Kundin Karattukan Mallan Ahmed Tijjani Yusuf Guruntum''

  • Home
  • Nigeria
  • Isa
  • Kundin Karattukan Mallan Ahmed Tijjani Yusuf Guruntum''

Kundin Karattukan Mallan Ahmed Tijjani Yusuf Guruntum'' Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Kundin Karattukan Mallan Ahmed Tijjani Yusuf Guruntum'', Grocers, Isa.

Duk wacce taga sunanta ta amsa tambayar da tazo Akan sunanta 1--fatima: ya sunan sayyidina Abubakar ?2--zainab: say nawa...
22/04/2024

Duk wacce taga sunanta ta amsa tambayar da tazo Akan sunanta

1--fatima: ya sunan sayyidina Abubakar ?

2--zainab: say nawa aka ambata annabi (S.A.W) acikin Alqur.ani ?

3-- maimuna : ya sunan mahaifiyar annabi ?

4-- Maryam: wani sahabi ne aka ambaci sunan sa a alqur.ani ?

5-- Aisha: surori nawane a alqur.ani ?

6-- Asiya: wacce halitta ce Allah ya halicce ta ba uwa ?

7-- safiya : shin matar annabi nuhu musulma ce ko kafira ?

8-- Salma: wacece matar annabi (S.A.W) ta farko ?

9-- hafas: fadi sunayen ulul azmi minar rusul ?

10--sa.adatu: annabi (S.A.W) yayi wafati Yana shekara nawa ?

11--habiba: hafsatu uwar muminai Yar wacece ?

12--hassan: a wani kogo annabi (S.A.W) yake bauta ?

13--usaina: wacce sura aka fara saukarwa annabi (S.A.W) ?

14--Rabi.atu: ya sunan mahaifin annabi (S.A.W) ?

15--sumaiya: wani sahabi ne ya auri ya Yan annabi (S.A.W) sau 2 ?

16--farida: Fadi kulafa'ul rashidun ?

17--khadija: ya sunan mijin Nana Fatima ?

18--fiddausi: wanene babban abokin annabi (S.A W) ?

19--hauwa.u : Fadi yayan manzon Allah (S.A.W) da sayyida usman ya aura ?

20--Asma.u: nawa ne adadin yayan annabi (S.A.W) ?

21--Nusaiba: Nana Aisha ta rasu Tana shekara nawa ?

22--Ramlat: ya sunan mahaifin annabi Yusuf ?

23--maryam : nawa ne adadin kufofin aljannah ?

24--Rukaiya: ya sunan Abu huraira ?

25--yasmeen : nawa ne adadin matan manzon Allah (S.A.W) ?

26--shamsiya: Fadi sunayen sahabbai guda 10 ?

27--shafa.atu : mutane nawa ne s**a hallarci yakin uhud ?

28--fa.iza : wanene mahaifin Nana Aisha ?

29--Amina : ranar arfa a wani wata ne ?

30--jamila: kabbara nawa akeyi a sallar Jana Iza ?

31-- suwaiba: ranar yaushe annabi (S.A.W) yai wafati ?

32-- Ramatu : ya sunan Abu zarri ?

33-- bilkisu: wacece ta raini annabi (S.A.W)

Zamu bibiya
Sannan kuma maza akwai naku

WUCE GONA DA IRI ACIKIN ADDUA…..1-Yana daga cikin wuce gona da iri a cikin addu'a, kuma shine ma yafi hatsari da cutar d...
21/04/2024

WUCE GONA DA IRI ACIKIN ADDUA…..
1-Yana daga cikin wuce gona da iri a cikin addu'a, kuma shine ma yafi hatsari da cutar da addinin bawa: wato Rokon wanin Allah ba Allah ba ko shi wanene kuma komai girmansa, k**ar rokon wanin Allah abinda ba wanda zai iya baka shi sai Allah.

Misali: Rokon Shehu da wasu daga cikin mutane a kasar hausa-fulani ke yi a lokacin da s**a zame zasu fadi, a madadin cewa: Innah lillahi wa innah ilaihi raaji'una, ko mak**ancin hakan, sai kaji sun ce ya shehu wane, wannan nau'i ne na wuce iyaka wanda ya kai yadda ya kai wajen muni, kuma ubangiji ta'alah ya kafirta ma'abota hakan a wurare da dama.

