Salihu yareema

Salihu yareema Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Salihu yareema, Grocers, Daura.

An Ruwaito, MANZON ALLAH(S.A.W) Lokacin Da Ya Je Al'arshi a Daren Mi'iraji Yayi Nufin Ya Cire Takalmansa, Sai Aka Ƙira S...
09/11/2025

An Ruwaito, MANZON ALLAH(S.A.W) Lokacin Da Ya Je Al'arshi a Daren Mi'iraji Yayi Nufin Ya Cire Takalmansa,

Sai Aka Ƙira Shi: "Me Yasa Zaka Cire Takalmanka???"

Sai Ya Ce:

"Ina Jin Tsoron Kar a Faɗa Min Abin Da Aka Faɗawa Ɗan-uwana ANNABI MUSA(A.S);

اخلع نعليك

Sai Aka Ƙira Shi(Da Wata Murya):

"Ya RASULULLAHI! Idan MUSA, Yana Da Nufi, Kai Kuma Kai Ne Abin Nufin,

Idan MUSA Ya Kasance Yana So, Kai Kuma Kai Ne Abin Son,

Idan MUSA Yana Nema, Kai Kuma Kai Ne Abin Neman,

Idan MUSA Ya Kasance Makusanci, Kai Kuma Masoyi Ne."

Tambaye Ni Abin Da Kake So, Ni Mai Ji Ne, Kuma Mai Amsawa;

Sai MA'AIKI(S.A.W) Ya Ce: "Ya UBANGIJINA! Ba Ina Roƙonka AMINATU Wacce Ta Haife Ni Ba Ne, Ko HALIMA Wacce Ta Shayar Da Ni, Ko FAƊIMATU 'Ya Ta, A'a, Ina Roƙonka Ne Al'umata.!"

Sai ALLAH(S.W.T) Ya Ce:

"Ya NABIYYUR-RAHMATI! Tausayinka Ga Al'ummarka, Al'ummarka Halitta Ce Mai Rauni,

Ni Kuma UBANGIJI Ne Mai Tausasawa, Kai Kuma ANNABI Ne Mai Girma.

Mai Rauni Ba Zai Tozarta Ba a Tsakanin Mai Tausasawa Da Mai Girma.

Na Rantse Da Girmana Da Ɗaukakata Ranar Ƙiyama Zan Raba Tsagi Biyu Tsakanina Da Kai, Kana Cewa; Al'ummata Al'ummata, Ni Kuma Ina Cewa; Rahmata Rahmata!".

صلوعلى بدرالمنيروالسراج الوهاج

ALLAH Ya 'Kara Rura Wutar SOYAYYAR ANNABI MUHAMMADU(S.A.W) a Cikin Zukatanmu, Ya Sa Mu Cikin CetonSA(S.A.W), Ameeeen❣️🙏😭

DUK MAI ƘAUNAR ANNABI ﷺ YAYI SHEARING

24/06/2025

💞ABUBUWA GUDA HUDU SUNA JANYO BUDEWAR KOFOFIN ARZIKI :

1. TSAIWAR DARE (Qiyamul Layl) : Manzon Allah (saww) ya nuna mana Muhimmancin Tsaiwar dare ya ce tana janyo ma mutum samun girman matsayi awajen Allah. Kuma duk wanda ya hana idonsa barci cikin dare don neman yardar Allah, Shi kuma Allah zai faranta zuciyarsa da rana.

2. ISTIGHFARI : Allah ya bamu labarin abinda Annabi Nuhu (as) yake gaya ma Mutanensa. Yace :

"NACE (MUSU) KU NEMI GAFARAR UBANGIJINKU DOMIN SHI MAI GAFARA NE. ZAI SAUKAR MUKU DA RUWA DAGA SAMA, KUMA QAREKU DA DUKIYA DA 'YA'YA, KUMA ZAI SANYA MUKU GONAKI KUMA ZAI SANYA MUKU QORAMU (Wato albarkacin Istighfarin nan Allah zai gafarta zunubanku, kuma zai yalwata arzikinku ta fuskar 'ya'ya da dukiya da gonakai da Qoramu da kuma ruwan sama mai albarka.

