAD(SAW) BAI TABA WANKE KAFARSA A AL-WALA BA, SHAFA YAKE YI; KAMAR YANDA AYAR QUR'ANI DA INGANTATTUN HADISAI S**A TABBATAR:

Duk wani hadisi da yaci karo da ayar Qur'ani to ba fadar Annabi(saw) ba ne, don ba zai yiwu Allah da Annabi(saw) su samu sabani ba. Sam ba zai yiwu a samu karo tsakanin maganar Allah da ta Annabi Muhammad(saw).

Qur'ani ya tabbatar mana da cewa; Allah ya umarcemu da mu shafi kafar mu a Al-wala.

Allah(t) yana cewa;

ﻳَﺎ ﺃَﻳُّﻬَﺎ ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﺁﻣَﻨُﻮﺍ ﺇِﺫَﺍ ﻗُﻤْﺘُﻢْ ﺇِﻟَﻰ ﺍﻟﺼَّﻠَﺎﺓِ ﻓَﺎﻏْﺴِﻠُﻮﺍ ﻭُﺟُﻮﻫَﻜُﻢْ ﻭَﺃَﻳْﺪِﻳَﻜُﻢْ ﺇِﻟَﻰ ﺍﻟْﻤَﺮَﺍﻓِﻖِ ﻭَﺍﻣْﺴَﺤُﻮﺍ ﺑِﺮُﺀُﻭﺳِﻜُﻢْ ﻭَﺃَﺭْﺟُﻠَﻜُﻢْ ﺇِﻟَﻰﺍﻟْﻜَﻌْﺒَﻴْﻦِ ...

"Ya ku mutane! Idan kun tashi zuwa sallah, to ku wanke fuskarku da hannayenku zuwa murafikai; sannan ku shafi kanku da kafafunku zuwa ka'abai (saman kafa)".

(Qur'an : 5 : 6).

Doriya akan zahirin wannan ayar da ya tabbatar da shafar kafa a Al-wala shine daidai; akwai wasu hadisai ingantattu da malaman Ahlus-Sunnah s**a nakalto; masu goyon bayan shafar kafa amadadin wankewa.

Babban malamin Ahlus-Sunnah; Ibn Abi Shaiba ya rawaito cewa; khalifa Usman Bin Affan ya ce; Annabi Muhammad(saw) shafar kafa ya keyi ba wankewa ba:

55 - ﺣﺪﺛﻨﺎ: ﻣﺤﻤﺪ ﺑﻦ ﺑﺸﺮ، ﻗﺎﻝ: ﺣﺪﺛﻨﺎ : ﺳﻌﻴﺪ ﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﺮﻭﺑﺔ، ﻋﻦ ﻗﺘﺎﺩﺓ، ﻋﻦ ﻣﺴﻠﻢ ﺑﻦ ﻳﺴﺎﺭ، ﻋﻦ ﺣﻤﺮﺍﻥ، ﻗﺎﻝ: ﺩﻋﺎ ﻋﺜﻤﺎﻥ ﺑﻤﺎﺀ ﻓﺘﻮﺿﺄ ، ﺛﻢ ﺿﺤﻚ ، ﻓﻘﺎﻝ: ﺃﻻ ﺗﺴﺄﻟﻮﻧﻲ ﻣﻤﺎ ﺃﺿﺤﻚ، ﻗﺎﻟﻮﺍ: ﻳﺎ ﺃﻣﻴﺮ ﺍﻟﻤﺆﻣﻨﻴﻦ، ﻣﺎ ﺃﺿﺤﻜﻚ؟ ﻗﺎﻝ: ﺭﺃﻳﺖ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ‏(ﺹ‏) ﺗﻮﺿﺄ ﻛﻤﺎ ﺗﻮﺿﺄﺕ، ﻓﻤﻀﻤﺾ ﻭﺇﺳﺘﻨﺸﻖ، ﻭﻏﺴﻞ ﻭﺟﻬﻪ ﺛﻼﺛﺎً ﻭﻳﺪﻳﻪ، ﻭﻣﺴﺢ ﺑﺮﺃﺳﻪ ﻭﻇﻬﺮ ﻗﺪﻣﻴﻪ.

- ﺇﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﺷﻴﺒﺔ - ﺍﻟﻤﺼﻨﻒ - ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﻄﻬﺎﺭﺍﺕ.

Shima Khalifa Usman Bin Affan shafar kafarsa yake yi a Al-wala ba wankewa:

ﺣﺪﺛﻨﺎ : ﻣﺤﻤﺪ ﺑﻦ ﺟﻌﻔﺮ، ﺣﺪﺛﻨﺎ: ﺳﻌﻴﺪ، ﻋﻦ ﻗﺘﺎﺩﺓ، ﻋﻦ ﻣﺴﻠﻢ ﺑﻦ ﻳﺴﺎﺭ، ﻋﻦ ﺣﻤﺮﺍﻥ ﺑﻦ ﺃﺑﺎﻥ، ﻋﻦ ﻋﺜﻤﺎﻥ ﺑﻦ ﻋﻔﺎﻥ: ﺃﻧﻪ ﺩﻋﺎ ﺑﻤﺎﺀ ﻓﺘﻮﺿﺄ ﻭﻣﻀﻤﺾ ﻭﺇﺳﺘﻨﺸﻖ ﺛﻢ ﻏﺴﻞ ﻭﺟﻬﻪ ﺛﻼﺛﺎً ﻭﺫﺭﺍﻋﻴﻪ ﺛﻼﺛﺎً ﺛﻼﺛﺎً ﻭﻣﺴﺢ ﺑﺮﺃﺳﻪ ﻭﻇﻬﺮ ﻗﺪﻣﻴﻪ...

- ﻣﺴﻨﺪ ﺃﺣﻤﺪ - ﻣﺴﻨﺪ ﺍﻟﻌﺸﺮﺓ ﺍﻟﻤﺒﺸﺮﻳﻦ ﺑﺎﻟﺠﻨﺔ - ﻣﺴﻨﺪ ﻋﺜﻤﺎﻥ ﺑﻦ ﻋﻔﺎﻥ‏(ﺭ‏) - ﺭﻗﻢ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ : (319‏).

Ibn Hajar Al-askalani ya rawaito a Al-isaba, a tarjamar Tamim Bin Zaid, cewa Annabi(saw) shafar kafarsa yake a Al-wala:

ﻭﺃﺧﺮﺝ ﺍﻟﺤﺎﻓﻆ ﺍﺑﻦ ﺣﺠﺮ ﻓﻲ ﺗﺮﺟﻤﺔ ﺗﻤﻴﻢ ﺑﻦ ﺯﻳﺪ ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺴﻢ ﺍﻷﻭﻝ ﻣﻦ ‏(ﺍﻹﺻﺎﺑﺔ): "ﻗﺎﻝ ﺍﺑﻦ ﺣﺒﺎﻥ: ﺗﻤﻴﻢ ﺑﻦ ﺯﻳﺪ ﺍﻟﻤﺎﺯﻧﻲ ﻟﻪ ﺻﺤﺒﺔ ﻭﺣﺪﻳﺜﻪ ﻋﻨﺪ ﻭﻟﺪﻩ ﻭﺭﻭﻯ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ﻓﻲ (ﺗﺎﺭﻳﺨﻪ‏) ﻭﺃﺣﻤﺪ ﻭﺍﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﺷﻴﺒﺔ ﻭﺍﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﻤﺮ ﻭﺍﻟﺒﻐﻮﻱ ﻭﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻭﺍﻟﺒﺎﺭﻭﺩﻱ ﻭﻏﻴﺮﻫﻢ ﻛﻠﻬﻢ ﻣﻦ ﻃﺮﻳﻖ ﺃﺑﻲ ﺍﻷﺳﻮﺩ ﻋﻦ ﻋﺒﺎﺩ ﺑﻦ ﺗﻤﻴﻢ ﺍﻟﻤﺎﺯﻧﻲ ﻋﻦ ﺃﺑﻴﻪ ﻗﺎﻝ: ﺭﺃﻳﺖ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻳﺘﻮﺿﺄ ﻭﻳﻤﺴﺢ ﻋﻠﻰ ﺭﺟﻠﻴﻪ. ﺭﺟﺎﻟﺔ ﺛﻘﺎﺕ"

Ibn Hajar ya ce duk marawaitan masu gaskiya ne.

