DH Hausa Tv

DH Hausa Tv Mun buɗe wannan kafa ta DH Hausa TV domin kawo muku sahihan labarai masu inganci da suka shafi labaran duniya, wasanni da siyasa cikin gaskiya da ƙwarewa.

Ku kasance tare da mu domin samun ingantattun labarai a kowane lokaci. WhatsApp: 09030255151

Al'umma KU GUJI HASSADA, KU RINKA GASAR A AIKATA AIYUKAN ALKHAIRI GA MUTANE MALAM AHMAD IBRAHIM ILYAS (SAYYADI).Na'ibin ...
12/06/2026

Al'umma KU GUJI HASSADA, KU RINKA GASAR A AIKATA AIYUKAN ALKHAIRI GA MUTANE MALAM AHMAD IBRAHIM ILYAS (SAYYADI).

Na'ibin Limamin Masallacin Juma’a na Maulana Sheikh Ilyas bin Abdurrahman da ke Danhassan, Malam Ahmad Ibrahim Ilyas (Sayyadi), ya yi kira ga al’umma da su guji hassada tare da mayar da hankali wajen aikata ayyukan alkhairi da za su amfani addini da al’umma.
A cikin huɗubar Juma’a da ya gabatar, Malam Ahmad Ibrahim Ilyas ya yi bayani kan illolin hassada, yana mai cewa hassada na daga cikin manyan munanan ɗabi’u da ke haddasa gaba, ƙiyayya da rabuwar kai a tsakanin mutane.
Ya bayyana cewa hassada ita ce laifin farko da aka fara sabawa umarnin Allah Maɗaukakin Sarki da shi, lokacin da Allah Ya umarci mala’iku su yi sujada ga Annabi Adam (A.S). Ya ce duk mala’iku sun yi biyayya ga umarnin Allah, amma Shaidan ya ƙi saboda hassada da girman kai, lamarin da ya sa Allah Ya kore shi daga rahamarsa.
Malam Ahmad Ibrahim Ilyas ya jaddada cewa Musulunci addini ne da ke koyar da soyayya, haɗin kai da yi wa juna fatan alkhairi, don haka ya kamata Musulmi su nisanci hassada tare da tsarkake zukatansu daga duk wani abu da zai haifar da ƙiyayya.
A ƙarshe, ya yi kira ga al’umma da su guji hassada, su rungumi kyawawan ɗabi’u, tare da yin rigingimu ne kawai wajen aikata ayyukan alkhairi da neman yardar Allah Maɗaukakin Sarki.

Rahoto Malam Yusuf Adamu Ɗanhassan kofar yamma DH Hausa TV.

JAMI'IN AMURKA Trump Ba Zai Halarci Wasan Farko Na Amurka A Gasar Kofin Duniya Ba.Rahotanni daga Amurka sun tabbatar da ...
12/06/2026

JAMI'IN AMURKA Trump Ba Zai Halarci Wasan Farko Na Amurka A Gasar Kofin Duniya Ba.

Rahotanni daga Amurka sun tabbatar da cewa Shugaban Ƙasar Donald Trump ba zai halarci wasan farko na tawagar ƙasar Amurka da Paraguay a gasar cin kofin duniya ta FIFA 2026 ba.
Wani jami'i ya bayyana cewa rashin halartar shugaban ya samo asali ne daga cunkoson jadawalin ayyukansa da sauran muhimman al'amuran gwamnati da ke gabansa.
Duk da rashin zuwansa filin wasa, gwamnatin Amurka za ta samu wakilci daga wasu manyan jami'ai da za su halarci wasan domin nuna goyon baya ga tawagar ƙasar.
Ana sa ran wasan tsakanin Amurka da Paraguay zai ja hankalin dubban magoya baya, kasancewar shi ne wasan farko da Amurka za ta fara bugawa a gasar ta 2026.
Masoya ƙwallon ƙafa na ci gaba da sa ido kan yadda Amurka za ta fara tafiyarta a gasar, duk da cewa shugaban ƙasar ba zai kasance a filin wasan ba.