2-Yana daga cikin wuce-gona-da-iri a cikin addu'a: Bawa ya roki abubuwan da Allah ya kebanta da su a rububiyyarsa ko sifofinsa, k**ar ya nemi: Taskokin Allah su kasance a wajensa, don ya rinka bawa wanda yaso abinda ya so, ya kuma hana wani abinda yaso, ko kuma ya roki sanin gaibu, da sauransu.

3-Yana daga cikin wuce-gona-da-iri a cikin addu'a: Bawa ya roki abubuwan da basu dace da shi ba, wanda yasan Allah ba zai ba shi su ba; k**ar ya roki a bashi matsayi da daraja irin ta annabawa da manzanni, ko ya nemi a mayar da shi mala'ika; da zai wofanta ga barin bukatar abinci da abin sha, da biyan bukata, ko ya roke shi ya kasantar da shi ma'asumi k**ar mala'iku ko annabawa da sauransu.

4-Yana daga cikin wuce-gona-da-iri a cikin addu'a: Bawa ya roki abinda aka sani cewa Allah cikin hikimarsa ba zai aikata su ba; k**ar ya roki Allah ya dawwamar da shi ba mutuwa har zuwa kiyama; (ma'ana: kar ya dauki ransa), ko ya nemi a kawar masa da halayya da bukatu na 'dan adam k**ar ci, sha, barci, mantuwa, ko ya musuluntar da duk duniya, ko yasa kowa-da-kowa cikin aljanna, ko ya bashi 'da ba tare da mace ba, da sauransu.

5-Yana daga cikin wuce-gona-da-iri a cikin addu'a: Bawa ya roki abinda Allah ya hane shi, k**ar mai neman taimakon Allah kan aikata haramun, misali: ya roke shi ya saukake masa hanyar alfasha ko magudi da zalunci da handama, ko ya taimake shi kan wani tafiyar da ya shirya don yin barna da zunubi a cikinta; k**ar sata, fashi, d. s.

6- Yana kuma daga cikin wannan nau'in: Bawa ya nemi Allah yayi gafara ga wadda ya mutu yana kafiri ko shi wanene; saboda Allah ya hana hakan, Lallai kuma wannan na faruwa da yawa musamman a zamaninmu; zamanin fitintinu da kashe-kashe, ta yadda sau da dama akan samu masu kashe mutanen da basu san me yasa s**a kashe ba, k**ar yadda mutane da-dama da aka da dama daga wadanda ake kashewan suma basu san dalilin da yasa aka kashe su ba. To a irin wannan hali in har labarin irin wannan mutuwa mai abun tausayi yazo maka sai kace: Allah ya jikan musulmi. Amma bai halatta kayi addu'ar gafara, rahama da jin kai ga wanda ba musulmi ba ko wanene shi; mahaifi ne, mahaifiya, 'da, b***e waninsu.

7- Yana daga cikin wuce-gona-da-iri a cikin addu'a: Bawa ya nemi Allah ya la'anci muminai, ko ya musu addu'an tabewa, kaskanci da nema musu masifa.

8- Yana daga cikin wuce-gona-da-iri a cikin addu'a: Bawa ya yawaita maganan da ba a bukata a lokacin addu'arsa, k**ar yace ya Allah in ka shigar dani aljanna ka bani: farin-gida (white house), ta hanun damanta, Shi yasa wani daga cikin salaf da yaji 'dansa yana addu'a yana fadan irin haka sai ya kwabe shi, sannan ya gaya masa cewa Manzo (s a w) yace: Za a samu wassu da zasu rika wuce gona-da-iri a cikin addu'a da tsarki, A hir dinka ka kasance daga cikinsu, in zaka roqo Aljannah ka roqi Aljannah kawai.

9- Yana daga cikin wuce-gona-da-iri a cikin addu'a: Bawa ya rika daga sauti a cikin addu'arsa, shi yasa yazo a cikin wata aya cewa: Ku roki Allah a boye; lallai Allah baya son masu wuce iyaka, Abdulmalik bn Abdul'aziz bn Juraij yace: "Lallai a cikin addu'a akwai wuce iyaka: An ki daga sauti, ihu da hauragiya a cikin addu'a, ana kuma umurni da Kankan-da-kai, da kuma nitsuwa, Ga lafazin nasa a larabce, ko acikin ko wanne irin harshe.
Ubangiji ka datar damu baki daya.
Mallam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum
Abdussamad Tijjani Sani ✍️

DAGA CIKIN ILLAR MADIGO A TAKAICE….Manzon Allah (SAW) a Hadisin Ibn Abbas (RA) a lokacin da yake jero wadanda Allah ya t...
20/04/2024

DAGA CIKIN ILLAR MADIGO A TAKAICE….
Manzon Allah (SAW) a Hadisin Ibn Abbas (RA) a lokacin da yake jero wadanda Allah ya tsine masu, harda ‘yan Luwadi’, Allah ya tsine ma duk masu aikin (luwadi), irin aikin da mutanen Annabi Lut s**a yi, Wallahi wanan tsinuwa ta shafi hadda yan madigo.