Imam Ali(as) shima ya tabbatar cewa Annabi(saw) shafar kafa ya keyi:

181 - ﺣﺪﺛﻨﺎ: ﻭﻛﻴﻊ، ﻋﻦ ﺍﻷﻋﻤﺶ، ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﺇﺳﺤﺎﻕ، ﻋﻦ ﻋﺒﺪ ﺧﻴﺮ، ﻋﻦ ﻋﻠﻲ ﻗﺎﻝ: ﻟﻮ ﻛﺎﻥ ﺍﻟﺪﻳﻦ ﺑﺮﺃﻱ ﻛﺎﻥ ﺑﺎﻃﻦ ﺍﻟﻘﺪﻣﻴﻦ ﺃﺣﻖ ﺑﺎﻟﻤﺴﺢ ﻣﻦ ﻇﺎﻫﺮﻫﻤﺎ ﻭﻟﻜﻦ ﺭﺃﻳﺖ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ(ﺹ‏) ﻣﺴﺢ ﻇﺎﻫﺮﻫﻤﺎ.

- ﺇﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﺷﻴﺒﺔ - ﺍﻟﻤﺼﻨﻒ - ﺍﻟﺠﺰﺀ : ‏(1) - ﺭﻗﻢ ﺍﻟﺼﻔﺤﺔ: ‏(30‏).

Imam Ali yana cewa;

"Da ace musulunci ra'ayi ne to karkashin kafa ya kamata a Shafa ba kan kafa ba, amma naga Manzan Allah(saw) yana shafar kafarsa".

Ibn Abass ya ce; wajibi a Al-wala shine; wankewa 2 (wanke fuska da hannuwa) da shafa 2 (shafar kai da kafa), (kamar dai yanda zahirin ayar Al-wala ya zo dashi):

10432 - ﺣﺪﺛﻨﺎ: ﺃﺑﻮ ﻛﺮﻳﺐ، ﻗﺎﻝ: ﺣﺪﺛﻨﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﺑﻦ ﻗﻴﺲ ﺍﻟﺨﺮﺍﺳﺎﻧﻲ، ﻋﻦ ﺇﺑﻦ ﺟﺮﻳﺞ، ﻋﻦ ﻋﻤﺮﻭ ﺑﻦ ﺩﻳﻨﺎﺭ، ﻋﻦ ﻋﻜﺮﻣﺔ، ﻋﻦ ﺇﺑﻦ ﻋﺒﺎﺱ، ﻗﺎﻝ: ﺍﻟﻮﺿﻮﺀ ﻏﺴﻠﺘﺎﻥ ﻭﻣﺴﺤﺘﺎﻥ.

- ﺍﻟﻄﺒﺮﻱ - ﺟﺎﻣﻊ ﺍﻟﺒﻴﺎﻥ - ﺍﻟﺠﺰﺀ : ‏( 6 ‏) - ﺭﻗﻢ ﺍﻟﺼﻔﺤﺔ : ‏( 175 ‏)

Anas bin Malik ya kalubalaci Hajjaj bin Yusuf As-Sakafi akan cewa a wanke kafa a Al-wala amadadin shafa. Hakan ya tabbatar da Anas bin Malik shima shafar kafarsa ya ke a al-wala.

10433 - ﺣﺪﺛﻨﺎ : ﺣﻤﻴﺪ ﺑﻦ ﻣﺴﻌﺪﺓ ، ﻗﺎﻝ : ﺛﻨﺎ ﺑﺸﺮ ﺑﻦ ﺍﻟﻤﻔﻀﻞ ، ﻋﻦ ﺣﻤﻴﺪ ﺡ ، ﻭﺣﺪﺛﻨﺎ ﻳﻌﻘﻮﺏ ﺑﻦ ﺇﺑﺮﺍﻫﻴﻢ ، ﻗﺎﻝ : ﺛﻨﺎ ﺇﺑﻦ ﻋﻠﻴﺔ ، ﻗﺎﻝ : ﺛﻨﺎ ﺣﻤﻴﺪ ، ﻗﺎﻝ : ﻗﺎﻝ ﻣﻮﺳﻰ ﺑﻦ ﺃﻧﺲ ﻷﻧﺲ ﻭﻧﺤﻦ ﻋﻨﺪﻩ : ﻳﺎ ﺃﺑﺎ ﺣﻤﺰﺓ ﺇﻥ ﺍﻟﺤﺠﺎﺝ ﺧﻄﺒﻨﺎ ﺑﺎﻷﻫﻮﺍﺯ ﻭﻧﺤﻦ ﻣﻌﻪ ، ﻓﺬﻛﺮ ﺍﻟﻄﻬﻮﺭ ، ﻓﻘﺎﻝ : ﺇﻏﺴﻠﻮﺍ ﻭﺟﻮﻫﻜﻢ ﻭﺃﻳﺪﻳﻜﻢ ﻭﺇﻣﺴﺤﻮﺍ ﺑﺮﺀﻭﺳﻜﻢ ﻭﺃﺭﺟﻠﻜﻢ ، ﻭﺇﻧﻪ ﻟﻴﺲ ﺷﺊ ﻣﻦ ﺇﺑﻦ ﺁﺩﻡ ﺃﻗﺮﺏ ﺇﻟﻰ ﺧﺒﺜﻪ ﻣﻦ ﻗﺪﻣﻴﻪ ، ﻓﺈﻏﺴﻠﻮﺍ ﺑﻄﻮﻧﻬﻤﺎ ﻭﻇﻬﻮﺭﻫﻤﺎ ﻭﻋﺮﺍﻗﻴﺒﻬﻤﺎ . ﻓﻘﺎﻝ ﺃﻧﺲ : ﺻﺪﻕ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﻛﺬﺏ ﺍﻟﺤﺠﺎﺝ ، ﻗﺎﻝ ﺍﻟﻠﻪ : ﻭﺇﻣﺴﺤﻮﺍ ﺑﺮﺀﻭﺳﻜﻢ ﻭﺃﺭﺟﻠﻜﻢ ﻗﺎﻝ : ﻭﻛﺎﻥ ﺃﻧﺲ ﺇﺫﺍ ﻣﺴﺢ ﻗﺪﻣﻴﻪ ﺑﻠﻬﻤﺎ.

