Zauren Hasken Musulunci

Zauren Hasken Musulunci Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Zauren Hasken Musulunci, Grocers, Pantami stadium, Gombe.

SALATIN ANNABI…..-Manzon Allah SAW ya ce: "Ku yawaita salati a gareni a daren Juma'a da ranar Juma'a, wanda yayi salati ...
17/04/2026

SALATIN ANNABI…..

-Manzon Allah SAW ya ce: "Ku yawaita salati a gareni a daren Juma'a da ranar Juma'a, wanda yayi salati daya a gareni, Allah zai yi salati goma a gareshi.

-Kuma ma wani qarin daraja da daukaka shine, duk wanda ya lizimci yawaita salati ga Manzon Allah damuwanshi da bakinciki za su gushe, farin ciki da kwanciyar hankali za su kusance shi.

-Yana daga cikin mafi soyuwan mutane ya kasance mai biyayya gare shi, kuma son Annabi wajibi ne a kan kowane Musulmi mai tauhidi. Kuma yana daga cikin son sa (S A W) yi masa salati da yi masa haƙiƙanin biyayya.

-Kuma yana daga cikin haƙiƙanin yi wa Annabi (S A W) salati to ya zama kana koyi da Manzon Allah a cikin komai.

-Kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce; “Marowaci shi ne wanda aka ambace ni yaji amma bai yi mini salati ba.

-Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce, Allah yana da waɗansu Mala’iku a bayan qasa, suna isar mini da sallama daga al’ummata.

-Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce; “Babu wani wanda zai yi mini sallama face Allah ya dawo mini da raina na amsa masa sallamarsa”.

‘Yan uwa masu Albarka muna gayyatarku zuwa ga taska wadda rahamar ta ba ta qarewa, taska wadda babu asara da tabewa acikinta, taska wadda take bude kofofin alkairi take kuma kulle kofofin sharri, taskar da duk wanda ya k**a sai ya tsira duniya da lahira, domin acikinta akwai gyaran zuciya idan zuciya ta gyaru jiki da aiki zasu tsarkaka, wanan taska ita ce koyi da Manzon Allah da yawaita yi masa salati acikin halin farin ciki da halin damuwa. Hakika Allah baya kunyatar da wanda yake koyi da Annabi kuma yake masa salati.

اَللّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ، وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ. اَللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ، وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ.

YAU ALKALAMI NA ZAI YI RUBUTU NE AKAN MATAN DA AKE BA SU RIKON YARAN MIJI KO MARAYU...Akwai wasu abubuwan da suke faruwa...
10/04/2026

YAU ALKALAMI NA ZAI YI RUBUTU NE AKAN MATAN DA AKE BA SU RIKON YARAN MIJI KO MARAYU...

Akwai wasu abubuwan da suke faruwa kullum a rayuwarmu na rashin imani da halin ko-in-kula da wasu mata suke nunawa a kan yaran mijinsu wanda mahaifiyarsu ta rasu, ko auren ya kare, ko kuma wasu marayu da aka kawo musu raino. Idan kaji irin wani cin mutunci, tozarci, da wulakanci da yaran nan suke tsintar kansu a ciki, wallahi sai ka zubar da kwalla.

Wallahi mata ku ji tsoron Allah, Kina da naki yaran a gida suna cin abinci mai kyau, suna sanye da kaya masu kyau, amma yaron da ba ke kika haife shi ba ya koma tamkar bawan gidan. Ke ce bashi aikin wanke-wanke tun da sassafe, ke ce rage masa abinci, ke ce yi masa duka akan abin da bai taka kara ya karya ba. Kina ganin kinyi wayo ko? Kina ganin babu wanda zai rama masa?

Shin yau idan wani abu ya same ki (Allah Ya kiyaye), wata ta rika yi wa naki yaran irin mugun rikon da k**e yi wa yaran wasu, zaki ji dadi a kabarinki? Duk macen da ta dauki yaron wata ta rike shi amana tamkar nata, wallahi Allah zai albarkaci nata yaran a duniya da lahira. Amma wacce take wulakanta marayu ko yaran miji, ita ma tana jiran nata sak**akon.