Karka/ karki yarda ku shiga cikin wannan tsinuwar ta Allah da tsinuwar Manzonsa, mala’ikunsa da mutanan kirki, domin babu asara ga dan adam k**ar ace Allah da Mazonsa sun tsine masa, lallai asara takai asara, Allah ya kiyaye mu.

Ta fannin zamantakewa da kiwon lafiya kuwa, akwai illoli masu yawa da madigo da luwadi ke haifarwa a jikin ma’abocinsu k**ar haka:

1. Suna kawar da sha’awar aure baki daya, domin a addinance da kuma al’adance akan daura aure ne tsakanin mace da namiji, To macen da take madigo zata kasance bata sha’awar namiji baki daya, ko tayi auren, tayi ne kawai, amma ba zata yi sha’awar mijin ba.

2. Ba zata sami biyan bukata a kwanciyar aure ba. Shi kuma jima’i a tsakanin ma’aurata, yana kara gina so da kauna a tsakanin juna, Koda an sadu da ita, to ba zata ji sha’awarta ta gushe ba har sai ta hadu da ‘yar uwarta mace sun goga da juna, Shi yasa kake ganin hatta daga cikin matan aure masu irin wanan mummunan aikin, suna aikata wannan mummunar dabi’ar, ko da kuwa suna gidan mijinsu.

3. Madigo na haifar da yaduwar ciwon sanyi. a duk lokacin da wadda take dauke da ciwon sanyi tayi tarayya da wadda bata da shi, to anan zata harba mata shi, domin wannan discharge din yana dauke da kwayoyin cuta da zasu yadu har ya shafe ta.

4. Madigo yana haifar da cututtukan da ke sa kaikayi ga farjin mace, idan mai kaikayin mara ko kuraje a cikin farji ko zubar farin ruwa, sanadiyyar wani infection, k**ar na vulvo vaginal candidiasis, yeast infection, da sauran su, idan s**a yi gogayya da juna, to zata dauki wannan ciwon, cikin sauqi.

5. Madigo yana haifar da yaduwar cutar Kanjamau/Sida (wato AIDS). Kuma ban ga yadda za’a kare wannan kwayar cutar ba, domin takan biyo ruwan dake fitowa a gaban mace ta shafi ‘yar uwarta, kuma ba za’a iya yin amfani da condom ba, kuma ma bincike ya nuna cewa Condom ba ta iya kare komai. Kawai magani shine, aji tsoron Allah a daina (Abstinence).

6. Madigo yana haifar da ciwon mara – Dama, su mata sun fi kowa yawan ciwon mara, wasu ma da shi aka haife su, wasu kuma a lokacin al’ada yake zo masu, wasu kuma daga baya s**a dauko shi a wani wuri (infections). Gogayyar da suke yi gaba-da-gaba da juna na haifar da kamuwa da ciwon mara, musamman na infections. Ayi ta faman neman magani a rasa sanin dalili.

7. Madigo yana haifar da ciwon ruhi (spiritual problems) – A nan, shi ciwon ruhi ba fa ciwo bane da zaki gani a zahiri, amma a hakika zaki ji alamunsa a gangar jikin ki. Na farko dai zai busar da zuciyar ki, sai ya kasance baki shakku ko tinanin zaki iya mutuwa a kowane lokaci. Sha’awarki zata gushe ta koma ga ‘yan mata kawai. Da zaran kin ga mace mai girman kirji ko mai manyan mazaunai duk sai sha’awarta ta k**a ki. Sannan komai nisan ki da ita zaki iya neman ta. Har ki tsufa zaki kasance kina ganin sha’awar mata ‘yan uwanki.

8. Zai janyo maki gushewar farin jini a fuskar maza, sai kiga duk masoyanki mata ne, gaki kyakkyawa amma ba mai so, basirar ki tabi ta dushe, tunanin ki ya sauya. Wata rana sai ki kasa daina wa. Kuma zuwa gaba sai ya busar da ke, ki rinka ramewa, duk ni’imar jikin ki ta mace, ta gushe, kibi ki bushe, kiyi matukar muni. Kuma a lokacin sai kiyi dana-sani, a lokacin da dana-sanin ba zai amfane ki ba! Allah ya shirye mu baki daya.