- ﺍﻟﻄﺒﺮﻱ - ﺟﺎﻣﻊ ﺍﻟﺒﻴﺎﻥ - ﺍﻟﺠﺰﺀ : ‏( 6 ‏) - ﺭﻗﻢ ﺍﻟﺼﻔﺤﺔ : ‏( 175 ‏).

Ibn Maja ya tabbatar da cewa Ibn Abbas ya karyata duk wani hadisi da ya ce Annabi(saw) ya wanke kafarsa yake a Al-wala, sannan ya tabbatar da cewa; Annabi(saw) shafar kafarsa yake, kuma da haka Allah ya aiko mala'ika Jibril(as) da ayar Al-wala; ko da wasu mutane sun fandare:

- ﺣﺪﺛﻨﺎ : ﺃﺑﻮ ﺑﻜﺮ ﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﺷﻴﺒﺔ ، ﺣﺪﺛﻨﺎ : ﺇﺑﻦ ﻋﻠﻴﺔ ، ﻋﻦ ﺭﻭﺡ ﺑﻦ ﺍﻟﻘﺎﺳﻢ ، ﻋﻦ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﻦ ﻣﺤﻤﺪ ﺑﻦ ﻋﻘﻴﻞ ، ﻋﻦ ﺍﻟﺮﺑﻴﻊ ﻗﺎﻟﺖ : ﺃﺗﺎﻧﻲ ﺇﺑﻦ ﻋﺒﺎﺱ ﻓﺴﺄﻟﻨﻲ ، ﻋﻦ ﻫﺬﺍ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺗﻌﻨﻲ ﺣﺪﻳﺜﻬﺎ ﺍﻟﺬﻱ ﺫﻛﺮﺕ ﺃﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ‏( ﺹ ‏) ﺗﻮﺿﺄ ﻭﻏﺴﻞ ﺭﺟﻠﻴﻪ ﻓﻘﺎﻝ ﺇﺑﻦ ﻋﺒﺎﺱ : ﺇﻥ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺃﺑﻮﺍ ﺇﻻ ﺍﻟﻐﺴﻞ ﻭﻻ ﺃﺟﺪ ﻓﻲ ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﻠﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻤﺴﺢ.

- ﺳﻨﻦ ﺇﺑﻦ ﻣﺎﺟﻪ - ﺍﻟﻄﻬﺎﺭﺓ ﻭﺳﻨﻨﻬﺎ - ﻣﺎ ﺟﺎﺀ ﻓﻲ ﻏﺴﻞ ﺍﻟﻘﺪﻣﻴﻦ - ﺭﻗﻢ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ : ‏(451).

Umar bin Khattab ma ya yarda Annabi(saw) shafar kafarsa ya ke a Al-wala:

ﺃﺧﺮﺝ ﺍﺑﻦ ﺷﺎﻫﻴﻦ ﻓﻲ ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﻨﺎﺳﺦ ﻭﺍﻟﻤﻨﺴﻮﺥ ﻋﻨﻪ ﺣﺪﻳﺜﺎ ﻓﻲ ﺍﻟﻤﺴﺢ، ﻭﻻﺣﻆ ﻋﻤﺪﺓ ﺍﻟﻘﺎﺭﻱ ﻓﻲ ﺷﺮﺡ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ 2 / 240.

Imam Fakhrud-din Razi a Tafsirul-Kabir ya ya kawo cikakken bayani akan cewa shafar kafa shine wajibi a Al-wala ba wankewa ba.

(Tafsirul-Kabir na Fakhrud-din Razi, karkashin tafsirin ayar Al-wala).

Ibn Taimiyyah ya tabbatar da cewa shafar kafa shine wajibi, ba wankewa ba; idan an karanta ﺃﺭﺟﻠﻜﻢ da wasalin jarra (wasali kasa):

قال ابن تيمية:
..ﻭﻫﺬﻩ ﺍﻵﻳﺔ (ﺍﻵﻳﺔ ﺍﻟﻮﺿﻮﺀ) ﻓﻴﻬﺎ ﻗﺮﺍﺀﺗﺎﻥ ﻣﺸﻬﻮﺭﺗﺎﻥ: ﺍﻟﺨﻔﺾ ﻭﺍﻟﻨﺼﺐ، ﻓﺎﻟﺬﻳﻦ ﻗﺮﺀﻭﺍ ﺑﺎﻟﻨﺼﺐ، ﻗﺎﻝ ﻏﻴﺮ ﻭﺍﺣﺪ ﻣﻨﻬﻢ: ﺃﻋﺎﺩ ﺍﻷﻣﺮ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﻐﺴﻞ، ﺃﻱ: ﻭﺍﻣﺴﺤﻮﺍ ﺑﺮﺀﻭﺳﻜﻢ، ﻭﺍﻏﺴﻠﻮﺍ ﺃﺭﺟﻠﻜﻢ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﻜﻌﺒﻴﻦ، ﻭﺍﻟﻘﺮﺍﺀﺗﺎﻥ ﻛﺎﻵﻳﺘﻴﻦ. ﻭﻣﻦ ﻗﺎﻝ: ﺇﻧﻪ ﻋﻄﻒ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻞ ﺍﻟﺠﺎﺭ ﻭﺍﻟﻤﺠﺮﻭﺭ ، ﻳﻜﻮﻥ ﺍﻟﻤﻌﻨﻰ: ﻭﺍﻣﺴﺤﻮﺍ ﺑﺮﺀﻭﺳﻜﻢ، ﻭﺍﻣﺴﺤﻮﺍ ﺃﺭﺟﻠﻜﻢ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﻜﻌﺒﻴﻦ...

- ﻣﻨﻬﺎﺝ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺍﻟﻨﺒﻮﻳﺔ‏: ﺍﻟﻔﺼﻞ ﺍﻟﺜﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺃﻥ ﻣﺬﻫﺐ ﺍﻹﻣﺎﻣﻴﺔ ﻭﺍﺟﺐ ﺍﻻﺗﺒﺎﻉ: ﻛﻼﻡ ﺍﻟﺮﺍﻓﻀﻲ ﻋﻠﻰ ﻣﺴﺢ ﺍﻟﺮﺟﻠﻴﻦ ﻓﻲ ﺍﻟﻮﺿﻮﺀ ﺑﺪﻻ ﻣﻦ ﻏﺴﻠﻬﻤﺎ... - ﻣﻜﺘﺒﺔ ﺍﺑﻦ ﺗﻴﻤﻴﺔ. ﺳﻨﺔ ﺍﻟﻨﺸﺮ: 1406 ﻫـ / 1986 ﻡ. ﻋﺪﺩ ﺍﻷﺟﺰﺍﺀ: ﺗﺴﻌﺔ ﺃﺟﺰﺍﺀ.

Kuma karantawa da wasali kasan, shine daidai, soboda ba Hikima, Balagah da tambatar ka'idojin Nahwu a karantawa da wasalin nasaba (wasali sama).

