Labarai masu Dadi da ban al'jabi

Labarai masu Dadi da ban al'jabi Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Labarai masu Dadi da ban al'jabi, Grocers, Kaduna Road, Suleja.

03/03/2026

Labari: Yarinyar da Ta Gaskata da Mafarkinta
A wani ƙauye mai nisa, akwai wata yarinya mai suna Amina. Amina ba ta da kuɗi, amma tana da babban buri — ta zama malamar Qur’ani domin ta koyar da yara.
Mutane da yawa suna cewa:
“Ke? Malama? Ai ba ki da gata, ba ki da kowa a baya!”
Amma Amina kullum tana tuna maganar Annabi ﷺ:
“Duk wanda ya nemi ilimi, Allah zai sauƙaƙa masa hanya zuwa Aljanna.”
Sai ta dage da karatu, tana tashi da dare, tana haddace Qur’ani a ƙarƙashin hasken fitila. Ta sha wahala, ta sha kuka, amma ba ta taɓa daina ba.
Shekaru s**a wuce…
Amina ta zama malama mai daraja. Yara da yawa sun haddace Qur’ani a hannunta. Mutanen da s**a taɓa raina ta, su ne suke kawo ‘ya’yansu wurinta.
Wata rana aka tambaye ta:
“Me ya sa ba ki daina ba duk da wahala?”
Sai ta ce:
“Na gaskata da Allah, kuma na gaskata da mafarkina.”
🌺 Darasi daga labarin:
Kada ki bari maganar mutane ta kashe miki buri.
Idan kina da mafarki, ki haɗa shi da tawakkali ga Allah.
Wahala ba tana nufin ƙarshen nasara ba.

25/10/2025

Dakin ta ta nufa ta kara gyara kanta ta fesa turare tana baza kamshi ta chanja wasu kayan karamar doguwar riga iyakarta cinya yellow ce ai kuwa ta hau da jikinta sosai musamman da yake farace sosai kuma tana da dan kauri ma'ana kiba daidai wadaida cinyoyinta sun haska sosai cikin kayan ta kara fesa wani turaren kana ta bude drawer mirror ta sauki chuwing-gum ta jefa a baki ta rufe drawer ta fita daga dakinta ta ja kofar ta nufi dakin Abdul.

A hankali ta murda handle din kofar ta shiga a kishingide ta sameshi saman gado yana danna waya yana murmushi da alamar chatting yake yi.

Jin and turo kofar da kuma kamshinta daya kai masa ziyara duka kofofin hancinsa ya sanar masa isowarta don haka yayi saurin kashe wayar ya jefata can baya ya mike zaune da kyau yana binta da kallo.

Ta karaso ta zauna dan nesa dashi kadan daga bakin gadon tace, barka da dare.

Ya d**o ya zuba mata idanu yana yaba zallar kyau da Allah ya h**e mata ga wannan shiga da tayi ta dauki hankalinshi sosai ta tafi dashi.

Kusan mintuna goma a haka babu wanda ya sake cewa kowa komai kuma bai amsa barkan data mai ba hakan yasa ta dan muskuta ta kwanta taja bargo ta rufe rabin jikinta ta lumshe ido.

Ganin wankin hula zai iya kaishi dare gashi ta tasar mai da kwadayinsa yasa ya kashe wutar dakin ya matsa dab da ita ya kwanta ya fara lalubenta tana jinsa amma batace komai ba kuma bata motsa ba, ganin haka yasa ya dakata da abunda yakeyi ya sauke numfashi ya kira sunanta da murya mai nuna tsant

25/10/2025

Ta rungume danta tana zubarda hawaye masu radadi wani tukuki takeji a zuciyarta cike da tarin karaya da nadama ta mike taja hannun shi s**a shige daki s**a bar Abdul tsaye a gurin yana sababi.

Zaunar dashi kan gadonshi tayi tana hadiyar abubuwa masu tarin yawa da s**a taru a makogwaronta suna bukatar fitowa amma ta tauyesu ta hanyar mayar dasu cikin cikinta tana sauke numfashi.

Shureim yace momma meyasa baba baya sona kullum saiya dakeni kuma ya zageni? Ni momma kawai ki daukeni mu kuma gidan kaka su suna sona tunda shi baya sona kuma kema sai yayi ta zaginki meyasa bazaki rama ba kina tsoron ya dakeki ne?

Ta rungume shi tana kuka tace, kayi hakuri yarona duk ni na jawo mana! Tabbas ni na jawo mana, da ban aikata abunda na aikata ba da ban biyewa son zuciya ba, da ban biyewa rudin shaidan ba da duk haka bata kasance gare mu ba, kaichona ya Allah ka agajeni Allah na tuba ka yafe mun.