Dr Sumayya Ibrahim Sa'ad Shin akwai kuskure cikin wanan bayani domin kuna daya daga cikin masana harkar lafiya ta dan Adam, hakika zan so mu qara samun haske cikin comment section.
Muhammad Ubale Kiru, Ina fatan zaka qara wayar mana da kai dan gane da wanan al’amari duk da cewar nasan kana iya bakin qoqarinka.
Abdussamad Tijjani Sani✍️

BABU ALKAIRI A ZINA, LUWADI, DA MADIGO…….Zina, luwadi da madigo suna tattare da zubewar mutuncin mutum da kuma wulakanci...
20/04/2024

BABU ALKAIRI A ZINA, LUWADI, DA MADIGO…….
Zina, luwadi da madigo suna tattare da zubewar mutuncin mutum da kuma wulakanci da suke sa mutum ya fada ciki, tare da kaucewar mutum daga kan manufar Allah a kan sa, kuma sun kasance manya-manyan zunubai abin kyama a wurin Allah, Sannan suna tattare da sharri da cutar da ta kai ace gwanda mutum ya rasa rayuwar sa ta hanyar kisan gilla da ace yana rayuwa cikin aikata wannan aikin, saboda duk mutumin da ya dauki wannan hanya ta lalacewa, to zai zama sharri da guba ne a cikin al’ummah, domin za’a wayi gari baya jin kunyar Allah b***e jin kunyar mutane, Kuma shiriya za ta yi wahala a wurin irin wannan mutum, sai fa idan Allah ne ya nufe shi da shiriyar.

In ban da toshewar basira da kokarin fito-na-fito da Allah ba, ya za ace namiji ya kwanta da namiji dan uwansa ko kuma mace ta kwanta da mace yar’uwarta, Namiji ya kwanta da mace wadda take haramun agare shi.

Amma a yau, an wayi gari duniyar kimiya da fasaha musamman duniyar yanar gizo (internet), an mayar da ita daya daga cikin hanyoyin da ke koyar da wadannan munanan dabi’u, musamman a social media, inda zaka tarar a can da suna yi abin sune a boye, amma yanzu sun fito fili har groups su ke da shi daban-daban a Facebook, WhatsApp Telegram da sauran su, kuma basa jin kunyar tallata wanan groups din nasu, wani abin takaici shine za ka tarar mafi yawansu da mabiyansu hausawa ne, kuma Musulmai, kuma ‘yan arewa.

Kenan ya zama dole a kan mu, mu tashi muna tallata addinin mu da al’adunmu, tare da rubuce rubuce akan illar zinah luwadi da madigo ya zama yana daga cikin abinda zamu dinga yawan bincike muna posting nashi a social media.

Don haka ina kira ga Malamanmu da Masarautunmu da Gwamnatocinmu da likitocinmu da masana hakayyar ‘yan Adam (Psychologists) da Hukumomin kula da harkar fina finai da kuma Matasanmu masu kishi da dukkanin masu ruwa da tsaki wurin ci gaban wannan al’ummah da zaman lafiyar ta, da mu tashi tsaye baki daya, mu hada karfi-da-karfe mu yaki wannan mummunar al’ada ta luwadi da madigo da zinah a cikin al’ummah, kafin mu jawo wa kan mu fushin Allah.

Ina fatan duk masu irin wannan hali Allah ya shiryar mana da su, mu kuma Allah ya kare mu daga irin wannan mafi munin aikin dabbancin.

Next zamu yi magana akan Illolin madigo da luwadi a kimiyance, in sha Allah.
Professor Isa Ali Pantami
Abdussamad Tijjani Sani✍️

AIKIN LADA MAI GUDANA A SOCIAL MEDIA….Yana daga cikin ayyuka masu falala a social media, wanda kuma mutum yake samun lad...
20/04/2024

AIKIN LADA MAI GUDANA A SOCIAL MEDIA….
Yana daga cikin ayyuka masu falala a social media, wanda kuma mutum yake samun ladansu har bayan ransa, akwai kiran mutane zuwa ga hanyar Allah zuwa ga shiriya, duk wanda yayi kira zuwa ga shiriya yana da kwatankwacin ladan wa’inda s**a bishi kuma ba za’a rage musu komai na ladansu ba, inji Annabin Allah.

