12/04/2026
MUTANE KALAR BIYAR 5 NA ROKE KU DON ALLAH KU CIRE SU A RAYUWARKU..
Akwai wasu mutane guda biyar wadanda ko jinin jikinka ne, matukar suna da wadannan halayen wallahi kaska ne wadanda suke tsotse maka farin ciki. Ga su nan:
1. Wanda Ka Yiwa 99 Ya Manta Saboda 1: Mutumin da zaka narkar da gumi da dukiyarka a kansa sau 99, amma ranar da ka gaza ko ka ce ba zaka iya ba sau 1, zai manta duk alherin da ka taba yi masa ya maida kai mugu.
2. Munafuki Mai Taya Ka Kuka: Wanda idan ka samu nasara ba zai taba yi maka murna ba, amma idan wata faduwa ko asara ta same ka, shine na farko da zai zo ya nuna yana tausaya maka alhalin a ransa murna yake yi yaga baka da komai.
3. Mai Ci Da Kai Yana Ɓata Ka: Wanda yake cin abincinka, yake amfana da aljihunka da girmanka a gabanka, amma idan ya fita majalisa ko cikin mutane shine zai fara zubar maka da mutunci ya tona asirinka.
4. Wanda Bai Tausayin Gumin Ka: Mutumin da ko yaga kana fuskantar matsanancin hali ko kana bin bashi, bai damu ba. Burinsa kawai ka biya masa bukatarsa, tunda a lissafinsa kai baka da matsala.
5. Mai Son Ka A Lokacin Da Kake Da Shi: Wanda girmanka da kwarjininka a wajensa ya danganta da kudin dake aljihunka. Ranar da asirinka ya tonu, wallahi ko kallon arziki ba zai yi maka ba, zai daina sanin kana yi.
Dan uwa, ba wai tsanarsu zaka yi ba, kawai ka yanke mu'amala da su domin ka tsira da lafiyar kwakwalwarka.
Allah ya bamu ikon tsare mutuncinmu.
UMAR ALIYU DAHIRU✍️