Manzon Allah (saww) yace duk wanda ya yawaita Istighfari Allah zai yaye masa damuwarsa kuma zai azurtashi ta inda ba ya tsammani.

3. SADAQAH : Sadaqah itama babbar hanyar budewar kofofin Arziki ne. Domin kuwa Allah yana cewa :

"IDAN KUKA BAMA ALLAH RANCHE, RANCHE MAI KYAWU, TO ZAI NINNINKASHI GAREKU KUMA ZAO GAFARTA MUKU.. ".

Kuma yace "DUK ABINDA KUKA CIYAR NA WANI ABU, TO (ALLAH) SHI ZAI NINKASHI KUMA SHINE MAFI ALKHAIRIN MASU AZURTAWA".

4. ZIKIRIN ALLAH : Zikirin Allah, Karatun Alqur'ani da Salatin Manzon Rahama (saww) su ke Sanya zuciya ta samu nutsuwa azahiri da badini. Kuma ta hanyar zikirin Allah mutum yana samun yayewar Talauci da Qunci. Kuma yana samun kusanci da Allah da jibintar lamarinsa aduniya da lahira.

Allah yasa mu dace da samun wadannan falaloli. Allah ya yaye mana Quncin rayuwa, ya Qara rufa asiranmu aduniya da lahira Ameeen.

A ZAMANIN SAYYADINA UMAR.A zamanin mulkin Khalifa Umar ibn al-Khattab (RA), yana da dabi’ar fita da dare yana yawo a cik...
09/06/2025

A ZAMANIN SAYYADINA UMAR.

A zamanin mulkin Khalifa Umar ibn al-Khattab (RA), yana da dabi’ar fita da dare yana yawo a cikin titunan Madina don duba halin da al’ummarsa ke ciki. A wata rana da daddare, yayin da yake yawo, ya tsaya kusa da wani ƙaramin gida, inda ya ji wata hira tsakanin wata uwa da 'yarta.

Uwar tana gaya wa 'yarta ta haɗa ruwa da madarar da za su kai kasuwa domin ya ƙaru, su sami riba mai yawa. Amma budurwar ta ƙi yarda da hakan, tana cewa:

"Uwa ta, Amirul Muminin (Umar) ya hana mu haɗa ruwa da madara."

Sai uwar ta ce: “To ai Umar baya nan, bai gan mu.”

Amma budurwar ta amsa da ƙarfi da cewa:

"Ko da Umar bai gan mu ba, Ubangijin Umar yana ganinmu."

Khalifa Umar (RA), wanda ke sauraren hirar daga waje, ya yi matuƙar jin daɗi da girmama gaskiyar yarinyar da kuma tsoron Allah da ta nuna. Washegari, ya tura wani don binciko wacece budurwar. Bayan ya tabbatar cewa ta isa aure, sai Umar ya shirya aurenta da ɗansa, Asim.

Daga zuriyar aurensu ne aka haifi wani fitaccen shugaba mai adalci: Umar ibn Abdul Aziz, wanda ya zama daya daga cikin shuwagabannin musulunci mafiya gaskiya da adalci a tarihin musulunci.

Idan Ka Tashi Aure Abokina....Ka Auri Matar Aure, Karka Kuskura Ka Auri Matar Gida.Kayi Aure, KarKa Bari A Aureka.Ka Aur...
27/05/2025

Idan Ka Tashi Aure Abokina....

Ka Auri Matar Aure, Karka Kuskura Ka Auri Matar Gida.
Kayi Aure, KarKa Bari A Aureka.
Ka Auri Wadda Take Sonka, Ba Wadda Kake So Ba.

