A A M MEDIA

A A M MEDIA My name is Abdulkarim auwal maihafizai I am in kaduna state

Duk da cewa majalisar dattawa ta yi wa ƙudirin dokar karatu na biyu kafin tafiyarta hutun ƙarshen shekara, an dakatar da...
14/01/2025

Duk da cewa majalisar dattawa ta yi wa ƙudirin dokar karatu na biyu kafin tafiyarta hutun ƙarshen shekara, an dakatar da dukkannin wasu ayyuka kan ƙudirin sakamakon janyo hatsaniya da ya yi daga faɗin ƙasar.

An nemi shugaba ƙasa da ya janye ƙudurin ko kuma majalisa ta yi watsi da ƙudurin baki ɗayansa, amma daga bisa sai majalisar ta dattawa ta sanar da jingine aiki kan ƙudirin.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibrin - wanda ya jagoranci zaman - shi ne ya sanar da hakan yayin da suke muhawara zauren majalisar.

Hakan na zuwa ne ƙasa da kwana ɗaya bayan Shugaba Tinubu ya umarci ma'aikatar shari'a ta ƙasar ta yi aiki tare da majalisar dokokin domin samun masalaha kan wasu ɓangarori na dokar da ake taƙaddama a kai.

Barau ya kuma sanar da kafa wani kwamati da zai yi aikin dubawa da kuma gyara saɗarorin dokar da ke jawo taƙaddama, musamman daga yankin arewacin ƙasar.

Majalisar ta kafa kwamiti ƙarƙashin sanata Abba Moro daga jihar Benue domin tattaunawa da ministan shari'a kan yadda za a yi wa ƙudirin garanbawul kafin sake mayar da shi ga majalisa.

Kuma bayanai na nuna cewa kwamitin ya kammala tattaunawa da tuntuɓar juna dangane da gyran siɗirorin da ke janyo cece-kuce a ƙudirin, inda bayanai ke nuna cewa akwai yiwuwar gudanar da jin ra'ayoyin ƴanƙasa kafin majalisar dattawa ta yi wa dokar karatu

Jam'iyyar adawa ta Labour a Najeriya ta zargi gwamnatin kasar da gazawa wajen yi wa 'yan Najeriya bayani kan yadda aka y...
13/01/2025

Jam'iyyar adawa ta Labour a Najeriya ta zargi gwamnatin kasar da gazawa wajen yi wa 'yan Najeriya bayani kan yadda aka yi da naira biliyan 234 wani bangare na kudin kidayar jama'a da aka shirya gudanarwa a shekara ta 2023, da aka dakatar.

Jam'iyyar na zargin cewa an karkatar da kudaden ne wajen yakin neman zaben 2023.

Jam'iyyar ta Labour ta ce a karkashin gwamnatin da ta gabata ta shugaba Muhammadu Buhari, hukumar kidayar jama'a ta kasar ta bukaci a sahale mata kashe naira biliyan 800 domin gudanar da kidayar jama'a data gidaje, to amma bayan watanni 17 shiru kake ji babu wani abu da aka yi, sannan kuma gwamnatin shugaba Bola Tinubu bata ce komai ba a kai ballantana sanar da ranar da za ayi kidayar.

Shirun da gwamnati mai ci yanzu ta yi wajen kin bayani a akan halin da ake ciki a game da batun kidayar shi ne ya janyo wannan zargi da jam'iyyar ta Labour ta yi.

Dr Yunusa Tanko, daya ne daga cikin masu magana da yawun jam'iyyar, kuma ya ce a yanzu dai shugaban Najeriyar Bola Ahmed Tinibu bashi da wani bayani da zai yi wa 'yan Najeriyar kan yadda aka yi da kudaden kidiyar, saboda gazawar gwamnatinsa na sanar da ranar da za a gudanar da ita.

Gwamnatin Najeriya ta amince da kamfanonin jiragen sama guda huɗu domin jigilar maniyyata Hajjin bana.Wannan na ƙunshe n...
13/01/2025

Gwamnatin Najeriya ta amince da kamfanonin jiragen sama guda huɗu domin jigilar maniyyata Hajjin bana.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban hukumar jin daɗin alhazai ta Najeriya, NAHCON, Farfesa Abdullahi Usman ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce an zaɓi kamfanoni huɗu ne daga cikin guda 11 da s**a nuna sha'awar aikin jigilar maniyyatan, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Ya ce kamfanonin huɗu su ne: Air Peace Ltd, da wani kamfanin ƙasar Saudiya mai suna Fly-Nas da Max Air da kuma UMZA Aviation Services Ltd.

