30/10/2025
DA SUNAN GWAGWARMAYA KA JEFA KANKA CIKIN DAMUWA๐๐.
Kotun Tarayya ta ajiye Lauya da wasu mutum huษu a gidan gyaran hali bisa zargin cin mutunci ta yanar gizo da kuma neman kuษin fansa a wurin Sanata Shehu Buba.
Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin a tsare wani lauya mai suna Ahmed Abdulrahman tare da wasu mutane huษu a sashen binciken manyan laifuka na โyan sanda (FCID) har zuwa ranar 10 ga watan Nuwamba, bayan gurfanar da su bisa tuhumomi 11 da s**a shafi cin mutunci ta yanar gizo (cyber bullying), zamba ta hanyar yanar gizo (advance fee fraud) da neman karษar kuษin fansa (extortion).
Wannan gurfanarwar, wacce Sufeto Janar na โYan Sanda (IGP) ya shigar, ta waษannan mutum biyar bisa zargin yi wa Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Tsaro da Leken Asiri, Sanata Shehu Umar Buba, barazana da batanci.
Sauran waษanda ake tuhuma tare da shi su ne Daure David, Ishaq Abubakar Muhammed, Abdulrashid Abdullahi Musa, da Nasiru Usman Abubakar. Saidai Dukkaninsu sun ฦi amincewa da laifin da ake tuhumar su da shi a gaban Mai Shariโa Rita Offili Ajumogobia a yau Alhamis.
Zargin Cin Mutunci da Neman Fansa
Takardar tuhumar ta bayyana cewa sun haษa kai wajen cin mutuncin Sanata ta hanyar yanar gizo. A cikin ษaya daga cikin tuhume-tuhumen, ana zargin Lauya Abdulrahman da aikawa da wani bidiyo ta shafinsa na TikTok (โKibanna Channelโ) da kuma tashar YouTube domin ษata sunan ษan majalisar.