Ballema, Babban malamin Ahlus-Sunnah; Ibn Hazam Al-Andalusi yana cewa:

ﻭﺃﻣﺎ ﻗﻮﻟﻨﺎ ﻓﻲ ﺍﻟﺮﺟﻠﻴﻦ ﻓﺈﻥ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻧﺰﻝ ﺑﺎﻟﻤﺴﺢ ‏(ﻭﺍﻣﺴﺤﻮﺍ ﺑﺮﻭﺀﺳﻜﻢ ﻭﺍﺭﺟﻠﻜﻢ) ﻭﺳﻮﺍﺀ ﻗﺮﺉ ﺑﺨﻔﺾ ﺍﻟﻼﻡ ﺃﻭ ﺑﻔﺘﺤﻬﺎ ﻫﻲ ﻋﻠﻰ ﻛﺎﻝ ﺣﺎﻝ ﻋﻄﻒ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺮﺅﻭﺱ

"Abinda zamu iya cewa akan shafar kafa shine; kamar yadda Qur'ani yazo dashi, koda an karanta ayar akan; Arjilakum Ko arjulakum (fataha ko jarra) duk ma'anar daya ce, tunda shafar kafa; adafi ce akan shafar kai".

(Muhalla Ibn Hazam, sifilina 3 shafi Na 44).

Kenan Idan muka duba ayar da aka saukar akan Al-wala duk yadda ka karanta to ma'anar daya ce. Ko kace ﺃﺭﺟﻠـِـﻜﻢ Ko kace ﺃﺭﺟﻠَـﻜﻢ Wannan bai sa wanke kafa ya zama wajibi ba; a al-wala ba (banbancin kisra ko rufua). Shafar kafa itace wajibi a al-wala.

Don haka duk wani hadisi da ya sabawa ayar Qur'ani; to 'magana jari' tafi shi kima. Ballema bincike da ilimin Masdalahul-hadis ya tabbatar da cewa; bawa wani ingantaccen hadisi da yace a wanke kafa a Al-wala amadadin shafa.

12/07/2023

BA DUKKAN SAHABBAI NE ALLAH YAYIWA ALKAWALIN SHIGA AL-JANNAH BA; AKWAI SAHABBAI DA YAWA DA ZASU SHIGA WUTAR JAHANNAMA

IDAN DUK SAHABBAI ‘YAN AL-JANNAH NE; ME YA SA ALLAH ZAI SAUKAR DA SURAR MUNAFUKAI A QUR’ANI?

IDAN MUNAFIKI BAYA ZAMA SAHABI SAI DAI YANA IYA ZAMA TARE DA SAHABBAI, TO MUNAFUNCI A FILI YA KE KO A ZUCIYA? TAYA ZAMU IYA TABBATAR CIKIN SAHABBAI BA MUNAFUKAI?

IDAN SAHABI SHINE WANDA YA HAFB_IMG_1515147094543DU DA ANNABI MUHAMMAD(SAW); YANA MAI IMANI DA SHI, KUMA YA MUTU A KAN MUSULUNCI:

KENAN BA DUK WANDA YA MUSULUNTA A LOKACIN ANNABI(SAW) NE SAHABI BA?

TAYA ZAMU GANE SAHABI; TUNDA LALLE NE YA KASANCE MAI IMANI, ALHALI IMANI A ZUCIYA YAKE?

KENAN MUNA BUKATAR SANIN GAIBI KO WANI WANDA YA SAN GAIBI; KAFIN MU TABBATAR DA SAHABBANCIN KO WANE SAHABI?

YA ZAMU YI DA AYOYIN DA KE TABBATAR DA AKWAI MUNAFUKAI CIKIN SAHABBAI?

KO MASU AKIDAR DUK SAHABBAI ‘YAN AL-JANNAH SUN YARDA DA AKIDAR TAHRIFI (JIRKITA QUR’ANI TAHANYAR RAGI KO KARI)?

KENAN DUK WANDA YACE; DUKKAN SAHABBAI YARDADDU NE KUMA ‘YAN AL-JANNAH NE; TO YA KARYATA AYOYI DA YAWA A QUR’ANI DA INGANTATTUN HADISAI MASU YAWAN GASKE?

KENAN AYOYIN QUR’ANI DA INGANTATTUN HADISAI SUN TABBATAR MANA DA CEWA; BA DUKKAN SAHABBAI NE ALLAH YAYIWA ALKAWALIN SHIGA AL-JANNAH BA; AKWAI SAHABBAI DA YAWA DA ZASU SHIGA WUTAR JAHANNAMA?

Wasu su kan kafa hujja da wasu ayoyin Qur’ani akan cewa Allah yayi al-kawalin Al-Jannah ga dukkan Sahabbai, misali:

Fadin Allah(saw);

ﻟَﺎ ﻳَﺴْﺘَﻮِﻱ ﻣِﻨْﻜُﻢْ ﻣَﻦْ ﺃَﻧْﻔَﻖَ ﻣِﻦْ ﻗَﺒْﻞِ ﺍﻟْﻔَﺘْﺢِ ﻭَﻗَﺎﺗَﻞَ ﺃُﻭﻟَﺌِﻚَﺃَﻋْﻈَﻢُ ﺩَﺭَﺟَﺔً ﻣِﻦَ ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﺃَﻧْﻔَﻘُﻮﺍ ﻣِﻦْ ﺑَﻌْﺪُ ﻭَﻗَﺎﺗَﻠُﻮﺍ ﻭَﻛُﻠًّﺎ ﻭَﻋَﺪَﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟْﺤُﺴْﻨَﻰ ﻭَﺍﻟﻠَّﻪُ ﺑِﻤَﺎ ﺗَﻌْﻤَﻠُﻮﻥَ ﺧَﺒِﻴﺮٌ.

“Wanda ya ciyar a gabanin cin nasara, kuma ya yi yaki daga cikinku, baya zama daidai (da wanda bai yi hakan ba). Wadancan sune mafifitan girman daraja, bisa ga wadanda s**a ciyar daga baya kuma su ka yi yaki. Kuma dukansu Allah Ya yi mu su alkawli da (sakamako) mai kyau, kuma Allah Masani ne ga abin da ku ke aikatawa”.

(ﺍﻟﺤﺪﻳﺪ : 10).

Shin wannan ayar ta nuna Sahabban da s**a yi jihad da infaki kafin fatuhu Makka ma’asumai ne? Idan ba ma’asumai ba ne; to wanda yayi wani aiki irin na ‘yan wuta daga baya (kamar kisan kai; irin yanda Fi’atul-bagiya s**a yi) to shi ma ba shida wani laifi; tunda an yi masa alkawalin Al-jannah?

Me ya sa wadanda ke kafa hujja da wannan ayar ba su kawo farkon ayar? Saboda farkon ayar yana nuna yanda wasu Sahabbai s**a ki tallafawa Musulunci da dukiyoyinsu? kamar yanda Allah ya ke cewa:

وَمَا لَكُمْ أَلَّا تُنفِقُوا فِي سَبِيلِ اللَّهِ وَلِلَّهِ مِيرَاثُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ لَا يَسْتَوِي مِنكُم مَّنْ أَنفَقَ مِن قَبْلِ الْفَتْحِ وَقَاتَلَ ۚ أُولَٰئِكَ أَعْظَمُ دَرَجَةً مِّنَ الَّذِينَ أَنفَقُوا مِن بَعْدُ وَقَاتَلُوا ۚ وَكُلًّا وَعَدَ اللَّهُ الْحُسْنَىٰ ۚ وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ خَبِيرٌ

“Me ya sa baku ciyar da dukiyarku wajen dauka kalmar Allah? Allah ne majibincin Sammai da kassai….”

Kenan akwai wasu Sahabbai masu yiwa Allah rowa da kin ciyar da dukiyar su wajen daukaka addinin Musulunci?

