05/08/2023
Shugaba Tinubu zai ji dadin aiki da tsohon Gwamna Matawalle Kuma ba zai yi nadamar zaben a majalisar zartarwar kasa ba, inji Comr Anas Abdullahi Kaura
Mai magana da yawun tsohon gwamnan jihar Zamfara Comr Anas Abdullahi Kaura ya yaba wa shugaban kasar Nigeria Alhaji Bola Ahmed Tinubu bisa mika sunan mai gidansa Bello Matawalle domin majalisa ta tantance shi a matsayin Minista a da zai kasance cikin majalisar zartarwar kasar.
Anas Abdullahi Kaurawanda yace hakan ya nuna cewa shugaba Tinubu mutum ne da ya san alkairi, ya san masoyansa, kuma yake maida alkairi da alkairi, domin irin jajircewar da Bello Matawalle ya yi akan Tinubu.
Mai magana da yawun tsohon Gwamnn, ya kara cewa ta sanadiyyar jajircewa da kuma kokarin Mohammed Bello Matawalle ya yi ne aka kawo kuri’a mafi rinjaye daga arewacin Nijeriya. Wannan himma da ya bayar ne ya sa har ya samu matsala a zaben Gwamna ya fadi.
Idan za ku iya tunawa dai, Bello Matawalle shi ne shugaban yakin neman zaben Ahmed Bola Tinubu na Arewacin Nijeriya, da mutane suke ganin ta dalilinsa yankin ya yi wa shugaba Tinubu ruwan kuri’un musamman daga jihar Zamfara.
A ranar biyu ga watan Agusta shekara ta 2023, shugaban kasar ya mika sunan Bello Matawalle a matsayin minista da kuma sauran mutane, wanda hakan ya yi musu matukar dadi a cewar mai magana da yawunsa, domin sun shaida cewa Tinubu mutum ne mai cika alkawari kuma wanda ya san masoyansa, duba da irin gudummawar da Bello Matawalle ya bashi, Matawalle ya jajirce kwarai da gaske tun daga lokacin da shugaban kasar ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa, tun daga zaben fidda gwani na jam’iyya ya jajirce wajen hada kan ragowar gwamnoni domin ganin an samu nassara.
Mai magana da yawun tsohon Gwamnan ya yi zargin cewa a lokacin da ake yakin neman zabe an kirkiro da maganar canjin kudi ne da gangan saboda ba a so Tinubu ya ci zabe, wanda kowa ya san yadda al'ummar wannan kasar s**a shiga cikin tashin hankali da matsi na rashin takardar kudi a hannu, musamman masu k