31/07/2026
MASARAUTAR LAME TA MIƘA TAKARDAR TABBATAR DA SARAUTA GA KILISHIN LAME NA FARKO
A ranar Alhamis, 30 ga Yuli, 2026, Mai Girma Kwamishinar Ilimin Manyan Makarantu ta Jihar Bauchi, Hon. Dr. Hadiza Abdulkadir Kango, ta karɓi Takardar Tabbatar da Sarautarta a matsayin Kilishin Lame na Farko, bisa umarnin Mai Martaba Sarkin Lame, Alhaji Aliyu Yakubu Lame.
Takardar ta iso ne ta hannun tawagar Masarautar Lame ƙarƙashin jagorancin Alhaji Yakubu Ibrahim Lame, Sakataren Masarautar, waɗanda s**a kai ziyarar girmamawa zuwa gidan iyayen Kwamishinar da ke Unguwar Bakin Kura, Jihar Bauchi. A nan ne Hon. Dr. Hadiza Abdulkadir Kango ta tarbe su tare da 'yan uwa, abokan arziki da masu fatan alheri.
Da yake jawabi, shugaban tawagar ya bayyana cewa isar da takardar tabbatar da sarautar umarni ne kai tsaye daga Mai Martaba Sarkin Lame, domin tabbatar da Hon. Dr. Hadiza Abdulkadir Kango a matsayin Kilishin Lame na Farko. Ya ce an ba ta wannan matsayi ne saboda kyawawan ɗabi'unta, jajircewarta wajen yi wa al'umma hidima, da kuma irin gudummawar da take bayarwa wajen bunƙasa ilimi, ci gaban al'umma da kuma martabar al'adun gargajiya.
A nata jawabin, Hon. Dr. Hadiza Abdulkadir Kango ta nuna matuƙar godiya ga Mai Martaba Sarkin Lame da Majalisar Masarautar bisa wannan babbar karramawa. Ta bayyana cewa za ta ci gaba da gudanar da wannan amanar cikin gaskiya, riƙon amana da sadaukarwa domin ci gaban Masarautar Lame da al'umma baki ɗaya.
A ƙarshen taron, ɗaya daga cikin yayyenta, Alhaji Abubakar Abdulkadir Mijinyawa Kango, ya jagoranci addu'ar neman Allah Ya ba ta ikon sauke wannan nauyi yadda ya kamata, Ya ƙara wa Mai Martaba Sarkin Lame lafiya, nisan kwana da ɗaukaka, tare da albarkace Masarautar Lame da al'ummarta.
E-sign:
Aliyu Alhaji Habibu
Social Media Director
Hon. Dr. Hadiza Abdulkadir Kango
Commissioner for Higher Education, Bauchi State