Shin ba ku kula da Fadin Allah cewa; ﻣِﻨْﻜُﻢ (daga cikinku) ba; a ayar? Kenan ya nuna ba dukkan Sahabban da s**a musulunta kafin Fatahu Makka; ayar take magana akan su ba? wadansu ne daga ciki? Idan dukkan Sahabban da s**a muasulunta kafin Fatahu Makka ayar take magana; to me ya sa aka kawo ‘Tab’idiyya’?

Idan har dukkan Sahabban da s**a musulunta kafin Fatahu Makka sun yi infaki da jihadi me ya sa Allah zai ce;

ﻫَﺎ ﺃَﻧْﺘُﻢْﻫَﺆُﻟَﺎﺀِ ﺗُﺪْﻋَﻮْﻥَ ﻟِﺘُﻨْﻔِﻘُﻮﺍ ﻓِﻲ ﺳَﺒِﻴﻞِ ﺍﻟﻠَّﻪِﻓَﻤِﻨْﻜُﻢْ ﻣَﻦْ ﻳَﺒْﺨَﻞُ ﻭَﻣَﻦْ ﻳَﺒْﺨَﻞْ ﻓَﺈِﻧَّﻤَﺎ ﻳَﺒْﺨَﻞُ ﻋَﻦْ ﻧَﻔْﺴِﻪِ ﻭَﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟْﻐَﻨِﻲُّ ﻭَﺃَﻧْﺘُﻢُ ﺍﻟْﻔُﻘَﺮَﺍﺀ.

“Ga kunan (ku Sahabbai), kune ake kiranku ku yi infaki amma wasunku suna rowa…”.

(Suratu Muhammad(saw); ayata 38).

Idan har wannan ayar tana nuna duk Sahabin da yayi jihadi da infaki kafin fatahu Makka dan Al-Jannah ne; me ya sa Allah zai ce;

ﻭَﺇِﻥْ ﺗَﺘَﻮَﻟَّﻮْﺍ ﻳَﺴْﺘَﺒْﺪِﻝْ ﻗَﻮْﻣًﺎ ﻏَﻴْﺮَﻛُﻢْ ﺛُﻢَّ ﻟَﺎﻳَﻜُﻮﻧُﻮﺍ ﺃَﻣْﺜَﺎﻟَﻜُﻢ.

“Idan (ku Sahabbai) kun juya baya (kun canza ayuka masu kyau da munana) (Allah) zai canza wasu mutane da ban; ba irinku ba, kuma ba zasu zama tamkar ku ba”.

(Suratu Muhammad(saw); ayata 38).

Kenan wannan ayar tana nuna ko da sahabi yayi jihadi da infaki; idan har ya canza daga baya; to Allah zai canza masa sakamako?

Cewa ayar tana nuna Abubakar, Umar, Usman… ‘yan Al-Jannah ne; Saboda sun yi infaki (ciyarwa) kafin bude Makka. Ba wata ruyawa da ta inganta da ta nuna Abubakar, Umar, Usman… Sun yi infaki kafin Fatahu Makka.

Ayar tana nuna cewa lalle wanda aka yiwa al-kawalin husna (Al-Jannah) a ayar sun yi jihadi, kuma sun kashe kafirai a jihadi. Kenan ayar ba akan su Abubakar, Umar, Usman… take magana ba, saboda ba wata ruyawa da inganta da ta nuna Abubakar, Umar ko Usman sun taba kashe wani kafuri a fagen daga, ba ruwaya ingantatta da ta nuna sun taba yin mubaraza, gwarzantaka ko jarunta a fagen yaki. Hasalima ruwayoyi ingantattu da littattafan Ahlus-Sunnah; sun nakalto yanda s**a ari takalmin kare a filin yakin Uhud, Khaibar, Hunai…

Shin ko ba ku san cewa ranar yakin Uhud; Abubakar, Umar, Usman… Sun gudu daga faken yaki?

Ko ba ku karanta hadisur-Raya (Hadisin bada tuta ga Imam Ali a Yakin khaibar) ba? Me ya sa aka tura Abubakar da Umar s**a gudo?

Me ya sa a yakin Ahzab Abubakar, Umar, Usman.. basu tari sadaukin kafirai Amr bin Abduwud ba? Me ya sa Imam Ali(as) ne kadai ya nuna jarubta a ranar?

Me ya sa a yakin Hunain Abubakar, Umar, Usman… S**a ranta a na kare?

Imam Malik a Muwatta, ya tabbatar mana da cewa, Annabi(saw) ya ki yiwa Abubakar bushara da Al-Jannah, saboda ya san zai canza bayan wafatinsa(saw). Ga matanin ruwayar:

ﻭَﺣَﺪَّﺛَﻨِﻲ ﻋَﻦْ ﻣَﺎﻟِﻚٍ، ﻋَﻦْ ﺃَﺑِﻲ ﺍﻟﻨَّﻀْﺮِ، ﻣَﻮْﻟَﻰ ﻋُﻤَﺮَ ﺑْﻦِ ﻋُﺒَﻴْﺪِ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺃَﻧَّﻪُ ﺑَﻠَﻐَﻪُ ﺃَﻥَّ ﺭَﺳُﻮﻝَ ﺍﻟﻠَّﻪِ(ص) ﻗَﺎﻝَ ﻟِﺸُﻬَﺪَﺍﺀِ ﺃُﺣُﺪٍ “ﻫَﺆُﻻَﺀِ ﺃَﺷْﻬَﺪُ ﻋَﻠَﻴْﻬِﻢْ”. ﻓَﻘَﺎﻝَ ﺃَﺑُﻮ ﺑَﻜْﺮٍ ﺍﻟﺼِّﺪِّﻳﻖُ ﺃَﻟَﺴْﻨَﺎ ﻳَﺎ ﺭَﺳُﻮﻝَ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺑِﺈِﺧْﻮَﺍﻧِﻬِﻢْ ﺃَﺳْﻠَﻤْﻨَﺎ ﻛَﻤَﺎ ﺃَﺳْﻠَﻤُﻮﺍ ﻭَﺟَﺎﻫَﺪْﻧَﺎ ﻛَﻤَﺎ ﺟَﺎﻫَﺪُﻭﺍ . ﻓَﻘَﺎﻝَ ﺭَﺳُﻮﻝُ ﺍﻟﻠَّﻪِ(ص) “ﺑَﻠَﻰ ﻭَﻟَﻜِﻦْ ﻻَ ﺃَﺩْﺭِﻱ ﻣَﺎ ﺗُﺤْﺪِﺛُﻮﻥَ ﺑَﻌْﺪِﻱ” . ﻓَﺒَﻜَﻰ ﺃَﺑُﻮ ﺑَﻜْﺮٍ ﺛُﻢَّ ﺑَﻜَﻰ ﺛُﻢَّ ﻗَﺎﻝَ ﺃَﺋِﻨَّﺎ ﻟَﻜَﺎﺋِﻨُﻮﻥَ ﺑَﻌْﺪَﻙَ”.

(Muwatta Malik, Littafin Jihadi: 21, Hadisi na 993).

Idan ayar ta nuna an yiwa Abubakar… al-kawalin Al-Jannah, me ya sa Annabi(saw) bai yimasa busharar ba? Me ya sa Annabi(saw) zai ce; “Ban san abinda zaku aikata bayana ba”? Kenan hakan yana nuna Annabi(saw) ya san zasu aikata wani abu a bayansa? Ko kun fi Annabi(saw) sanin Qur’ani?