DH Hausa TV

IFTILA'I A KASUWAR SABON GARI Iska Mai Ƙarfi Ta Lalata Kayayyaki A Ƙofar Sani Abacha, Kano.Wata iska mai ƙarfi da ta biy...
12/06/2026

IFTILA'I A KASUWAR SABON GARI Iska Mai Ƙarfi Ta Lalata Kayayyaki A Ƙofar Sani Abacha, Kano.

Wata iska mai ƙarfi da ta biyo bayan ruwan sama ta yi barna a yankin Ƙofar Sani Abacha da ke Kasuwar Sabon Gari a Jihar Kano, inda ta lalata kayayyaki da dama tare da jawo asara ga ’yan kasuwa.
Rahotanni sun nuna cewa iskar ta taso cikin ƙarfi, lamarin da ya haddasa tarwatsewar kayayyaki da wasu rumfunan kasuwanci a yankin, wanda ya jefa ’yan kasuwa cikin damuwa da alhini.
Wasu daga cikin waɗanda abin ya shafa sun bayyana cewa sun yi asarar dukiya mai yawa sakamakon iftila'in, tare da kira ga hukumomi da masu hannu da shuni da su kawo musu ɗauki.
Ana ci gaba da tantance girman asarar da aka yi, yayin da al'umma ke addu'ar Allah Ya kare gaba da irin waɗannan iftila'ai.

DH Hausa TV .

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UNKwanaki 54 Kacal Da Bikinsa, Allah Ya Karɓi RayuwarsaAl'umma sun shiga jimami bayan r...
11/06/2026

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN
Kwanaki 54 Kacal Da Bikinsa, Allah Ya Karɓi Rayuwarsa

Al'umma sun shiga jimami bayan rasuwar wani matashi da Allah Ya yi wa rasuwa kwanaki 54 kacal bayan
gudanar da bikin aurensa, lamarin da ya girgiza iyalai, abokan arziki da maƙwabta.
Rasuwar tasa ta tuna wa mutane cewa rayuwa amana ce daga Allah, kuma babu wanda ya san lokacin da ajalinsa zai zo.
Muna addu'ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya jiƙansa da rahama, Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa, tare da bai wa iyalansa da matarsa haƙurin jure wannan babban rashi.
"Kowace rai mai ɗanɗanar mutuwa ce."
Allah Ya jikansa, Ya gafarta masa. Amin.

Rahoto Halifa Na Ma'aiki

DH Hausa TV.

BUƊE GASAR KOFIN DUNIYA Mexico Ta Doke Afirka Ta Kudu Da Ci 2-0.Tawagar ƙwallon ƙafa ta Mexico ta fara gasar cin kofin d...
11/06/2026

BUƊE GASAR KOFIN DUNIYA Mexico Ta Doke Afirka Ta Kudu Da Ci 2-0.

Tawagar ƙwallon ƙafa ta Mexico ta fara gasar cin kofin duniya ta FIFA 2026 da ƙafar dama bayan da ta lallasa Afirka ta Kudu da ci 2-0 a wasan buɗe gasar.
Mexico ta nuna ƙwarewa da ƙarfin gwiwa tun daga farkon wasan, inda Julián Quiñones da Raúl Jiménez s**a zura ƙwallayen da s**a tabbatar wa ƙasarsu nasara mai muhimmanci a wasan farko.
Wasan ya ɗauki hankalin duniya bayan da alkalin wasa ya fitar da katin ja guda uku, lamarin da ya sa wasan ya ƙara ɗaukar zafi da ce ce ku ce tsakanin 'yan wasa da magoya baya.
Nasarar ta bai wa Mexico muhimman maki uku a rukuninta, yayin da Afirka ta Kudu za ta koma shirye-shiryen wasanta na gaba domin farfaɗo da burinta na tsallakewa zuwa zagaye na gaba.
Masoya ƙwallon ƙafa sun yaba da irin wasan da Mexico ta nuna, yayin da ake sa ran gasar za ta ci gaba da samar da wasanni masu kayatarwa a kwanaki masu zuwa.