Abdul tunda Ameena ta shiga ciki ta barshi a falo ya karaci sababinshi yayi waje.

Da daddare ta zubo musu abinci itada shureim s**a ci s**a koshi duk da ranta babu dadi amma hakanan ta daure ta dura abincin ta koshi ta maida plates din kitchen ta Adana su ta dawo tayi wanka ta ma shureim wanka duk a cikin dakin shureim din take haka don bata yadda shureim din ya nufi dakinta tun lokacin da mai gidan ya nuna bacinran sa akan hakan sai take komai a dakin shureim din sai bayan ta gama wa mai gidan hidimominsa take dawowa dakin shureim idan yayi bacci ta koma nasu dakin yanzuma hakan ta kasance da taga yayi bacci ta rage gudun AC ta rufa mai bargo ta tofa masa addu'o'i kana taja masa kofar ta fita.

25/10/2025

🤦‍♀️FENTIN ZIN🅰️🙅‍♀️🤦‍♀️

EESHERT ADAMU

PAGE 1.



BISMILLAHIRRAHMANIRRAHEEM.

Zaune take cikin falonta mai alfarma daidai gwargwadon mai arziki a karnin mu cikin damuwa ta dafe kanta da duka hannayen ta guda biyu idanunta na tsiyayar da hawaye gefe daya ga danta mai shekara biyar yana wasa a tsakar falon da kekensa wadda ta siya masa. Mijinta na tsaye a kanta cikin fusata da hargowa yana cewa.

Nace zaki fada mun wanda naga ya fita daga gidana yanzu ko saina saba miki wato kin maidani shashasha bansan me nikeyi ba zaki kawo mun katon saurayi cikin gidana? Gidan aurena na sunnah? Bazan lamunta ba! Sam bazan yadda da wannan iskancin ba har wani zaki raina mun wayo wai yayanki ne eh naji yayankine amma ai muharraminkine shaidan na iya shiga tsakaninku ku aikata ba daidai ba nawa akayi kuma?

Ta d**o jajayen idanunta ta kalle shi tana sheshahekar kuka tace, yanzu zargina kake kenan? Kana zargina da aikata fasadi a cikin gidan aurena? Allah ya tsare ni da aikata wannan zunubin da bashida hukunci saina kisa, bance dole saika yarda dani ba amma tsakani na da Allah wannan yayanane ya jima ne baya gari sai jiya ya dawo shinefa yace bari yazo mu gaisa kenan yin hakan ya zama laifi? Danasan hakan zata faru da tun farko ban bari an gwada mai hanyar gidana ba da nasan hanyar da zan kaucewa zuwansa tun kafin yazo.

Shureim dake wasanshi ya ajiye kekenshi ya taho gurin Abdul ya rike kafarsa ya duka kasa yace cikin sanyin murya, baba ka daina yiwa mommata fada bata aikata komaiba kayi hakuri.

Abdul ya kara zuwa wuya ya tunkure shureim har saida ya fadi kasa ya nuna shi da yatsa kai kace sa'anshi ne yace, kai idanma kasan irin bakin cikin da nikeji idan na ganka bazakayi kuskeren dinga rabata ba domin kamar yadda na tsani mutuwata haka na tsani ganinka cikin gidana babu dai yadda na iyane kawai tunda na riga na jajibowa kaina.

Shureim ya tashi ya nufi gurin mahaifiya shi yana matsar kwalla.

Ta rungume danta tana zubarda hawaye masu radadi wani tukuki takeji a zuciyarta cik

19/10/2025

Mijina Yana Kwanciya A Bandaki Kowane Dare — Kashi na 3

Da na juya na ganshi tsaye a ƙofar… zuciyata ta tsaya cak.

Idanunsa sun yi ja, fuskarsa babu tausayi — yana kallona kamar wanda yake da wata muguwar niyya.
Ya ji komai.

“Caro,” ya ce cikin natsuwa, “me kika faɗa wa ’yar uwarki?”

Muryata na rawa.
“Ba–ba komai, Felix. Tana tambaya ne kawai—”

“Ƙarya!” ya yi ihu, yana bugun bango da hannu.
’Yar uwata ta ja da baya cikin tsoro.

“Wa ya gaya miki zaki fara faɗa wa mutane sirrina?”
Na kasa magana, hawaye na zubo.

Sai ya juya ya kalli ’yar uwata, ya ce da murya mai tsanani,
“Ke! Fita daga gidana. Yanzu nan.”

“Don Allah, ranka ya daɗe, ni ba—” kafin ta gama, ya sake ihu.
“Na ce fita!”