Ka Auri Mace Ba Ƴar Gwagwarmaya Ba.
Ka Auri Mai Son Addini, Ba Mai Ilimin Addini Ba.
Karka Damu Da Auren Ƴar Alhaji Wane, Domin A Mafiya Yawan Lokuta Auren Ƴar Malam Wane Yafi Alheri A Gareka.

Ka Auri Nagarta, Kaso Nagarta, Ka Nemi Nagarta, Tabbas Aurenka Zai Kasance Mai Nagarta!

26/05/2025

Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa
WAJE BIYAR (5) DA DAN ADAM KE AMFANA DA
AYATUL KURSIYYU

1. Karanta kafa daya (1) kafin fita daga gida, Allah Zai aiko Mala'iku dubu saba'in (70,000) su tsare ka/ki har sai ka/ki koma gida.

2. Karanta kafa daya (1) kafin shiga gida, talauci bazai shigan maka/ki gida ba

3. Karanta kafa daya (1) bayan alwalla, darajar ka/ki zata daga sau saba'in (70) a wajen Allah

4. Karanta kafa daya (1) lokacin kwanciya, Allah Zai aiko Mala'ka daya (1) ya tsare ka/ki har lokacin daka tashi

5. Karanta kafa daya (1) bayan kowace Sallar farillah, mutuwa kawai zata hana ka/ki shiga Aljannah.

Ma'ana da zaka/ki mutu a wannan lokacin Aljannah zaka/ki kai tsaye insha Allahu Allah Ya bamu dacewa, amin summa amin.

YAWAN AMBATON ALLAH YAYIN KWANCIYAR BACCI.

Yana kara lafiyar bacci cikin nitsuwa,
Bacci cikin nitsiwa yana kara kaifin hankali,
Kaifin hankali kuma yana sanya kyayyawan tunani,
Kyayyawan tunani kuma yakan sanya mutum yaji tsoron Allah,
Tsoron Allah kuma yakan sa mutum ya kyautata ayyukan sa,
Kyawawan ayyuka kuma suna sa mutum ya dace da Rahamar Allah.
Saida Rahamar Allah ake shiga Aljannatul firdaus.
Allah ya sa mu dace.
Duk wanda yayi forwarding Allah ka biya mishi bukatun shi na alkhairi. Amin
Gass Ne Wlh ✍️

SIRRIN SAMUN AMFANIN GONA MAI, ALBARKA DA IZININ ALLAH. Assalamu Alaikum. Duba da yanayin, damuna ta kusa faduwa, mu kag...
23/05/2025

SIRRIN SAMUN AMFANIN GONA MAI, ALBARKA DA IZININ ALLAH.

Assalamu Alaikum.

Duba da yanayin, damuna ta kusa faduwa, mu kaga dacewar ya kamata, mu kawo maku wannan babban sirrin na samun amfanin gona mai, albarka.

Sirrin ba boyayye bane, domin mun taba, sakinsa a can baya Kuma alhamdulillah 🙏 mutane da dama, sun yi shi ALLAH ya basu amfanin gona mai albarka Wanda da dama, ma sun turo Mana, hotunan gonakin su yadda amfani yayi kyau.

Wasu da dama Kuma sun yi rantsuwa da cewa, basu taba samun amfanin gona mai kyau da albarka ba, sai da s**a yi wannan, sirrin sannan ALLAH ya basu amfani mai kyau, don haka kuma gashi nan kuyi da ikhlasi da izinin ALLAH za ku samu amfanin gona Wanda baku taba samun irinsa ba in Sha Allahu.

YADDA ZA AYI.

Ana samo holama wato takarda fara marar zane wato plain sheet guda 5 kowacce holama 1 za a rubuta mata FATIHA kafa 1 a jikinta.

Sai ayi laya sai a samo kwalabe guda 5 irin na, maganin yara sai a saka, kowacce laya guda 1 a cikin kwalba 1 sai a rufe da murfinta sai a ajiye su a waje mai kyau.