Gare ku maza, ina son ku sani yara amanar Allah ne a wajenku, Abin kunya ne ka zama uba a gida amma ka kasa tsayawa ka kare hakkin danka ko 'yarka don kawai kana tsoron bacin ran matarka. Ka ga yaro yana ramewa, yana tsoron shiga gida, ya rasa gata, amma ka yi shiru ka zuba ido. Wallahi Allah zai tambaye ka wannan amanar da ka bari aka wulakanta a gabanka.

Matasa da iyaye, mu gyara mu'amalarku da marayu da yaran miji, don bamu san wanda zai rike namu a gobe ba.

Allah ya bamu ikon sauke amana.
Kada ku Manta kuyi following din Wannan shafi Mai Albarka

•┈┈••✦FALALAR RANAR JUMA’A✦••┈┈•1-Itace mafi alkhairin ranaku a wajan Allah.Manzon Allahﷺ yace;*(Mafi alkhairin ranaku a...
03/04/2026

•┈┈••✦FALALAR RANAR JUMA’A✦••┈┈•

1-Itace mafi alkhairin ranaku a wajan Allah.
Manzon Allahﷺ yace;
*(Mafi alkhairin ranaku a wajan Allah, itace ranar juma’a)*
@صححه الألباني فيالسلسلة الصحيحة – رقم: (1502) صحيح الجامع – رقم: (1098)

2-Mafi alkhairin salloli a wajan Allah tana cikin ranar juma’a.

Manzon Allahﷺ yace;
*(Mafi alkhairin salloli a wajan Allah, itace sallar assubar Ranar juma’a)*
@السلسلة الصحيحة الألباني صحيح – رقم: 1566.

3-Manzon Allah ﷺ yayi Umarni akan mu yawaita yin Salati a gareshi a Daren juma’a da yinin Juma’a.

Manzon Allahﷺ yace;
*(Ku yawaita yin salati a gareni a Daren juma’a da yinin juma’a, dukkan wanda yayi min Salati guda daya,Allah zai yi masa Salati guda goma)*
@صحيح الجامع الألباني حسن – رقم: 1209

4-Wanda ya mutu ranar juma’a ko Daren juma’a, Allah yana bashi kariya daga fitinar Qabari.

Manzon Allahﷺ yace;
*(Babu wani musulmi da zai mutu a ranar juma’a ko Daren juma’a, face sai Allah ya tseratar da shi daga fitinar Qabari)*.
@حسنه الألباني في صحيح الترمذي – رقم: (1074) ، تخريج مشكاة المصابيح – رقم: (1316) الألباني :إسناده حسن أو صحيح لغيره.

5-Samun kankarar zunubai daga juma’a zuwa wata juma’ar.

Manzon Allahﷺ yace;
*(Salloli guda biyar na farilla,da juma’a zuwa wata juma’a, ana kankare zunuban da ke tsakaninsu idan an nisanci manyan laifuka)*..@صحيح مسلم -رقم:(233)
Kada amanta da falala karatun سورة الكهف
Koda ayoyin goman farko na surar ka karanta.

Imamul-Hakim (r.h) Yace:*
"Lallai Duk Wanda Ya Karanta Suratul-Kahfi A Ranar Juma'a, Za'a Haskaka Masa Haske Na Daga Abinda Yake A Tsakanin Juma'a Biyu"
رواه الحاكم في المستدرك مرفوعا, وصححه الألباني..

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN!Allah Ya yi wa daya daga cikin iyayen kungiyar Izala a Jihar Gombe, Alhaji Sa’idu Mu...
26/03/2026

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN!

Allah Ya yi wa daya daga cikin iyayen kungiyar Izala a Jihar Gombe, Alhaji Sa’idu Muhammad (Marafan Tumu), rasuwa a safiyar wannan Alhamis, bayan gajeruwar jinya a wani asibiti da ke birnin Kano. Lamarin ya faru ne bayan dawowarsa daga ibadar Umrah, kafin ya iso Gombe.

Ana sa ran, idan Allah Ya kawo gawarsa, za a yi masa jana’iza a Masallacin JIBWIS na Bolari, Gombe, a yammacin yau Alhamis, kusan ƙarfe 4:00 na yamma, In sha Allah, gwargwadon lokacin da gawar za ta iso.

Marafa mutum ne mai ƙoƙari wajen gina masallatai, tallafa wa addini, da sauran ayyukan alheri.