Wannan yana nuna Falalar Kira zuwa ga alkhairi da shiriya da Sunnah, yake kuma nuna hadarin kira zuwa ga bata, da sabon Allah da Bid’ah, Sannan kuma ya k**ata mutum ya sani cewa shi kira zuwa ga shiriya yakan kasance ta hanyar Magana ko da aiki, kenan kada ka fadi wata magana ko ka aikata wani aiki wanda kasan wani zaiyi koyi dakai a kansa, sai in ya kasance wannan aiki ne da ya zama ba na sabon Allah bane.

ZUNUBI MAI GUDANA A SOCIAL MEDIA….
haka nan wanda yayi kira zuwa ga wani ɓata yana da zunubi kwatankwacin zunubin wa’inda s**a bishi kan wannan ɓata kuma ba za’a rage musu komai daga zunubinsu ba.

Daga cikin ƙira zuwa ga ɓata akwai yaɗa Alfasha tsaƙanin Musulmai, domin hakan zai iya saka wani yaje ya aikata wannan alfashan, Don haka ya dace Musulmi ya kula sosai kan abubuwan da yake yaɗawa a social media, domin laifin ba ga wanda ka tura masa kaɗai yake tsaya wa ba, zaka iya tura wani abu mara kyau na saɓon Allah laifin yaci gaba da binka har ranan tashin Al Qiyaama.

MISALI…..
Idan ka tura wani abu na batsa wa mutane, wannan batsa zai cigaba da yaɗuwa ne shekaru aru aru, kuma kullum kana samun zunubi ne, musamman a irin wannan zamani na yanar gizo, wanda da zarar ka tura abu kafin mintoci kaɗan ya zagaye duniya,
ashe akwai buqatar ace muna kula, da duk abinda muke yadawa a social media, ya zamto abinda za mu faɗi ko zamu tura baya ƙunshe da saɓon Allah.

Wallahi Tallahi masu yaɗa alfasha cikin Musulmai in basu tuba ba har s**a mutu toh Suna da azaba mai raɗaɗi kuma a kullum suna ƙara samun zunubi ne da adadin wanda wannan alfasha da s**a yaɗa ya riska su, inya zamto abinda zamu faɗi babu Alkhairi aciki toh shiru shi yafi mana alkhairi.
Muji wanan da kyau……

Allah yasa mudace, Ya kuma bamu ikon tuba zuwa gare shi ya bamu ikon aikin alkairi ya kuma sanya mana cikin mizani na hasaana.
Mallam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

Abdussamad Tijjani Sani ✍️

20/04/2024



Kayiwa Kanka Tanbayoyi guda 7
👇
1 Kai Waye...?
2 Waye Yayi ka..?
3 Maiyasa Yayika..?
4 A Ina Kake..?
5 Me Kakeyi...?
6 Ina Zaka...?
7 Me Zai Faru...?

Abubuwan 7, Dazasu Faru bayan Zaman Duniya
👇
1 Mutuwa..!
2 Zaman Qabari Da Tambayar Qabari
3 Tashin Qabari/Tashin Qiyama
4 Hisabi
5 Sikeli
6 Siradi
7 Tafiya Zuwa Wuta Ko Aljanna.

Tambayoyi guda 7 dazamu Amsa Bayan Mutuwa,. 3 a Qabari, 4, A gaban Allah
👇

3 A Qabari
1 Man Rabbuka..?
2 Waman na biyuka..?
3 Wama Dinuka .. ?

4 A gaban Allah
1 Ya ka Tara Dukiya..?
2 Yaya kaka Sheta...?
3 Ilimin Da kasamu Na Addini ne Na Boko ne ya Kayi dashi wajan taimakon al'umma...?
4 Yakayi Amfani Da lokacinka, ...?

Allah Yasa Mu Dace Duniyar-mu Da Lakhira Amin

MUGUN CIWO MAI AJALIN MAI SHI……Mutane da dama s**an tsinci kansu a cikin wani yanayi mai ban al’ajabi, za kaga mutum yan...
18/04/2024

MUGUN CIWO MAI AJALIN MAI SHI……

Mutane da dama s**an tsinci kansu a cikin wani yanayi mai ban al’ajabi, za kaga mutum yana yawaita Azumi, Nafilfili, tsayuwar dare, Sallolin Farilla sam basa wuceshi amma sam baya cigaba a rayuwarsa, kullum yana nan a inda yake, daga cikin babban dalilin haka, Zuciyarsa tana dauke da ciwon hassada, sam babu alkhairi a mu’amalarsa da mutane, kullum ya bude bakinsa sai dai ya fadi Sharri ko ya kulla Makirci, ko kuma zargi akan abinda ba damuwarsa bace.