Sai a samo ruwa mai kyau idan son samu, ne a samo na sama idan kuma ba a samu ba sai a samo mai kyau kamar na famfo sai a zauna a karanta SALATIN ANNABI MUHAMMAD (S.A.W) Kafa dubu 1 ana karantawa ana tofawa har a kammala.

Wannan ruwan duk abun da za a shuka, sai a debi ruwan kadan a Zuba a cikin irin da za a shuka sai a jujjuyashi a hautsina sosai.

Sai aje ayi shuka, idan shukar ta fito su Kuma wadannan kwalaben da, aka rubuta fatiha aka saka a ciki sai a binne a kowacce kusurwa, ta gonar da Kuma tsakiyar gonar.

D'anuwa wallahi idan kayi wannan, sirrin da niyyar ALLAH ya baka, amfanin gona mai albarka wallahi sai kaga yadda ALLAH zai albarkaci gonarka, ya baka amfanin da baka taba samu ba in sha Allahu.

ALLAH ya baku, ikon yi Ameen. 🙏
👇
IZINI AYI, COMMENT DA SALATIN ANNABI, (S.A.W ) AYI SHARE DA LIKE DOMIN, 'YANUWA SU AMFANA.
👆

MIJI NA GARI yana buqata da kuma son waďannan Abubuwa guda 20 daga matar sa............💞(1) Yana son mace me bashi dukka...
19/05/2025

MIJI NA GARI yana buqata da kuma son waďannan Abubuwa guda 20 daga matar sa............

💞(1) Yana son mace me bashi dukkan Damar ya ji cewar "ya isa da ita, yana jin cewar ya isa ya saka ta ko ya Hana ta, wannan yana qara sanya shi jin tabbas shi MIJI ne kuma yana da mata.✍
💞(2) Yana son MACE me gaskiya, unguwa za taje ta fadi gaskiya, wani abu ya tambaye ta ta fada masa gaskiya, wannan yana sanya shi jin nutsuwa sosai tare da Matar sa.✍
💞(3) Yana son MACE me son ýan uwansa da Iyayen sa gami da mutunta su da girmama su, baya son a Raina masa su ko a wulaqanta masa su✍
💞(4) Yana Son MACE me son zaman Gidanta, ma'ana baya son mace me yawo na rashin mafadi✍
💞(5) Yana son macen da zata ta kula masa da karatun ýaýan sa da kuma Tarbiyyar ýaýan sa da Addinin su.✍
💞(6) Yana son mace me Tattali, duk abin da ya kawo ta taya shi tattalawa tamkar ita ta yi wahala ta kawo.✍
💞(7) Yana son MACE me adani da kintsi, komai ya shigo da shi bashi da haufi ko ya bata Ajiya Hankalin sa kwance ya san za'a adana mishi.✍
💞(8) Yana son MACE tashi shi kaďai, wacce za ta SO shi shi kaďai da dukkan zuciyar ta da soyayyar ta da kulawar ta.✍
💞(9) Yana son MACE me fahimta ba Me rashin kan gado ba, ta yanda ba shi da haufi wurin tattaunawa da ita da Hira da ita. ✍
💞(10) Yana son MACE me tsafta, na JIKI da na muhalli baki ďaya gami da qamshi me sanyi da sanya nutsuwa, iya sarrafa Ado da sauya salo a komai nata✍
💞(11) Yana son mace wacce ta iya sarrafa Abinci, ta yanda ko yaya ya kawo me yawa ko kaďan za'a ci ta dadin rai kuma a qoshi.✍
💞(12) Yana son mace me sauqin Kishi, wacce akan kishi ba zata haukace ba, ta daga Hankalinta ta hana kowa zaman lafiya ko ta yi mugun Aiki, yana son wacce za ta zauna lafiya da Abokan xamanta, kuma ta zama Adala a zamanta da su da shi✍
💞(13) Yana son MACE me Haquri da akwai da babu, da kuma juriya da Haquri da shi da Halin sa kan inda ya gaza na Ajizanci.✍
💞(14) Yana son MACE me Sirrin zama, ba ta yayata gidan shi ko sirrin sa a waje ko bini bini ta kir

Rannan Na hau Keke Napep zanje Unguwa sai wasu Mata guda biyu s**a shigo ana tafiya suna hirarsu ta duniya da ni dai ina...
16/05/2025

Rannan Na hau Keke Napep zanje Unguwa sai wasu Mata guda biyu s**a shigo ana tafiya suna hirarsu ta duniya da ni dai inata jan Carbina.

