Majalisu Dillabul Ilmi Bauchi

  • Home
  • Majalisu Dillabul Ilmi Bauchi

Majalisu Dillabul Ilmi Bauchi Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Majalisu Dillabul Ilmi Bauchi, Grocers, Unguwan Jaki Bauchi, .

12/01/2022

MATA KUNA INA ?
innalillahi wa'inna Ilaihirraji'un, watarana Sayyidina Ali da matarsa faɗima sun shiga gurin Annabi ﷺ s**a same shi Yana ta kuka, kuka mai tsanani, sai Sayyidina Aliyu Yace me ya sa ka Kuka Ya Ma'aikin Allah ﷺ ? Sai Annabi Yace Ya Aliyu Daren da Akayi isra'i dani Naga MATAN wannan Al'ummar Anayi masu nau'i-nau'i na Azaba, nayi kuka matsananci da naga Azabar da Ake yi masu.
👇
Naga mace An rataye ta da gashinta ƙwaƙwalwarta tana Zaɓalɓaka, saboda ta kasance bata rufe (gashin) kanta daga mazaje, naga mace An rataye ta da harshenta ana zuba mata ruwan Zafi A maƙogoronta saboda tana cutar da mijinta, Naga wacce aka rataye nononta ta kasance tana ɓata shimfiɗar mijinta
ﻭﺃﻣﺎ ﺍﻟﺘﻲ ﺗﺸﺪ ﺭﺟﻼﻫﺎ ﺇﻟﻰ ﺛﺪﻳﻴﻬﺎ ﻭﻳﺪﺍﻫﺎ ﺇﻟﻰ ﻧﺎﺻﻴﺘﻬﺎ ﻭﻗﺪ ﺳﻠﻂ ﻋﻠﻴﻬﺎ ﺍﻟﺤﻴﺎﺕ ﻭﺍﻟﻌﻘﺎﺭﺏ ﻓﺈﻧﻬﺎ ﻛﺎﻧﺖ ﻻ ﺗﻨﻈﻒ ﺑﺪﻧﻬﺎ ﻣﻦ ﺍﻟﺠﻨﺎﺑﺔ ﻭﺍﻟﺤﻴﺾ ﻭﺗﺴﺘﻬﺰﺉ ﺑﺎﻟﺼﻼﺓ ﻭﺃﻣﺎ ﺍﻟﺘﻲ ﺭﺃﺳﻬﺎ ﺭﺃﺱ ﺧﻨﺰﻳﺮ ﻭﺑﺪﻧﻬﺎ ﺑﺪﻥ ﺣﻤﺎﺭ ﻓﺈﻧﻬﺎ ﻛﺎﻧﺖ ﻧﻤﺎﻣﺔ ﻛﺬﺍﺑﺔ ﻭﺃﻣﺎ ﺍﻟﺘﻲ ﻋﻠﻰ ﺻﻮﺭﺓ ﺍﻟﻜﻠﺐ ﻭﺍﻟﻨﺎﺭ ﺗﺪﺧﻞ ﻣﻦ ﻓﻴﻬﺎ ﻭﺗﺨﺮﺝ ﻣﻦ ﺩﺑﺮﻫﺎ ﻓﺈﻧﻬﺎ ﻛﺎﻧﺖ ﻣﻨﺎﻧﺔ ﺣﺴﺎﺩﺓ
Amma wacce aka ɗaure ƙafarta Zuwa nononta, da hannayenta Zuwa ƙoƙuwar kanta An sallaɗo mata macizai da kunamai (Suna azabtar da'ita) bata tsarkake jikinta daga janaba da haila, tana yiwa salla izgilanci, Amma wacce kanta Yake Kan Alade Jikinta kuma jikin Jaki ta ka sance Annamimiya, makaryaciya, Amma wacce take da surar kare, wuta ta shiga ta bakinta tafita ta duburarta, Ta kasance mai Yawan gori da hassada
👇
Alkaba'eera Babi na 47 shafi na 115-116
Mafita kawai itace Maganar Annabi ﷺ Da yace idan mace tayiwa mijjinta biyayya, tayi salla 5 ɗinta, Ta azumci Watanta, Tayi zakkar kuɗinta, ta baƙunci ɗakin ubangijinta, zata shiga Aljanna ta ko wacce ƙofa taso!
👇

12/01/2022

HUKUNCIN MUSULMAI MASU GABA DA JUNANSU :*

Assalumu alaikum, Allah ya karawa malan kaifin basira, Malan tambaya itace ? Menene matsayin mutumin dayake gaba da dan uwansa har tsawon shekaru amma dayan mutumin ya yi masa sallama har sau wajen biyar baya amsawa, amma idan yana cikin mutane dayan yayi musu sallama yana amsawa, amma idan sun hadu daga shi sai shi bawan da yake wa kowa sallama?

AMSA
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Wannan kiyayyar juna da sukeyi ko kaurace wa juna, haramun ne. Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) yace :

"Bai halatta ga musulmi ya kaurace ma dan uwansa sama da kwanaki uku ba. Suna haduwa sai wannan ya dauke kansa, wannan ma ya dauke kansa, Amma mafi alkhairi acikinsu shine wanda ya fara yiwa dan uwansa sallama".

Imamu Malik da Bukhari da Muslim da Abu Dawud da Nisa'iy ne s**a ruwaitoshi.

Acikin wata riwayar ta Muslim da Nisa'iy kuma, Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya Qara da cewa wanda ya kaurace wa Dan uwansa sama da kwanaki uku, idan ya mutu wuta zai shiga.. "..

Kuma acikin wani hadisin ma Manzon Allah (saww) yace "A kowacce ranar Alhamis Ana gafarta wa kowanne musulmin da ba ya yin shirka. Sai dai mutane biyun da suke Qiyayyar juna, za'a ce wa Mala'iku "Ku dakata ma wadannan har sai sun shirya da junansu".

Don haka kuyi musu nasihar cewa suji tsoron Allah su dena wannan gabar da sukeyi da juna, domin su samu gafarar Ubangijinsu.

Tunda har wani daga cikinsu yana yiwa dayan sallama, to yaci gaba da aikata haka. In sha Allahu da haka har zasu daidaita da juna.
WALLAHU A'ALAM.

Send a message to learn more

Address

Unguwan Jaki Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Majalisu Dillabul Ilmi Bauchi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Grocery Store?

Share