Idan har ayar tana nuna an yiwa Umar alkawalin Al-Jannah; ME YA SA UMAR YA GAGARA SAMUN NUTSUWA; YAYI TA BIN HUZAIFA AKAN YA GAYAMASA YANA CIKIN MUNAFUKAI KO BAYA CIKI?

Me Ya sa Umar Ya Takura A Gayamasa Yana Cikin Munafukai Ko Baya Ciki?

Shin Bai Yarda Da Alkawalin Al-jannar bane?

ME YA SA UMAR DAN KHADDAB BAI JE JANA’IZAR ABOKINSA; ABUBAKAR BA? An Tambayi Umar Me Ya sa Baka je Jana’izar Abubakar ba? Sai Umar Yace Saboda Huzaifa Bai je Ba.

Huzaifatul Yamani Shine Wanda Ya san Munafukai, Kuma Duk Wanda Huzaifa Bai je Jana’izar Sa Ba To Munafiki Ne.

Shin Ko Kunsan Cewa Amr Bin Ass Ne Yayi Sallah Ga Abubakar kuwa? Shin Kunsan Waye Amr kuwa? To ku duba; Al-isti’ab na Ibn Abdulbar Juz’i Na 1 Shafi Na 228. Siratul Halbiya Juz’i Na 3 Shafi Na 143. Al-fitna Bainas-Sahaba Shafi Na 80… Ku ganewa idonku.

Fadin Allah(swt):

ﻭَﺍﻟﺴَّﺎﺑِﻘُﻮﻥَ ﺍﻷَﻭَّﻟُﻮﻥَ ﻣِﻦَ ﺍﻟْﻤُﻬَﺎﺟِﺮِﻳﻦَ ﻭَﺍﻷَﻧْﺼَﺎﺭِ ﻭَﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﺍﺗَّﺒَﻌُﻮﻫُﻢْ ﺑِﺈِﺣْﺴَﺎﻥٍ ﺭَﺿِﻲَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻨْﻬُﻢْ ﻭَﺭَﺿُﻮﺍ ﻋَﻨْﻪُ ﻭَﺃَﻋَﺪَّ ﻟَﻬُﻢْ ﺟَﻨَّﺎﺕٍ ﺗَﺠْﺮِﻱ ﺗَﺤْﺘَﻬَﺎ ﺍﻷَﻧْﻬَﺎﺭُ ﺧَﺎﻟِﺪِﻳﻦَ ﻓِﻴﻬَﺎ ﺃَﺑَﺪًﺍ ﺫَﻟِﻚَ ﺍﻟْﻔَﻮْﺯُ ﺍﻟْﻌَﻈِﻴﻢُ.

“Kuma wadanda fara (shiga Musulunci) daga Muhajirin da Ansar da wadanda s**a biyo bayan su da kyautatawa, Allah Ya yarda da su; su ma sun yarda da Shi, kuma Ya yi masu tattalin gidan Al-janna; koramu suna gudana a karkashinsu, suna madawwama a cikinsu har abada. Wancan ne babban rabo mai girma”.

(Q : 9 : 100).

Saboda Allah tabbatar da ba dukkan Sahabbai ne “Sabikunal-auwalun” ba; bayan wannan ayar sai Allah ya ce;

وَمِمَّن حَولَكُم مِنَ الأَعرابِ مُنافِقونَ ۖ وَمِن أَهلِ المَدينَةِ ۖ مَرَدوا عَلَى النِّفاقِ لا تَعلَمُهُم ۖ نَحنُ نَعلَمُهُم ۚ سَنُعَذِّبُهُم مَرَّتَينِ ثُمَّ يُرَدّونَ إِلىٰ عَذابٍ عَظيمٍ.

“Kuma daga cikin wadanda ke tare da ku (Sahabbai); daga Larabawa akwai munafukai, haka kuma daga cikin mutanen Madina (akwai munafukai), sun kware a cikin munafunci, kai ba ka san su ba, mu ne muka san su, da sannu za mu yi musu azaba sau biyu, sannan kuma mu mayar da su zuwa ga azaba mai girma”.

(Q: 9 : 101).

Sannan kuma, Me harafin ﻣِﻦَ yake nufi a harshen Larabci? Me ya sa Allah ya ce “daga cikin muhajirun da Ansar” (ﻣِﻦَ ﺍﻟْﻤُﻬَﺎﺟِﺮِﻳﻦَ ﻭَﺍﻷَﻧْﺼَﺎﺭِ) kenan ba dukkan Sahabbai Muhajirun da Ansar ake nufi ayar ba?

Ya zaku yi da Sahabbai muhajirun da Ansar da suke cikin Fi’atul-bagiya, ‘Yan Jamal…? Ko kun koma ‘yan Qur’aniyyun ne baku yarda da Hadisai ba?

Idan ma kun koma ‘yan Qur’aniyyun ya zaku yi da fadin Allah(saw):

ﻭَﻣِﻤَّﻦْ ﺣَﻮْﻟَﻜُﻢْ ﻣِﻦَ ﺍﻟْﺄَﻋْﺮَﺍﺏِ ﻣُﻨَﺎﻓِﻘُﻮﻥَ ﻭَﻣِﻦْ ﺃَﻫْﻞِ ﺍﻟْﻤَﺪِﻳﻨَﺔِ ﻣَﺮَﺩُﻭﺍ ﻋَﻠَﻰ ﺍﻟﻨِّﻔَﺎﻕِ ﻟَﺎ ﺗَﻌْﻠَﻤُﻬُﻢْ ﻧَﺤْﻦُ ﻧَﻌْﻠَﻤُﻬُﻢْ ﺳَﻨُﻌَﺬِّﺑُﻬُﻢْ ﻣَﺮَّﺗَﻴْﻦِ ﺛُﻢَّ ﻳُﺮَﺩُّﻭﻥَ ﺇِﻟَﻰ ﻋَﺬَﺍﺏٍ ﻋَﻈِﻴﻢٍ.

Su waye ﺃَﻫْﻞِ ﺍﻟْﻤَﺪِﻳﻨَﺔِ? Shin akwai bambanci da tsakanin ﺃَﻫْﻞِ ﺍﻟْﻤَﺪِﻳﻨَﺔِ da ﺍﻷَﻧْﺼَﺎﺭِ a istilahin lokacin Annabi(saw)?

Idan ﺍﻷَﻧْﺼَﺎﺭِ sune ﺃَﻫْﻞِ ﺍﻟْﻤَﺪِﻳﻨَﺔِ to kenan hakan kara tabbatar ba dukkan Sahabbai ne Allah yake nufi a ayar:

ﻭَﺍﻟﺴَّﺎﺑِﻘُﻮﻥَ ﺍﻷَﻭَّﻟُﻮﻥَ ﻣِﻦَ ﺍﻟْﻤُﻬَﺎﺟِﺮِﻳﻦَ ﻭَﺍﻷَﻧْﺼَﺎﺭِ ﻭَﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﺍﺗَّﺒَﻌُﻮﻫُﻢْ ﺑِﺈِﺣْﺴَﺎﻥٍ ﺭَﺿِﻲَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻨْﻬُﻢْ ﻭَﺭَﺿُﻮﺍ ﻋَﻨْﻪُ ﻭَﺃَﻋَﺪَّ ﻟَﻬُﻢْ ﺟَﻨَّﺎﺕٍ ﺗَﺠْﺮِﻱ ﺗَﺤْﺘَﻬَﺎ ﺍﻷَﻧْﻬَﺎﺭُ ﺧَﺎﻟِﺪِﻳﻦَ ﻓِﻴﻬَﺎ ﺃَﺑَﺪًﺍ ﺫَﻟِﻚَ ﺍﻟْﻔَﻮْﺯُ ﺍﻟْﻌَﻈِﻴﻢُ.