DAGA CIKIN ALAMAR HASSADA…..

Kaji kana cewa wani ji shi k**ar ba kwanan nan yazo muke taimaka sa ba, oh su wane an haye, sai kace da ba teburin mu daya a wajen aiki ba, lokacin nan kuwa kayansa basu wuce kala biyar ba, ji wai yanzu shine kaza, sai kace ba tare aka daukemu aiki ba, nan fah yake zuwa nake bashi aron kudi sanan yaje yaci abinci, kana fara jin haka to hassada ta fara auren ka.

SHAWARA TA GARE MU…..

To mai zai hana kayi kokarin cire kanka akan duk wani al’amurran da basu shafe ka ba.
Kayi kokari wajen focusing akan inganta rayuwarka, ka kiyaye kanka daga kananan Gulmace-Gulmace.

HABA ABOKI NA…..

Yadda zaka kare kanka daga Hassada shi yafi komai sauki, saboda ai yin Hassadar yafi wuya, domin takurawa kanka kawai ka keyi dole sai kayi Hassadar, to k**ar yadda kake takurawa kanka yin hassada, k**ar hakane zaka danne zuciyarka, da dauke hankalinka daga kan duk abinda kasan cewa falala ce ta Allah don wa bawa waninka, ka sanyawa zuciyarka hakurin domin kaima akwai inda kafi waninka.

Ubangiji ka rabamu da ciwon hassada.

Mallam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

Yahaiya Sani Abubakar ✍️

18/04/2024

ka taimaki mahaifanka da gwargwardon karfinka!

Don ba lalle bane lokacin da zakayi arziki suna raye duniya ba.

MU HARAMTAWA MATAN MU SHIGA WUTA…….Ya ku bayin Allah! yana daga cikin rahamar Allah ta’ala, da ya rufewa bayinsa qofofin...
18/04/2024

MU HARAMTAWA MATAN MU SHIGA WUTA…….
Ya ku bayin Allah! yana daga cikin rahamar Allah ta’ala, da ya rufewa bayinsa qofofin sharri, ya toshe duk wata qofa ta fitina, da sabon Allah.

Wanda duk ya bude wannan qofa kuwa, to zai fada cikin sabon Allah da zunubi, Sannan kuma abu ne sananne ga kowanne mutum irin hadarin da qasashen musulmi s**a fada na fitsarar mata, da shiga ta rashin kunya da gujewa hijabi, da bayyana kwalliyarsu ga mazajen da ba nasu ba.

Babu shakka wannan abu ne da yake jawowa al’umma fushin Allah da azabarsa idan ba su tashi sun gyara halinsu ba, Ya ku jama’ar musulmi, ku yi aiki da umarnin Allah, ku tilastawa matanku kyakkyawar shiga, da sutura ta musulunci, wanda hakan zai sa su sami kubuta, ku ma ku kubuta.

Allah ta’ala yana cewa: Ya kai wannan Annabi ka gayawa matanka da ‘ya’yanka mata, da matan muminai, su lullube jikinsu da mayafansu, don da haka ne za a gane su, kuma ba za a cutar da su ba. Lallai Allah mai yawan gafara ne mai jinqai, a nan Allah ta’ala yana umartar mata musulmai da su lullube jikinsu da sutura ta musulunci wato hijabi, ta haka ne za a gane cewa su mata ne k**ammu, ba za su fitini mutane ba da kyan da Allah ya yi musu, kuma su ma ba za a fitine su ba, ta hanyar maganar banza.

Don haka ku ji tsoron Allah ya ku musulmai, Ku hana wawayenku yin wauta, Kuma ku hana matanku aikata abin da Allah ya haramta, Ku umarce su da sanya hijabi da sutura ta musulunci, kuma ku tsoratar da su fushin Allah.

Kamar yaddda ya tabbata a hadisi, Imam Ahmad da Abu Dawud da Tirmizi s**a rawaito shi, daga Abubakar Siddiq (R.A), cewa manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Lallai idan mutane s**a ga azzalumi yana zalunci, kuma ba su hana shi ba, to ba da dadewa ba Allah zai lullube su da uqubarsa.