Allah Ya gafarta masa, Ya jikansa da rahama, Ya sanya Aljannatul Firdausi ce makomarsa. Ameen.

SUNNONI DA LADUBBAN RANAR IDI❶- [Yin wanka kafin fita zuwa salla]فقد صح في الموطأ وغيره أَنَّ عَبْدَ اللَّهِ بْنَ عُمَرَ...
19/03/2026

SUNNONI DA LADUBBAN RANAR IDI

❶- [Yin wanka kafin fita zuwa salla]
فقد صح في الموطأ وغيره أَنَّ عَبْدَ اللَّهِ بْنَ عُمَرَ رضي الله عنه:
"Ya kasance yana wanka ranar ƙaramar salla kafin ya fita zuwa salla".
📓📔موطأ مالك 384 صححه
الألباني في الإرواء

❁ عن سعيد بن المسيب رحمه الله قال:
"Sunnah a ƙaramar salla guda uku ce:
i. Yin tattaki zuwa salla (Tafiya salla a ƙasa)
ii. Da cin Abinci kafin tafiya zuwa Masallaci
iii. Da yin wanka".
📔📓(1/102) أحكام العيدين للفريابي
📔📓صحَّح إسناده الألباني الإرواء 3/104

❁ قال ابن قدامة رحمه الله:
"Wannan yana nuna cewa lallai kwalliya a wajen su, a wannan wajen, abu ne sannan ne".
📔📓المغني 2/274

┉┅━━━✺❁✺━━━┅┉

❷-[Cin Abinci kafin fita zuwa salla a ƙaramar salla. Da barin cin Abinci sai bayan an dawo masallaci a Idin Layya]
An sunnan ta kafin fita zuwa salla a ƙaramar salla da mutum yaci Dabinai witri.
Daga Anas Bin Malik Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya kasance baya fita ranar ƙaramar salla har sai yaci Dabinai, kuma yana cin su witri".
📓📔رواه البخاري 953

┉┅━━━✺❁✺━━━┅┉

❸-[Yin Barka]
❉ Yana daga ladubban Idi yin Barka (da lafazi) mai daɗi wadda mutane suke yiwa junan su, duk yadda lafazin ta ya kasance, misali faɗin sashen su ga sashe:
✦ "Allah ya karɓa mana daku" ✦
da abinda yayi k**a da wannan na daga magana na Barka na halal
❁ Daga Jubair bin Nufair ya ce: "Sahabban Manzon Allah ﷺ sun kasance suna cewa idan sashen su ya haɗu da sashe:
[Allah ya karɓa mana da kai] 2/517
❁ الراوي: جبير بن نفير
📓📔الألباني تمام المنة 354 إسناده صحيح
📓📔ابن حجر العسقلاني فتح الباري لابن حجر 2/517 إسناده حسن

┉┅━━━✺❁✺━━━┅┉

❹-[Tafiya zuwa Masallaci a wata hanya, da dawowa a wata hanyar daban/Chanza Hanya]
عَنْ جَابِرِ بْنِ عَبْدِ اللَّهِ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُمَا قَالَ:
"Annabi ﷺ ya kasance a ranar Idi yana chanza hanya".
📓📔 البخاري 986

┉┅━━━✺❁✺━━━┅┉

❺-[Tafiya zuwa Masallaci a ƙasa/Tattaki]
عَنِ ابْنِ عُمَرَ، رضي الله عنهما، قَالَ:
"Manzon Allah ﷺ ya kasance yana fita zuwa Idi a ƙasa, kuma yana dawowa a ƙasa"

BAN-KWANA DA WATAN RAMADAN MAI CIKE DA ALHERI: Watan Ramadan wata ne da bawa ke abota da ibada da addu'oi, sadaka, tilaw...
18/03/2026

BAN-KWANA DA WATAN RAMADAN MAI CIKE DA ALHERI:

Watan Ramadan wata ne da bawa ke abota da ibada da addu'oi, sadaka, tilawa da sauran aiyukan alheri.

Kwanaki Ramadan na nuna mana Amfanin kusaci da zama da Mutanen kirki, da yin abokai nagari

Aiyukan da'a na wata guda a watan Ramadan na taimaka wa mutum wajen gyara halaye da kusantar da bawa zuwa ga Allah

Acikin wannan wata na gane cewa abokai na gari suna ƙarfafa mutum wajen aikata alheri, suna kuma nusantar dashi a lokacin da ya manta ko ya aikata kuskure.

