12/05/2026
A yau, Sakataren Karamar Hukumar Zaria, Hon. Shuaibu Abdullahi (Mai Canter), daga cikin manufofinsa na bada dama da kuma hada kai da kungiyoyi don cigaban alโumma, yayin da yake wakiltar Shugaban Karamar Hukumar Zariya, Engr. Jamil Ahmad Muhammad (Jaga), ya karbi bakuncin tawaga da mambobin kungiyar โ๐๐๐๐๐๐ ๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐ ๐๐๐๐๐๐๐๐๐ ๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐ ๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐ ๐๐๐๐๐โ da kuma โ๐๐๐๐๐ ๐๐๐๐๐ ๐๐๐๐๐ ๐๐๐๐๐๐๐๐๐ ๐
๐๐๐๐โ a ofishinsa.
Sunkai ziyarar ne domin kara karfafa hadin gwiwa tsakanin gwamnatin karamar hukumar Zaria da kungiyoyin wajen bunkasa hadin kai, karfafa mata, da kuma ci gaban alโumma a fadin Zaria.
Sakataren ya yaba wa kungiyoyin bisa jajircewarsu da gudunmawar da suke bayarwa wajen cigaban alโumma, tare da tabbatar musu da ci gaba da samun goyon bayan karamar hukumar kan duk wasu shirye-shiryen da za su amfani jamaโa.
Haka kuma, ya sake jaddada kudurin wannan gwamnati karkashin jagorancin Engr. Jamil Ahmad Muhammad (Jaga) na tabbatar da shugabanci mai bai wa kowa dama, hada kan alโumma, da kuma dorewar ci gaba a matakin karkara.
๐ฆ๐ถ๐ด๐ป๐ฒ๐ฑ:
๐๐ฎ๐๐๐ฎ๐ป ๐ญ๐ฎ๐ธ๐ฎ๐ฟ๐ถ๐๐๐ฎ
๐ฃ.๐ ๐ ๐ฒ๐ฑ๐ถ๐ฎ ๐ฎ๐ป๐ฑ ๐๐ผ๐บ๐บ๐๐ป๐ถ๐ฐ๐ฎ๐๐ถ๐ผ๐ป
๐ข๐ณ๐ณ๐ถ๐ฐ๐ฒ ๐ผ๐ณ ๐๐ต๐ฒ ๐๐ผ๐๐ป๐ฐ๐ถ๐น ๐ฆ๐ฒ๐ฐ๐ฟ๐ฒ๐๐ฎ๐ฟ๐
๐ญ๐ฎ๐ฟ๐ถ๐ฎ ๐๐ผ๐ฐ๐ฎ๐น ๐๐ผ๐๐ฒ๐ฟ๐ป๐บ๐ฒ๐ป๐
11๐๐ต ๐๐ฝ๐ฟ๐ถ๐น, ๐ฎ๐ฌ๐ฎ๐ฒ