Siririyar ta cewa" Lukutar Ke kin yiwa Zee jaje kuwa?

Lukutar tace" me ya faru da ita?

Siririyar tace" bakisan kwanan gida taje ba aka samu matsala tayi targade

Lukutar tace" Dama matsalar kwanan gida kenan yanzu sauro yayi yawa matukar baki da maganin sauro sai kin kwaso Maleria

Siririyar tace" Hakane yanzu fa kwanan gida a matsala ne gwanda Kwanan Waje yafi tsaro musamman idan babanku baya gari.

Da naji hirar tasu tayi nisa, sai na ɗauko wayata na danna kira kamar da gaske kiran Wani nake sai nace" Hello!! Nisa'u a ajiye Waya?

Muka ci gaba da tafiya har aka zo inda zasu sauka bayan sun sauka daga Napep ɗin, sai Direban Napep ɗin ya kasa yin shiru yake ce min malam kaga zamani ko?

Yanzu dubi Yara ƴaƴan Musulmai ne s**a gwammace kwana a waje fiye da gidajen Iyayensu har suna hirar a t**i basa jin kunya.

Ni dai Nayi masa shiru saida aka zo inda zan sauka na bashi ƙudinsa nace" masa Baba duk sadda kaji ance maka Kwanan Gida ana nufin kwanan Hotel

Su waɗancan Matan da kaji suna maganar Kwanan Gida suna nufin Ƙawarsu ce ta kwana a Hotel aka kamata amma ba'a kulleta ba kuma iyayenta basu sani ba shine targaɗen da tayi.

Ni kuma da kaji na buga waya nace a Ajiye Waya" ina nufin suyi shiru saboda nazata ka fara gane hirar da sukeyi ne. Ashe ma kai Ciki Ne Ba Waje Ba.

Mai Keke Napep ɗin kawai sai a ɗora hannu a kansa yace" LAILALAHA ILLALLAHU Ashe Duk Ƴan Iska Uku na kwaso bansani ba nake ta kiranka da Malam kana amsawa...!😂

Kawai sai Nayi gaba ina jan Carbina Nabarshi iya mamaki.🥴🚶

AL-AJABI: Ko kun san wurare 5 a Duniya da Rana bata faduwaDaga Taskar LabaraiWurare guda biyar a duniya inda rana ke fit...
15/05/2025

AL-AJABI: Ko kun san wurare 5 a Duniya da Rana bata faduwa

Daga Taskar Labarai

Wurare guda biyar a duniya inda rana ke fitowa ba tare da ta fadi ba na tsawon kwanaki, musamman a lokacin bazara. Wannan abin al'ajabi na faruwa ne saboda yadda duniya ke juyawa

Taskar Labarai ta tattaro maku wuraren guda biyar da rana ke haskawa na tsawon sa’o’i 24:

1. Norway:
A arewacin Norway, musamman garin Hammerfest, rana idan ta fito to sai ta shafe tsawon kwanaki 76 wato watanni Uku (Mayu har zuwa Yuli) bata fadi ba.

2. Utqiaġvik, Alaska (Amurka):
Wannan gari shi ne mafi arewaci a Amurka. Rana na fitowa a can ba tare da fadi ba na kusan kwanaki 80 wato tun daga ƙarshen Mayu har zuwa farkon Agusta.