Ta ɗauki jaka tana kuka ta gudu waje.

Sai ya juya gare ni… a hankali.
Kuma abin da ya faɗa sai jikina ya mutu da tsoro.

“Caro, na gargade ki. Idan kika ƙara karya dokata, wani kusa dake zai biya.”

Na durƙusa ina kuka, ina roƙonsa.
“Don Allah, Felix, kada ka cutar da kowa. Zan yi shiru. Na rantse!”

Ya kalle ni na ɗan lokaci, sannan ya yi murmushi mai ban tsoro.
“Madalla. Ki tabbata baki karya wannan alƙawarin ba.”

Ranar nan bai shiga bandaki ba.
Ya zauna a falo har zuwa safe, yana kallo cikin sarari kamar wanda ba ya cikin hankalinsa.

Ni kuma, ko kwana ban yi ba.
Tunanina guda ɗaya — me yake ɓoye?
Me yasa tsoro da barazana a cikin aure?

Da safe na samu saƙo daga ’yar uwata.
Ta ce ta yi mafarki na — wai an kulle ni a ɗaki ina kuka ina neman taimako.

Ta roƙe ni da kada in zauna a wannan gida.
Na soma tunani — ya kamata in gudu, ko in gano gaskiya?

Saboda wani abu a zuciyata yana cewa…
bandakin nan… yana ɓoye sirri da ya fi tunanina.

Zan ci gaba

18/10/2025

Mata makwabtan ta na unguwa s**an zo don su duba ta, suna mata addu’a:
“Allah ya warkar da ke,”
“Allah ya baki lafiya”…

Yaran suna jin sunan Allah akai-akai daga bakunan masu zuwa dubiya suna mata addu’a.
S**a fara tambaya cike da mamaki:
"Wane ne Allah?"
"A ina yake?"
"Shin idan mun kira shi, zai ji mu?"

S**a tambayi kakarsu, wadda ita kaɗai ta rage a cikin gidan.
Kakarsu ta ce:
"I, Allah yana jin duk wanda ya roƙe shi. Matukar yayi imani dashi."

Yaran s**a sa wannan a zuciyarsu.

Da daddare, suna zaman jiran mahaifinsu wanda har yanzu bai dawo ba, suna kwance suna kallon wata a sama.
Karamin cikinsu ya ce:
"Yaya, kana ganin Allah yana cikin wannan watan?
Ko kuma yana nan a cikin wani wajen a sama?"
Haka s**ayi ta tattaunawa, suna yiwa junansu tambayoyi har sai da s**a yi barci.

Da safe, bayan sun dawo daga makaranta, sai s**a je wajen wani mai shago don su sayi takardar aika wasiƙa.
Mai shagon ya ce:
"Kai me yasa kuke da gaggawa?
Kuna son ku aika wa mahaifinku wasiƙar ne?
Kuyi hakuri nan ba da jimawa ba zai dawo"
Yaran s**a ce:
"A’a, ba mahaifinmu zamu turawa ba!"

S**a koma gida, s**a ɓuya a cikin garken tumaki, s**a fara rubuta wasiƙar kamar haka:

بِسْمِ اللّٰهِ الرَّحْمٰنِ الرَّحِيمِ

Ya Allah, ka zo ka ceci mahaifiyarmu, tana fama da rashin lafiya mai tsanani.
Baba ya tafi birni kuma har yanzu bai dawo ba, kuma cutar na kara ƙaruwa.
Kakarmu ta ce kai mai Rahama ne, mai tausayi, kuma kana amsa roƙon masu roƙo a gare ka.
Kaka tace mana kana kaunar kananan yara, kuma kana amsa addu’ar su da gaggawa saboda basa laifi, basu taba aikata maka aikin saɓo ba.
Kada ka ba mu kunya, muna roko a gare ka.
Ka taimaki mahaifiyarmu, idan ka yi haka, za mu ƙaunace ka, mu gode maka.
Idan kuma ba ka zo ba, za mu kasance cikin baƙin ciki har abada.

Za mu zauna a bakin t**i mu jira motar da za ka aiko da ita.

Wasiƙa daga: ....... zuwa ga Allah.

S**a saka a cikin envelope, ba tare da sun rubuta adireshin wanda zasu aikawa ba.
S**a kai zuwa akwatin aika wasiƙa dake a ƙarshen

18/10/2025

MIJINA NA YIN BARCI A BANDÀKI KOWACE DARE – Kashi na 1

Kwana biyu kacal bayan bikinmu ne abin ya fara.
Ranar farko cike take da dariya da soyayya. Mun kwana muna rungume juna har bacci ya ɗauke mu. Da safe muka tashi cike da farin ciki… kamar aljanna ta sauka cikin ɗaki.