Kenan ba dukkan Sahabbai ne masu imani na gaskiya ba? Shin su Munafukan Sahabbai ne? Kada ku manta fa; duk mai kin Imam Ali(as), to munafiki ne, inji Annabi(saw).

Kuma Annabi(saw) ya tabbatar mana akwai munafikai a cikin Sahabbai, kamar yanda yazo a wannan ruwayar:

ﺣﺪﺛﻨﺎ ﻭﻛﻴﻊ، ﺣﺪﺛﻨﺎ ﺳﻔﻴﺎﻥ، ﻋﻦ ﺳﻠﻤﺔ، ﻋﻦ ﻋﻴﺎﺽ ﺑﻦ ﻋﻴﺎﺽ، ﻋﻦﺃﺑﻴﻪ، ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻣﺴﻌﻮﺩ ﻗﺎﻝ: ﺧﻄﺒﻨﺎ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ‏(ﺹ‏) ﺧﻄﺒﺔ ﻓﺤﻤﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺃﺛﻨﻰ ﻋﻠﻴﻪ، ﺛﻢ ﻗﺎﻝ: ﺇﻥ ﻓﻴﻜﻢ ﻣﻨﺎﻓﻘﻴﻦ ﻓﻤﻦ ﺳﻤﻴﺖ ﻓﻠﻴﻘﻢ ﺛﻢ ﻗﺎﻝ: ﻗﻢ ﻳﺎ ﻓﻼﻥ ﻗﻢ ﻳﺎ ﻓﻼﻥ ﻗﻢ ﻳﺎ ﻓﻼﻥ ﺣﺘﻰ ﺳﻤﻰ ﺳﺘﺔ ﻭﺛﻼﺛﻴﻦ ﺭﺟﻼً ﺛﻢ ﻗﺎﻝ: ﺇﻥ ﻓﻴﻜﻢ ﺃﻭ ﻣﻨﻜﻢ ﻓﺈﺗﻘﻮﺍ ﺍﻟﻠﻪ، ﻗﺎﻝ: ﻓﻤﺮ ﻋﻤﺮ ﻋﻠﻰ ﺭﺟﻞ ﻣﻤﻦ ﺳﻤﻰ ﻣﻘﻨﻊ ﻗﺪ ﻛﺎﻥ ﻳﻌﺮﻓﻪ ﻗﺎﻝ: ﻣﺎ ﻟﻚ ﻗﺎﻝ: ﻓﺤﺪﺛﻪ ﺑﻤﺎ ﻗﺎﻝ ﺭﺳﻮﻝﺍﻟﻠﻪ(ﺹ‏) ﻓﻘﺎﻝ: ﺑﻌﺪﺍً ﻟﻚ ﺳﺎﺋﺮ ﺍﻟﻴﻮﻡ.

“Abi Mas’ud ya ce; …Manzan Allah(saw) ya yi mana khuduba, ya yi godiya ga Allah tare da yabo a gare shi, sannan ya ce: Lallai daga cikinku (Sahabbai) akwai munafikai! duk wanda na kira sunan shi ya mike tsaye!, sai ya ce: kai wane tashi! kai wane tashi! kai wane mike!, har sai da Manzan Allah(saw) ya tayar da mutum 36, sannan ya sake cewa: har yanzu daga cikinku akwai munafikai, ku ji tsoron Allah! (alamun basu kenan ba) mai ruwayar ya ce: sai Umar ya hadu da daya daga cikin wadanda Manzan Allah(saw) ya ce su tashi, ya rufe kansa amma Umar din ya gane shi, sai ya ce da shi: me ya same ka? sai ya ba shi labarin abin da ya faru da su a Masallaci, sai Umar ya ce da shi: Tir da kai! Allah ya nisantar da kai daga rahamarsa”.

(Musnadu Ahmad: Hadisi mai lamba: 21317. Dala’ilun-Nubuwwa na Baihaqi: Hadisi mai lamba: 2030. Al-bidaya wan nihaya na Ibnu kasir: j 5, s 33).

Wannan Hadisi ya tabbatar mana da akwai munafikai da yawa a cikin Sahabbai, kuma ba sukenan wadanda Annabi(saw) tayar ba. Idan suke nan me ya sa Annabi(saw) bayan ya gama taryar da 36; sai kuma ya cewa da Sahabbai kuji tsoron Allah? Sannan me ya sa Umar ya ke da alaka da Munafiki? Da alama lokacin da Annabi(saw) ya tayar da munafikan Umar baya nan? Kenan Umar bai fiye zama tare da Annabi(saw) ba?

Ingantattun Hadisai sun tabbatar mana akwai Sahabban da zasu shiga wutar Jahannamah:

