22/02/2026
Dan girman Allah kuyi sharing!
Dan Allah muna mai neman taimakon gaggawa a garin Danjibga dake jahar zamfara!
Bayin Allah na cikin tashin hankali ,wanda yanzu haka Basu iya fita wajen gari kuma haka zalika bbu mai shigowa!
Wanda yanzu haka garin basuda komai bbu abinda zasuci hatta icce babu a garin ga azumi suna fama dashi a baki,ga rashin lafiya suna fama dashi,asibiti da sukeda ita a garin yanzu haka bbu komai cikin ta !
Yan bindiga sun tare hanyar shiga garin,wanda yanzu kan hanyar sun aje boma bomai,wanda munyi asarar rayuka da dama harda jami an tsaro suma sun taka wannan boma bomai da s**a aje akan hanyar garin!
Muna mai neman alfarma ga shuwabannin mu dan Allah su taimaka mana da agajin gaggawa dan Allah!
Allah ta'ala ya kawo mana karshen wannan taaddancin daya addabi Nigeria alfarmar manzon Allah!