28/08/2025
TAUSAYIN TSADAR RAYUWAR GA MA'AIKATA GWAMNAN JIHAR IMO YA KARA ALBASHI ZUWA 104,000.
______
Gwamnan Imo Ya Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi Zuwa N104,000
Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma, ya amince da ƙarin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan gwamnati a jihar daga N76,000 zuwa N104,000.
Uzodimma ya sanar da wannan sauyi ne a lokacin wata ganawa da shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago da aka gudanar a daren Talata a fadar gwamnatin jihar da ke Owerri.
A cewar rahoton jaridar The Punch da kuma Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa (NAN), ƙarin ya shafi ma’aikata daban-daban, inda:
Mafi ƙarancin albashin likitoci ya tashi daga N215,000 zuwa N503,000
Na malamai a manyan makarantu daga N119,000 zuwa N222,000
Da kuma sauran ma’aikata bisa tsari.
Gwamnan ya bayyana cewa ma’aikatan jihar sun fuskanci manyan ƙalubale tun bayan zuwansa mulki, ciki har da matsalar tsaro, annobar COVID-19, matsin tattalin arziki sakamakon manufofin gyara, da kuma rikici kan mafi ƙarancin albashi da cire tallafin man fetur.
Ya ce: “Idan aka biya ma’aikata albashi mai kyau, za a samu ƙwarewar aiki, iyalai su more rayuwa mai sauƙi, kuma tattalin arzikin cikin gida ya bunƙasa.”
Uzodimma ya kuma bayyana cewa kudaden shiga na jihar (IGR) sun ƙaru daga N400m zuwa sama da N3bn a kowane wata, lamarin da ya bai wa gwamnati damar ɗaukar wannan sabon mataki.
ME ZAKU CE KAN HAKAN.....?