17/04/2026
Alhaji Musa Ɗan Kwairo — Gwarzon Mawakin Gargajiya na Hausa
An haifi Alhaji Musa Ɗan Kwairo a garin Bakura, Jihar Zamfara, a farkon shekarun 1909. Tun yana ƙarami ya nuna baiwar fasaha da ƙaunar kiɗan gargajiya, abin da ya kai shi zama ɗaya daga cikin fitattun mawakan Hausa a tarihi.
Musa Ɗan Kwairo ya taka muhimmiyar rawa wajen adanawa da yaɗa al’adun Arewa ta hanyar kiɗa. Wakokinsa sun haɗa sauti mai armashi da hikima, suna taɓo batutuwa kamar sarauta, jarumta, soyayya, haɗin kai da kuma darussa na rayuwa.
Ya yi amfani da kayan kiɗan gargajiya kamar kotso, tare da salon rerawa mai ɗauke da labari da jan hankali. Wannan ya sa wakokinsa s**a zama abin so ga al’umma daga kowane ɓangare.
Daga cikin fitattun wakokinsa akwai:
Mai Dubun Nasara, Yan Arewa, Sarkin Daura, Noma Babar Sana’a, Ahmadu Bello Sardauna, Ado Bayero da sauransu.
Musa Ɗan Kwairo ya samu girmamawa da lambobin yabo da dama saboda gudunmawarsa ga al’adu da kiɗan Hausa.
Ya rasu a ranar 3 ga Satumba, 1991, amma tarihinsa da wakokinsa na ci gaba da rayuwa a zukatan mutane har yau.
Allah ya jikansa da rahama, ya gafarta masa. 🤲