Ubangiji ya datar damu baki daya.
Mallam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum
Dr. Bashir Aliyu Umar
Abdussamad Tijjani Sani✍️

DA ME K**E TAQAMA K**E TINQAWO?Kyawun fuska, kyawun halitta, kyawun sura da diri, iya tafiya da kwalliya ko kuma me?Haki...
18/04/2024

DA ME K**E TAQAMA K**E TINQAWO?
Kyawun fuska, kyawun halitta, kyawun sura da diri, iya tafiya da kwalliya ko kuma me?

Hakika duk cikakken namiji wanda ya amsa sunansa namiji, babu shakka yana son wayannan abubuwa da na zayyana, amma cikakken namiji wanda ya amsa sunansa namiji kuma yasan abinda yake, wayanan abubuwa basa cikin lissafinsa ga wadda yake son aura, domin yasan nan gaba kadan zasu gushe su barki da halayenki ta yadda shi kuma zai cigaba da shan wahalar zama dake, wai idan ma kin yi sa’a mai hakurin ne.

Amma namiji wanda yasan abinda yake yafi kallon kyawawan mu’amalarki, tsayuwarki akan addininki, tarbiyarki, hankalinki, nutsuwarki, sanin ya k**anki, saboda acikin wayan nan abubuwan ne zai samu nutsuwa da ke bayan ya aure ki, alokacin da duk wani kyau naki ya gushe awanan lokacin kyawawan halayyarki zasu sake mamaye masa zuciyarsa.

SHAWARA TA GARE KI…..
Kiyi qoqarin zama mace ta gari mace wadda take alfahari da addininta, tarbiyarta, asalinta, da hankalinta.

Sister kina zama ta gari iskan da ke ratsa gidan ki zata canza, Ki ji kin samu wani qarin kwalliyan da baki iya ganinta, Ki ji kin samu qarfin guiwar kusantar Mahaliccin ki, ki ga samari na gari suna neman aurenki, idan kinyi auren kuma kiji dadin zaman auren, Kuma zaki samu mabuɗin buďe kofar shigar ki zuwa Jannah.

TO WAI TAYAYA ZAN ZAMA MACE TAGARI?
2-Farkon matakin zama ta gari shine ki kasance musulma, wacce ta yi imani da Allah ta kaďaita Shi a matsayin abun bautar ta, kuma ta miqa wuya ga Allah ta hanyar miqa wuya ga umurnin Sa da dokokin Sa, ta yi imani da Annabi Muhammad ta hanyar yi masa da’a a umurnin sa da gasgata shi a labaransa, tare da nisantar haninsa.

2-Ilimi da aiki da shi shima yana daga cikin matakin farko ga dukkan macen da take son zama ta gari. da ilimi ne ake sanin matakan zama musulmi na gari mai kyawawan halaye da dabi’u, da ilimi ne ma ake sanin yanda ake bauta ma Allah, duk macen da ba ta da ilimi kuma bata neman sa, to hakika zaman ta na gari zai yi mata wuya, sboda ba ta da fitilar da zata rinqa haskaka mata hanyar rayuwarta.

Kuma kada ki ce wai kin yi sauka shi kenan kin bar neman ilimi, A’a ki cigaba da zuwa in da za a rinqa tunatar da ke Allah, In da za,a nuna miki hanyoyin shiga Aljannah, in da za’a rinqa koya miki zamantakewar magabata don ke ma ki yi koyi da su. In da za a koya miki yanda zaki tarbiyyantar da ‘ya’yanki, In da za a tunatar da ke aure da kuma muhimmancin sa, don samun tsira a gobe qiyama, Wurin da za a rinqa nusar da ke ladabi da biyayyan miji, da kokarin gyarawa da kyautata zamantakewar ku.

Sannan shi ilimi ai kogi ne yana da yawa, ki cigaba da nemansa, zai sanya miki son addini da son ibada, kuma za’a rinqa miki wa’azi a hankali kina gyara halin ki, Sannan uwa uba ilimi zai taimaka ma ‘ya’yanki, domin zaki taya su tilawa a gida, zaki musu assignment, zai taimakawa mijinki domin zama da jahili akwai wahala mutuqa, kin ga kuwa dole mace ta gari ta nemi ilimi.

