24/05/2025
Abubuwa goma da za su iya faruwa idan Tinubu ya zarce a wa’adi na biyu
DAGA-Ky Tebo
1. Nigeria ce za ta zama cikin kasashe masu fama da bakin talauci saboda fifita siyasa da ake yi da mayar da hankali kan cigaban yan siyasa maimakon cigaban kasa da yan kasa.
2. Za a rasa masu fadawa gwamnati gaskiya saboda ba masu kishin kasar sai na aljihu, kuma za a tilastawa mutane bin dokokin k**a karya da aka samar ta hanyar amfani da yan majalisu marasa kishin kasa da sune mafi yawa a majalisun Nigeria.
3. Ba wanda ya isa ya kara yin tasiri da sunan hamayya a demokradiyya irinta Nigeria, Tinubu zai kafa yan uwansa da wadanda yake so su mulki Nigeria na dindindin k**ar yadda ya yi a Lagos.
4. Arewa za ta koma kufayi na mabarata saboda jahilcin da ke cikinta, dole yan cikinta su mika wuya ta hanyar komawa karkashin daular Tinubu k**ar yadda s**a tare yanzu saboda kwadayi, masu kudin cikinsu da taurin kai za a kakaba musu takunkumi kan dukiyoyinsu idan basu bi gwamnati ba.
5. Ta’addanci zai zama ruwan dare, ta yadda talaka zai yi ta ransa ya manta da maganar neman yanci ko wani jin dadi, malamai da sauran masu fada aji a Arewa za a kakk**a su idan s**a soki gwamnati.
6. Za a raunana doka, za kuma a wulakanta masu ruwa da tsaki kan sha’anin doka k**ar lauyoyi da alkalai da aka kashe kasar da su a baya, kuma za a cigaba da yin barazana ga rayuwar yan kishin kasar ta hanyar kashewa, batarwa ko kullewa.
7. Mata za su shiga masifar da basu taba shiga ba, za su fito neman abinci kan t**i irin yadda ba a taba yi ba a tarihin Nigeria, kuma cututtukan zamani za su yawaita tsakanin al’umma.
8. Yan mulkin mallaka za su hada karfi da karfe su kwashi arzikin Nigeria ta hanyar kashe mu raba da masu ruwa da tsaki kan harkar mulki tare da juya akalar cigaban kasar kan tsarinsu na Turawa.
9. Matasa za su nemi inda za su gudu, amma ba za su samu kudin da za su iya jigilar fita ba, karshe kowa zai rasa aikinyi, za a rufe kasuwanni ta hanyar rasa jari da hauhawar farashi na tashin h