3. Lapland, Finland:
A wannan yanki na arewacin Finland, rana na ci gaba da bayyana a sama har na tsawon watanni huɗu wato daga Mayu zuwa Agusta.

4. Yukon, Kanada:
Yankin arewa da Yukon a Kanada na samun kwanaki masu tsawo da rana ke ci gaba da haskawa ba tare da faduwa ba.

5. Sweden:
A arewacin kasar Sweden, musamman a garin Kiruna, rana tana kwashe kusan wata biyu ba tare da faduwa ba.

Wadannan wurare suna jan hankalin masu yawon bude ido daga sassa daban-daban na duniya da ke sha'awar ganin wannan abin mamaki inda babu dare

Wanne gari kuke fatan ziyarta a ciki?

MAGANIN CIWAN QODA ciwan HANTA ciwan ZUCIYA mujarabun insha Allahu Duk Wanda yakeda daya daga cikin wa'yannan cututtukan...
01/05/2025

MAGANIN CIWAN QODA ciwan HANTA ciwan ZUCIYA mujarabun insha Allahu Duk Wanda yakeda daya daga cikin wa'yannan cututtukan kokuma dukkansu WA,IYAZU BILLAHI To anasamun wannan ciyawar kamar yadda kagani ajikin wannan hotan anacemata

DA'BURI

Anasamun ta acikin FADAMA kokuma RAFI watondai gurarenda akeyin noman LAMBU To anadafata ashanye Ruwan acinye CIYAWAR kuma anayankata acikin ABINCI Kamar yadda akeyanka TUMATIR kokuma ALBASA Acikin ABINCI aci to insha Allahu zakawarke kwata kwata kodakuwa yayimaka kamunda tafara kumbura JIKINKA Indai matsalar QODA CE dakuma CIWAN ZUCIYA Dakuma CIWAN HANTA Wallahil azimu wannan sirrin mujarabunne Duk Wanda yakeda wannan larurar kokuma Wanda yakeda Wanda yakefamada Ita To yadaure yayiwannan aikin Kamar yadda kagani insha Allahu zakasamu Lafiya zaiwarke dagadukkan wannan larurar wannan sirrin mujarabunne kadaure kajarabayin aikidashi kagani Allah yataimakemu Amin summa amin

26/04/2025

Abu biyu a Duniya kada kaji Tsoron su
1. ARZIKI
2. MUTUWA
SABODA DUK SUNA HANNUN ALLAH NE.

A yau da kullum, muna ganin yadda mutane ke yawan damuwa:
"Shin zan iya samun nasara?"
"Me zai faru idan rayuwa ta gagara?"
"Yaushe mutuwa za ta zo?"

Amma gaskiya daya ce:
Arziki da Mutuwa duk a hannun Allah suke.
Kuma wanda ya gaskata da haka, zai samu nutsuwa da karfin zuciya a cikin kowace irin rayuwa.

Kalli rayuwar yau da kullum:
Akwai wadanda suke gudun faduwa, su ki fara sana'a ko daukar mataki saboda tsoron rashin arziki.
Akwai wadanda kullum cikin tsoron mutuwa suke har s**a kasa jin dadin rayuwa.
Suna mantawa da cewa babu wani abu da zai same su sai abin da Allah Ya rubuta.

Allah (SWT) Yace:

"Allah ne mai yalwata arziki ga wanda Yake so kuma Yana takaita ga wanda Yake so."
(Suratul Rum: 37)

Ina da wata tambaya gare ka:
Me ya sa za ka ji tsoron arziki, alhali ka san Allah ne Mai bayarwa?
Me ya sa za ka ji tsoron mutuwa, alhali ita ce hanya zuwa ga rahamar Ubangiji?

Mu koyi daga abokan zamanmu:
Wani dan kasuwa yana iya fara karamar sana'a da hannu biyu, amma saboda dogaro da Allah, sai ya samu arziki fiye da yadda ya zata.
Wani yana cikin ƙalubale amma kullum yana cewa:
"Allah na tare da ni."
Shi yasa koda mutuwa ta zo, ya fuskance ta da imani da kwanciyar hankali.