Aikin alheri da zama da Mutanen kirki ba iya Ramadan kaɗai ake so muyi ba, a’a, hanya ce da take taimakawa mutum ya tsaya kan tafarkin alheri a kowane lokaci.

Allah ya kar6a mana yasa mu dace, amin

Kowace cikin waɗannan ayoyin, addu'a ce mai tsada:ربّ إني لما أنزلت إليّ من خير فقيرYa Ubangijina! Lallai ni mai tsanani...
15/03/2026

Kowace cikin waɗannan ayoyin, addu'a ce mai tsada:

ربّ إني لما أنزلت إليّ من خير فقير
Ya Ubangijina! Lallai ni mai tsananin buƙata ne ga duk wani alheri da Ka saukar mini.
ربّ لا تذرني فرداً وأنت خير الوارثين
Ya Ubangijina! Kada Ka bar ni ni kaɗai (ba tare da zuri’a ba), alhali Kai ne Mafi alherin masu gado.
ربّ إني مسني الضر وأنت أرحم الراحمين
Ya Ubangijina! Lallai cuta ta same ni, kuma Kai ne Mafi jin ƙai daga masu jin ƙai.
ربّ إني مغلوب فانتصر
Ya Ubangijina! Lallai an rinjaye ni, don haka Ka ba ni nasara.
ربّ اشرح لي صدري ويسرلي أمري
Ya Ubangijina! Ka buɗe mini ƙirjina, kuma Ka sauƙaƙa mini al’amurana.
ربّ إني ظلمت نفسي فاغفرلي
Ya Ubangijina! Lallai na zalunci kaina, don haka Ka gafarta mini.
ربّ أعوذ بك من همزات الشياطين
Ya Ubangijina! Ina neman tsarinka daga waswasi da tunzurar shaiɗanu.
ربّ اجعلني مقيم الصلاة ومن ذريتي ربنا وتقبل دعاء
Ya Ubangijina! Ka sanya ni mai tsayar da salla, ni da zuri’ata. Ya Ubangijinmu! Kuma Ka karɓi addu’ata.

Ya Allah, k**ar yadda Ka ba mu damar Dauka A wannan rana ta Ashirin da Uku:   Ka karɓi azuminmu da sallolinmu. Ka yafe m...
12/03/2026

Ya Allah, k**ar yadda Ka ba mu damar Dauka A wannan rana ta Ashirin da Uku:

Ka karɓi azuminmu da sallolinmu.
Ka yafe mana kurakuranmu na bayyane da na ɓoye.
Ka sanya rahamarka ta lullube mu.

Ya Allah, Ka sa mu dace da falalar kwanakin nan na ƙarshe,
Ka ba mu ikon yin ibada da zuciya mai tsarki,
Ka sa mu dace da Lailatul Qadr.

Duk wanda yake cikin damuwa, Ka sauƙaƙa masa.
Duk wanda yake cikin buƙata, Ka biya masa.
Duk wanda yake neman alkhairi, Ka ba shi fiye da abin da yake fata.

Allah Ya karɓa. 🤲🌙

🌌LAILATUL QADRI🌌●Dare ne mai daraja da alkhairai, dare mai cike da aminci, daren da ya fi watanni dubu alkhairi.●Manzon ...
12/03/2026

🌌LAILATUL QADRI🌌

●Dare ne mai daraja da alkhairai, dare mai cike da aminci, daren da ya fi watanni dubu alkhairi.

●Manzon Allah SAW ya kasance yana k'ara damara a goman k'arshe, yana raya dukkan dararrakinsa, kuma yana tada iyalansa.

●Ana kirdadon wannan dare mai albarka ne a daren 21, 23, 25, 27, 29.

●Wanda ya tsayu ma wannan dare yana mai imani mai neman lada an gafarta masa zunubansa da s**a gabata (Bukhary da Muslim).

●Daga cikin alamomin wannan dare: Shi dare ne mai matsakaicin yanayi, babu zafi babu sanyi, sannan a wayewar garin wannan dare rana tana zama mara zafi da launin jaa.

