23/07/2026
Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa duk wata haɗakar siyasa tsakanin Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso gabanin zaɓen 2027 ba za ta yi nasara a Jihar Kano ba.
Ganduje ya ce tikitin da ake hasashen za a kafa ba shi da ƙarfin siyasa, jagoranci da kuma abin da zai ja hankalin al’ummar Kano su ba shi goyon baya. Ya jaddada cewa irin wannan haɗaka “ta mutu tun kafin ta fara” a Kano, yana mai cewa ba za ta iya ƙalubalantar ƙarfin siyasar APC a jihar ba.