Idan mun samu lokaci zamu dora daga inda muka tsaya in sha Allahu.
Ubangiji yasa wanan sako ya amfanar damu baki daya.
Copied by Babban Yaya Abdussamad Tijjani Sani✍️

ALLAH KA AMSA MANA…….Ya Allah kai ne mai jujjuya zukata, ka tabbatar da zuciyarmu a kan addininka, Allah ka shiryar da m...
17/04/2024

ALLAH KA AMSA MANA…….
Ya Allah kai ne mai jujjuya zukata, ka tabbatar da zuciyarmu a kan addininka, Allah ka shiryar da mu ga mafi kyan halaye, babu wanda yake shiryar wa ga ma fi kyan halaye sai kai, Kuma ka raba mu da miyagun halaye, babu mai raba mutum da miyagun halaye sai kai.

Ya Allah ka taimaka mana bisa ga ambatonka, da gode maka da kyautata bauta gareka, ya Ubangijinmu kada ka karkatar da zukatanmu bayan ka shiryar da mu, lalle kai mai yawan kyauta ne.

BAYAN HAKA…..
ya ku wadanda s**a yi imani, ku gaggauta tuba, tuba ta gaskiya zuwa ga Allah, hakika wanda baya laifi Manzon Allah (S A W) yana tuba sau saba’in a yini guda.

Tuba ta gaskiya ita ce wadda ta cika sharudan da malamai s**a fada guda hudu.
Sharudan su ne: Yin nadama a kan abin da ya wuce, da quduri kan ba za’a sake aikata laifin ba acikin abida yayi saura naga rayuwar bawa, kuma ya daina sabon, idan a lokacin yana yin sa.

Idan kuwa laifin ya shafi bayi ne cikin haqqoqinsu, to sai ya biya su, ko ya nemi yafiyarsu, sharadi na qarshe, ya tuba a lokacin da lokacin tuba ne, kafin ya sharafa, ko kuwa rana ta fito daga yamma.
Allah ya datar da mu, ya bamu ikon tuba zuwa ga Allah.

Mallam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum
Abdussamad Tijjani Sani 🙏

DAGA CIKIN MASU SHIGA INUWAR ALLAH, A RANAR DA KOWA YAKE NEMAN INUWA…..1-Shugaba adali: Shugaban da yake tsoron Allah ga...
17/04/2024

DAGA CIKIN MASU SHIGA INUWAR ALLAH, A RANAR DA KOWA YAKE NEMAN INUWA…..
1-Shugaba adali: Shugaban da yake tsoron Allah game da talakawan da yake kiwo, yake daidaita kansa da su, yake tausaya musu ya ji kansu. Ya kwato hakkin wanda aka zalunta daga azzalumi, k**ar yadda mazajen farko na wannan al’umma Halifofin Manzon Allah (SAW) s**a aikata.

2-Matashin da ya tashi cikin da’a ga Allah. Wannan matashi ya rayu yana mai ibada ga Allah, mai karanta littafinSa, mai bin Sunnar ManzonSa (SAW), mai runtse ganinsa, mai tsare gabbansa daga abin da Allah Ya haramta. Ba ruwansa da giya ko kwaya ko abubuwa masu bugarwa. Shi dai ya tafiyar da lokacinsa wajen da’a ga mahaliccinsa.

3-Mutumin da zuciyarsa ke ta’allake da masallaci, idan ya fita daga gare shi har sai ya dawo gare shi. Ya bayin Allah! Zuciya tana ta’allaka ne da abin da aka sabar mata. idan aka saba mata da da’a ga Allah da ikhlasi, sai ta ginu kan haka, ba za ta ji dadin sabanin haka ba. Idan aka saba mata da son sabo aka dauwamar da ita kan aikata haka, sai ta ta’allaka da shi. Don haka mutanen kwarai suna natsuwa ne da ambaton Allah Madaukaki.

Manzon Allah (SAW) yana siffanta mana ayyukan wadannan mutane, domin muyi kwaikwayi kasancewa daya daga cikinsu, kuma domin mu tsarkake ayyukanmu, mu samu wannan daraja madaukakiya, mu samu wannan karramawa mai girma, mu kubuta a ranar da yara ke zama masu furfura, ranar guje wa iyaye, ranar da uwa ke jefar da jaririnta da take shayarwa, ranar da Annabawa suke cewa a cikinta “Ya Ubangiji! Sauki! Sauki!! sauki!!! Illah Manzon Allah ka dai wanda shine zai kasance yana cewa UMMATI! UMMATI!! UMMATI!!!

Ubangiji ka datar damu baki daya.
Mallam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum
Abdussamad Tijjani Sani✍️

Address

Isa

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kundin Karattukan Mallan Ahmed Tijjani Yusuf Guruntum'' posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category