Abin da rayuwa ke koya mana:

Ka nemi arziki cikin halal, ka bar tsoron talauci — Allah na gani.

Ka gyara zuciyarka da aikinka — don haka idan mutuwa ta zo, ka kasance mai farin ciki da haduwar da Allah.

Kada ka yarda tsoro ya sace maka farin ciki.
Ka rayu cikin aiki tukuru da addu'a.
Ka kasance daga cikin masu yawan ambaton Allah da tsayuwar zuciya.

Domin hakikanin rayuwa tana farawa ne lokacin da ka daina jin tsoron rasa komai — ka bar komai a hannun Allah.

Allah yasa Mudace......

01/04/2025

Mafarki! Mafarki!! Mafarki!!!
Wanda Yayi Mafarkin Gona da Yabanya Kore Shar Anayi Masa Bushara Da Zai Haifi Ƴaƴa Kyawawa.
Wanda Yayi Mafarkin Gona Ta Ƙanjame Kuma Zai Faɗa Wani Babban Iftila'i, Allah Ya Kyauta.
Wanda Yayi Mafarkin Yana Shan Rubutu Buƙatunsa Ne Zasu Biya..
Wanda Yayi Mafarkin Yana Yawo a Sama Kamar Tsuntsu Wannan Ɗaukaka Zai Samu Amma Zaiyi Gwagwarmaya Da Maƙiya Don Haka Yanemi Dafa'i...
Wanda Yayi Mafarkin Ya Hau Kan Dutsen Uhudu Zai Auri Mace Ko Zata Auri Namiji Wanda Ba Garin Su Ɗaya Ba..
Wanda Yayi Mafarkin Yana Gudu Shi Kuma Wani Abin Ƙi Ne Zai Same Shi Yayi Sadaka....
Wanda Yayi Mafarkin Raƙumi Na Binshi Wannan Mayu ne Ke Bibiyar sa .....
Wanda Yayi Mafarkin Yana Shan Kayan Marmari kamar su Mangoro Alkhairine....
Wanda Yayi Mafarkin Yana Limanci Tabbas Zai Samu Wani Jagoranci ne idan Macece tayi wannan mafarkin Tau Mutuwa ne....
Wanda Yayi Mafarkin Ana Ruwan Sama Shima Alkhairine....
Wanda Yayi Mafarkin Ya Yanka Kaza Zai Saki Matar Sa Ko Idan anga kazar ne za a auri mace mara hankali....
Wanda Yayi Mafarkin Zakara Wannan Cikar Addinin Mai Mafarkin ne .....
Wanda Yayi Mafarkin Hannun Sa Yayi Tsawo Ɗaya Yafi Ɗaya Zai Auri Mata ne Biyu ne Ɗaya tafi Ɗaya Tsawo a wani Qaulin Kuma Samun Biyan Buƙata ne na wani abu da aka saka gaba...
Wanda Yayi Mafarkin Taurari a sama wannan Kuma Zai Zama Maɗaukaki acikin Dangi.....
Wanda Yayi Mafarkin Yana Kuka Baƙin Cikine ga mai mafarkin....
Wanda Yayi Mafarkin Dariya Kuma Abin Farin Ciki Zai Samu Mai Mafarkin.....Anan Muke Dasa Aya A saurare mu zuwa gaba Insha Allah. Kuyi Sharing Ɗin Posting Don Ƴan Uwa Su Amfana Sannan Kuyi Following Ɗina Domin Samun Wasu Karatuttukan Anan Gaba,Masha Allah Tammat Bihamdillah.Dan Allah Kar Abini Private Domin Neman Neman Fassara Adaiyi Following Na Duk Lokacin Da Na Sake Karatu Za a gani

Allah shine Mafi Sani......09016332719 WatsApp

Address

Daura

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Salihu yareema posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category