ﺣﺪﺛﻨﺎ ﺃﺑﻮ ﺍﻟﻮﻟﻴﺪ ﺣﺪﺛﻨﺎ ﺷﻌﺒﺔ ﺃﺧﺒﺮﻧﺎ ﺍﻟﻤﻐﻴﺮﺓ ﺑﻦ ﺍﻟﻨﻌﻤﺎﻥ ﻗﺎﻝ ﺳﻤﻌﺖ ﺳﻌﻴﺪ ﺑﻦ ﺟﺒﻴﺮ ﻋﻦ ﺇﺑﻦ ﻋﺒﺎﺱ‏(ﺭ) ﻗﺎﻝ ﺧﻄﺐ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ(ﺹ) ﻓﻘﺎﻝ ﻳﺎ ﺃﻳﻬﺎ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺇﻧﻜﻢ ﻣﺤﺸﻮﺭﻭﻥ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﺣﻔﺎﺓ ﻋﺮﺍﺓ ﻏﺮﻻ ﺛﻢ ﻗﺎﻝ: “ﻛﻤﺎ ﺑﺪﺃﻧﺎ ﺃﻭﻝ ﺧﻠﻖ ﻧﻌﻴﺪﻩ ﻭﻋﺪﺍ ﻋﻠﻴﻨﺎ ﺇﻧﺎ ﻛﻨﺎ ﻓﺎﻋﻠﻴﻦ” ﺇﻟﻰ ﺁﺧﺮ ﺍﻵﻳﺔ ﺛﻢ ﻗﺎﻝ ﺃﻻ ﻭﺇﻥ ﺃﻭﻝ ﺍﻟﺨﻼﺋﻖ ﻳﻜﺴﻰ ﻳﻮﻡ ﺍﻟﻘﻴﺎﻣﺔ ﺇﺑﺮﺍﻫﻴﻢ. ﺃﻻ ﻭﺇﻧﻪ ﻳﺠﺎﺀ ﺑﺮﺟﺎﻝ ﻣﻦ ﺃﻣﺘﻲ ﻓﻴﺆﺧﺬ ﺑﻬﻢ ﺫﺍﺕ ﺍﻟﺸﻤﺎﻝ ﻓﺄﻗﻮﻝ ﻳﺎ ﺭﺏ ﺃصحبي! ﻓﻴﻘﺎﻝ ﺇﻧﻚ ﻻ ﺗﺪﺭﻱ ﻣﺎ ﺃﺣﺪﺛﻮﺍ ﺑﻌﺪﻙ ﻓﺄﻗﻮﻝ ﻛﻤﺎ ﻗﺎﻝ ﺍﻟﻌﺒﺪ ﺍﻟﺼﺎﻟﺢ “ﻭﻛﻨﺖ ﻋﻠﻴﻬﻢ ﺷﻬﻴﺪﺍ ﻣﺎ ﺩﻣﺖ ﻓﻴﻬﻢ ﻓﻠﻤﺎ ﺗﻮﻓﻴﺘﻨﻲ ﻛﻨﺖ ﺃﻧﺖ ﺍﻟﺮﻗﻴﺐ ﻋﻠﻴﻬﻢ ﻭﺃﻧﺖ ﻋﻠﻰ ﻛﻞ ﺷﻲﺀ ﺷﻬﻴﺪ” ﻓﻴﻘﺎﻝ ﺇﻥ ﻫﺆﻻﺀ ﻟﻢ ﻳﺰﺍﻟﻮﺍ ﻣﺮﺗﺪﻳﻦ ﻋﻠﻰ ﺃﻋﻘﺎﺑﻬﻢ ﻣﻨﺬ ﻓﺎﺭﻗﺘﻬﻢ.
“…Manzan Allah(saw) ya yi khuduba ya ce:” ya ku mutane lallai za’a tashe ku a gaban Allah ba takalmi da sutura, ba kaciya, sannan ya karanto fadar Allah(swt): “kamar yanda muka fari halitta haka za mu maida ta, Alkawali ne a kanmu kuma lallai mu masu aikatawa ne”. Sannan ya ce: farkon wanda za’a fara yiwa sutura a ranar Al-kiyama shine Annabi Ibrahim(as). Kuma lallai za’a zo da wasu mazaje daga Al’ummata, sai a bi ta hanyar wuta da su, sai in ce ya rabbi ai wadannan Sahabbaina ne fa! sai a ce da ni ai ba ka san abin da s**a aikata ba a bayanka, sun canza bayan wafatinka. sai in fada kamar yadda Annabi Isa(as) ya fada: “Ni mai shaida ne a kansu matukar ina a cikinsu, amma a lokacinda ka karbi raina to kai ne ka fi kusanci dasu, kuma kai mai shaida ne a kan komai.

(Sahihul Buhari, hadisi mai lamba 6528, da 609, da 4259. Sahihu Muslim, hadisi mai lamba 368, da 4253. Musnadu Ahmad, hadisi mai lamba 7652. Sunan na Ibnu Maja, hadisi mai lamba 3048. Mustadrak na Hakim, hadisi mai lamba 6958).

Sahabi Barra’u bin Azib ya tabbatar da Sahabbai da yawa sun canza (ta hanyar canza wasiyar Annabi(saw) bayan wafatinsa(saw):

ﺣﺪﺛﻨﻲ ﺃﺣﻤﺪ ﺑﻦ ﺇﺷﻜﺎﺏ ﺣﺪﺛﻨﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﺑﻦ ﻓﻀﻴﻞ ﻋﻦ ﺍﻟﻌﻼﺀ ﺑﻦ ﺍﻟﻤﺴﻴﺐ ﻋﻦ ﺃﺑﻴﻪ ﻗﺎﻝ ﻟﻘﻴﺖ ﺍﻟﺒﺮﺍﺀ ﺑﻦ ﻋﺎﺯﺏ ﻓﻘﻠﺖ ﻃﻮﺑﻰ ﻟﻚ ﺻﺤﺒﺖ ﺍﻟﻨﺒﻲ ‏(ﺹ) ﻭﺑﺎﻳﻌﺘﻪ ﺗﺤﺖ ﺍﻟﺸﺠﺮﺓ ﻓﻘﺎﻝ ﻳﺎ ﺍﺑﻦ ﺃﺧﻲ ﺇﻧﻚ ﻻ ﺗﺪﺭﻱ ﻣﺎ ﺃﺣﺪﺛﻨﺎ ﺑﻌﺪﻩ.

“Al-Musayyib ya ce na hadu da Barra’u Bin Azib. Sai na ce; ku (Sahabbai) kun dace, kun zauna da Annabi(saw) kuma kun yi masa mubaya’a a karkashin bishiya. Sai Barra’u yayi ajeyar zuciya ya ce; ai baka san abinda mukayi ba a bayan (wafatin Annabi(saw) ba ne!”.

(ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ، ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﻤﻐﺎﺯﻱ، ﺑﺎﺏ ﻏﺰﻭﺓ ﺍﻟﺤﺪﻳﺒﻴﺔ).

Kenan Sahabbai da yawa; har da wadanda s**a yiwa Annabi Muhammad(saw) mubaya’a a karkashin bishiya (bi’atur-ridwan) sun canza; bayan wafatin Annabi(saw)?

Saboda haka, duk wanda yace kacokaf din Sahabbai yardaddun Allah ne, to ya karyata ayoyin Qur’ani da ingantattun hadisai. Haka ma duk wanda yace; kacokaf dinsu mutanen banza ne, shima ya karyata ayoyin Qur’ani da ingantattun hadisai.

A takaice, wadannan ayoyin da ake kafa hujjar alkawarin Al-Jannah ga dukkan Sahabbai da su; sun sauka ne akan Imam Ali(as) da Sahhaban da s**a lizimce shi; domin shine ruwayoyi ingantattu s**a tabbatar da yayi infaki, yayi jihadi; har ya kashe kaso mai yawa a mafi yawan yakokan da Annabi(saw) yayi, kuma ya rigya dukkan Sahabbai imani, doriya akan cewa; Annabi(saw) ya tabbatar mana da cewa; duk Sahabin da bai son Imam Ali(as) munafiki ne.

12/07/2023

Salam tambaya inaso nasan babancin shi'a Imamiyya da shi'a Jafariyya nagode ?

Amsa:

Shi’a imamiyya da Shia Ja’afariyya duk abu guda ne!

Idan akace Shia Imamiyya Ana nufin magoya (Masu bin Tafarkin Imamai 12) da Annabi ya bar mana wasiya da muyi riko dasu a bayan sa!

Shia Ja’afariya shima duk Abu gudane domin imam Jafar yana daga cikin imamai 12 da Annabi Muhammad yabar mana!

Ana cewa Shia Ja’afariya ne saboda a zamaninsa ne Ilimin Gidan Annafta Wato Ahlulbait ya yadu cikin Al Umma ta dalilin Imam Jafar Assadiq!

Kusan duk imamai sun rayu cikin takura ne da zalinci ga sarakunan zamaninsa!

A wurin Shi'a Ithna Ashariyya da Shi'a imamiyya suna ƙaddara Imam Jafar Sadiq (a.s) a matsayin Imami na 6 daga Jerin Imaman tsira, ana jinginawa gareshi cewa: Shine ya yada Fiqhun Shi'a da kuma aqida ta bangaren tauhidi, sabida hakanne ma ake kiran shi'a Ithna Ashariyya da Mazhabar "Ja'afariyya"

Wallahu A'alamu.

Muna maraba da tambayoyin ku kofa a bude take a ko wani lokaci !

Address

Jajà Ung/borno, Railway Road

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Umar Gwaskwaram posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Grocery Store?

Share