Amma ranar biyu… wani abu ya canza.
Na jira shi ya shigo gadonmu har bacci ya ɗauke ni. Ban sani ba, cewa daren nan… bai kwanta ba. Ya shafe duka daren a bandàki!

Da safe na tashi shi kadai ke cikin ɗakin wanka, riga a jiki, kamar wanda zai fita kasuwa.

Na yi murmushi:
“Ka tashi da wuri yau.”

Ya amsa da murmushi:
“Eh… akwai meeting da safe.”

Na ce, “Ni ma ban ma san lokacin da ka kwanta ba.”
Sai ya ce, “Na dade ina kiran waya, bana son na tashe ki.”

Na yi dariya, “Ai sai ka shigo ka kwanta, bana damuwa.”
Sai kawai ya sumbaci goshina ya fita.

Amma daga wannan rana… ba ya kwana a gado!

Ko da na tashi 2 na dare, 3 na dare… sai in shafi gadon, babu shi.
Da farko na ɗauka watakila yana fita falo… amma kullum, hasken bandàki ne ke kunne.

Na taba ƙofar bandàki da hankali, na ce,
“Yaya, lafiya?”
Sai ya amsa da sauri,
“Eh lafiya, ki koma ki kwanta!”

Amma bai fito ba.
Kullum haka.

Sai wata rana, ya manta bai kulle ƙofar ba.
Na tashi da daddare… na matsa ƙofar da hankali…
Na tura ta a hankali…

Abin da na gani a ciki... ya girgiza ni.

✋🏻 Zamu ci gaba a Kashi na2

18/10/2025

Kashi na 2

Ban iya gaskata abin da idona s**a gani ba.
Na tsaya cak, numfashina ya tsaya.
“Subhanallah!” na furta cikin rawar murya.
“Haba Felix! Me hakan ke nufi?”

Kafin in ƙarasa magana, ya daga murya da ƙarfi:
“Ki tsaya! Kar ki tambaye ni komai. Bai kamata ki shigo ba!”

Idonsa jajaye kamar wanda bai taɓa barci ba.
Murya kamar guguwa.
Tunda muka yi aure, ban taɓa ganin wannan fuskarsa ba.

Na ji jikina na rawa.
Na kasa magana.
Shin wannan ne mutumin da na aura?

Ya matso kusa, ya kalle ni da idanu masu cike da barazana, ya ce:
“Abin da kika gani… kar ki taɓa faɗa wa kowa.
Idan kika yi, ke da kanki kika nemi matsala.
Ki rike wannan sirri har abada.

Game da aurenmu kuma…”
Ya ɗan yi shiru.
“Babu dawowa baya. Ba za ki iya gudu ba.
Ranar da kika gwada tserewa… ke ce kika ɓace.”

Ya rufe ƙofar, ya cigaba da zama a ciki.

Na koma kan gado da hawaye.
Ban san lokacin da zuciyata ta fara fashewa da kuka ba.
Na tuna da lokacin da muka yi soyayya – yadda yake guje da tambayoyi.
Yana cewa: “Zaki fahimce ni daga baya. Abin da ya fi muhimmanci shine soyayyata gare ki.”

To, wannan ce “fahimtar” da yake nufi?

Ranar, ban runtsa ba.
Na zauna ina tunani — in yi shiru ko in faɗa?
A ƙarshe na ɗauki shawara:
Zan yi shiru na ɗan lokaci.
Amma da zarar na samu dama, zan gudu.

Da safe, ya fito kamar ba komai ya faru ba.
Ya yi shiri, ya fita, bai ma kalle ni sosai ba.

Na fara tunani:
Ina yake zuwa kullum da sassafe haka?
Ban taɓa tambayarsa sosai ba.
A lokacin, burina kawai a yi aure ne — ban yi zurfin tunani ba.

Da rana ina cikin girki, sai ya shigo ya tsaya a bakin ƙofa.
Ya ce:
“Ki tuna abin da na faɗa jiya.
Idan kika ɓoye sirrin, zaki zauna lafiya.
Amma idan kika faɗa wa kowa…
Wani abu mai muni zai faru — da ke, da shi.”

Ya juya ya fita.
Na tsaya ina kallon ƙofa, cokali ya faɗi daga hannuna.
Na ce a raina, “Wane irin aure ne wannan?”

Da daddare, ban sake kwana a ɗaki ba.
Na koma falo — ina zaman shiru, da kuka.

Wata rana da rana, sai ga ƙwanƙwaso a ƙofa.
Na tashi na buɗe…

Address

Kaduna Road
Suleja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labarai masu Dadi da ban al'jabi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category