Ya ƙara da cewa kwamiti mai mutum 32 da aka kafa a ranar 26 ga Nuwamban bara ne s**a zauna s**a tantance kamfanonin, kafin s**a amince da guda huɗun

Ƙungiyar nan ta ƙasa da ƙasa, ta Global Firepower, mai fitar da jadawalin mizanin ƙarfin sojojin ƙasashen duniya, ta fit...
12/01/2025

Ƙungiyar nan ta ƙasa da ƙasa, ta Global Firepower, mai fitar da jadawalin mizanin ƙarfin sojojin ƙasashen duniya, ta fitar da rahoton da ke cewa a shekara ta 2025 Najeriya ta kasance ta 39 a ƙarfin soji daga cikin ƙasashe 145 na duniya.

Shekaru uku jere ƙarfin sojojin ƙasar na raguwa kamar yadda rahoton ƙungiyar ya nuna.

A duniya, Amurka ce ta farko a jadawalin inda ta shafe shekaru 18 jere tana kan matsayin.

Sauran ƙasashen da suke baza ƙarfin sojinsu sun haɗa da Rasha, da China, da Indiya, da kuma Koriya ta Kudu wadda ta kasance ƙasa ta biyar a duniya da take da ƙarfin soji.

Mun yi nazarin jadawalin da ƙungiyar ta fitar ga kuma jerin ƙasashe biyar da s**a fi ƙarfin soji a nahiyar Afirka.

Jami'an kashe gobara a Amurka na ƙoƙarin hana gobarar nan da ke ci gaba da ci a Los Angeles kaiwa Brentwood, ɗaya daga c...
12/01/2025

Jami'an kashe gobara a Amurka na ƙoƙarin hana gobarar nan da ke ci gaba da ci a Los Angeles kaiwa Brentwood, ɗaya daga cikin wurare masu muhimmanci a birnin.

Masana na hasashen dawowoar iska mai ƙarfin gaske, a dai dai lokacin da wutar ke ci gaba da karuwa.

Ya zuwa an tabbatar da mutuwar mutum 16, sannan ba a san inda kimanin 10 suke ba bayan shafe kwana biyar wutar na ci ganga-ganga.

Ɗaruruwan jirage na ta zubo ruwa da sinadaran kashe gobara daga sama, a ƙoƙarinsu kare rayuka da dukiyoyin jama'a.

Jirgin Sojin Nijeriya ya yi luguden wuta ga Askarawa da yan Sakai bisa kuskure a Yankin Maradun da ke jihar Zamfara.Lama...
12/01/2025

Jirgin Sojin Nijeriya ya yi luguden wuta ga Askarawa da yan Sakai bisa kuskure a Yankin Maradun da ke jihar Zamfara.

Lamarin wanda ya faru a yammacin jiya Asabar, zuwa yanzu dai wani rahoto ya ce aƙalla an samu gawa 16.

Al ummar Nigeria kuzo ga mafita
06/08/2024

Al ummar Nigeria kuzo ga mafita

Da dumi dumi Mai girma gwamnan jahar kaduna yasa dokar hana walwala a fadin jahar na tsawon 24 hours
05/08/2024

Da dumi dumi Mai girma gwamnan jahar kaduna yasa dokar hana walwala a fadin jahar na tsawon 24 hours

Zanga zanga tayi qamari a jahar kaduna a yayinda matasa suketa daga tutar rasha da nufin qasar ta kawo musu dauki
05/08/2024

Zanga zanga tayi qamari a jahar kaduna a yayinda matasa suketa daga tutar rasha da nufin qasar ta kawo musu dauki

Ya Allah katai maki matasa akan wanna tafiyar 🙏🙏🙏🙏
12/07/2024

Ya Allah katai maki matasa akan wanna tafiyar 🙏🙏🙏🙏

Address

Am2 Abuja Road Rigasa Kaduna
Kaduna

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when A A M MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category