●Wanda Allah Yasa ya dace da wannan dare, to ya yawaita Ibada da Addu'a, Karatun Alkur'ani, da kuma yawaita Addu'ar:

●ALLAHUMMA INNAKA AFUWWUN TUHIBBUL AFWA FA'FU ANNIY

Azumi sirri ne tsakanin bawa da Ubangijinsa;ba ido ke ganinsa ba, amma Allah yana ganinsa.Shi ya sa ladan azumi ba a ƙid...
11/03/2026

Azumi sirri ne tsakanin bawa da Ubangijinsa;
ba ido ke ganinsa ba, amma Allah yana ganinsa.
Shi ya sa ladan azumi ba a ƙididdige shi,
domin Allah da kansa ne ke saka masa.

Azumi ba yunwa ba ne kawai; horo ne na zuciya.
Wanda ya koyi hana cikinsa, zai iya hana zuciyarsa bin son zuciya.

Azumi makaranta ce ta haƙuri, darasi ne na tsoron Allah,
kuma hanya ce ta tsarkake zuciya kafin gyaran halayya.

Annabi ﷺ yana yawan yin addu’a musamman a lokacin azumi, yana roƙon Allah gafara da rahama.

Duk wanda ya azumci watan Ramadan da imani da yana nema lada daga Allah, Allah zai gafarta masa zunubansa.

(Bukhari & Muslim)

Allah Ya sa mu da iyalanmu mu kasance cikin zaman lafiya da wadatar zuciya har abada. Allah Ya biya mana buƙatunmu, Ya karɓi dukkan addu’o’inmu, Ya kawar mana da duk wata wahala, Ya kare mu daga Shaiɗan da dukkan wani sharri.
Allah ya ba mu dacewa mu riski Lailatul Qadr, ya karɓi ibadunmu. 🤲✨

Amin Ya Rabbal Alamin.

RAMADAN RANA TA 2️⃣0️⃣.⛔Falalar Goman Ƙarshe na RamadanTambaya: Mun san cewa goman ƙarshe na Ramadan suna da falala mai ...
09/03/2026

RAMADAN RANA TA 2️⃣0️⃣.
⛔Falalar Goman Ƙarshe na Ramadan

Tambaya: Mun san cewa goman ƙarshe na Ramadan suna da falala mai girma da matsayi mai daraja. Muna roƙon Sheikh ya bayyana mana falalar waɗannan kwanaki.

Amsa daga Sheikh Al-Allamah Muhammad ibn Salih al‑Uthaymeen رحمه الله:

Alhamdulillahi, tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabinmu Muhammad ﷺ da iyalansa da sahabbansa baki ɗaya.

Goman ƙarshe na Ramadan su ne mafi falala a cikin watan Ramadan. Saboda haka Annabi ﷺ ya kasance yana keɓance su da Iʿitikafi, domin neman daren Laylat al‑Qadr.

A cikin waɗannan darare akwai Daren Lailatul Qadr, wanda Allah Ya ce a cikin Qur'an: Lailatul Qadr ta fi wata dubu (1000) alheri.

Annabi ﷺ ya kasance yana ƙara ƙoƙari a cikin waɗannan darare, yana yin sallar dare gaba ɗaya. Don haka ya dace ga musulmi ya:

Yi ƙoƙari wajen sallar dare (Qiyamul-Lail)

Tsawaita karatun Al-Qur’ani, ruku’i da sujuda

Idan yana tare da liman a sallar tarawihi ko tahajjud, ya zauna tare da shi har sai ya gama, domin Annabi ﷺ ya ce: Duk wanda ya yi salla tare da liman har sai da ya gama, za a rubuta masa ladan tsayuwar dare gaba ɗaya.

A ƙarshen waɗannan kwanaki kuma akwai:

Yawaita kabbara (Takbir) ga Allah

Fitar da Zakkatul Fitr kafin sallar Idi.
Saboda Annabi ﷺ ya ce: Idan aka ba da ita kafin sallar Idi, to zakka ce karɓaɓɓiya.

Saboda haka ya wajaba a bayar da Zakkatul Fitr kafin sallar Idi, wato a ranar Idi kafin a fita sallah.

Daga: Silsilatul Fatawa Nur ‘Ala Ad-Darb 154.

Zauren Hasken Musulunci .

Address

Pantami Stadium
Gombe

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zauren Hasken Musulunci posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zauren Hasken Musulunci:

Share

Category