DH Hausa TV

MAJALISAR DATTAWA TA HANA JIHOHI KULLA SULHU DA ’YAN BINDIGA DA MASU GARKUWA DA MUTANE.Majalisar Dattawan Najeriya ta bu...
11/06/2026

MAJALISAR DATTAWA TA HANA JIHOHI KULLA SULHU DA ’YAN BINDIGA DA MASU GARKUWA DA MUTANE.

Majalisar Dattawan Najeriya ta bukaci gwamnatocin jihohi da su daina kulla yarjejeniyar sulhu da ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane, tana mai bayyana cewa irin waɗannan yarjejeniyoyi ba sa samar da zaman lafiya mai ɗorewa.
Sanatocin sun yi nuni da cewa sulhu da masu aikata laifuka kan ƙarfafa musu gwiwa tare da samar musu da kuɗaɗen da za su ci gaba da gudanar da ayyukansu na ta’addanci da garkuwa da mutane.
Majalisar ta kuma nuna damuwa kan yadda wasu shugabannin ƙungiyoyin ’yan bindiga ke amfani da shafukan sada zumunta, musamman TikTok, wajen nuna dukiya, makamai da kuma yaɗa saƙonnin da ke tayar da hankali.
A sakamakon haka, Majalisar Dattawa ta umarci Rundunar ’Yan Sandan Najeriya da hukumomin tsaro masu kula da harkokin yanar gizo da su gaggauta gano tare da kamo duk masu aikata irin waɗannan laifuka.
Wannan mataki na zuwa ne yayin da ake ci gaba da neman hanyoyin da za a kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro da ta’addanci a sassa daban-daban na ƙasar nan.
Me Kuke Tunani?
Shin hana yin sulhu da ’yan bindiga zai taimaka wajen kawo ƙarshen matsalar tsaro a Najeriya?

Rahoto Yusuf Ibrahim Abdullahi Ɗanhassan

DH Hausa TV

MAJALISAR WAKILAI TA AMINCE DA KUDIRIN KAFAR RUNDUNAR ’YAN SANDAN JIHOHI A NAJERIYA.A wani mataki da ake ganin zai kawo ...
11/06/2026

MAJALISAR WAKILAI TA AMINCE DA KUDIRIN KAFAR RUNDUNAR ’YAN SANDAN JIHOHI A NAJERIYA.

A wani mataki da ake ganin zai kawo gagarumin sauyi a tsarin tsaro na ƙasar nan, Majalisar Wakilai ta Tarayyar Najeriya ta amince da kudirin dokar kafa rundunar ’Yan Sandan Jihohi (State Police) bayan samun goyon bayan mafi yawan mambobinta.
Rahotanni sun nuna cewa ’yan majalisa 288 ne s**a kada kuri’ar amincewa da kudirin a zaman majalisar da aka gudanar ranar Alhamis.
Idan kudirin ya zama doka, zai bai wa gwamnonin jihohi damar naɗa kwamishinonin ’yan sanda tare da ba su umarni kan harkokin tsaro a matakin jihohinsu, domin ƙarfafa yaƙi da matsalolin tsaro da ke addabar sassa daban-daban na ƙasar.
Sai dai kafin a fara aiwatar da sabon tsarin, wajibi ne Majalisar Dattawa da kuma majalisun dokoki na jihohi su amince da kudirin kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanada.
Masana harkokin tsaro da siyasa na ci gaba da bayyana ra’ayoyi mabambanta kan wannan mataki, inda wasu ke ganin zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro, yayin da wasu ke nuna damuwa kan yiwuwar amfani da rundunar wajen manufofin siyasa.
Me Kuke Tunani?
Shin kafa ’yan sandan jihohi zai taimaka wajen magance matsalar tsaro a Najeriya?

Daga Yusuf Ibrahim Danhassan.

DH Hausa TV

GWAMNATIN NIJAR TA HARAMTA AUREN JINSI ƊAYA, TA TANADI HUKUNCI MAI TSANANI GA MASU LAIFI.Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta a...
11/06/2026

GWAMNATIN NIJAR TA HARAMTA AUREN JINSI ƊAYA, TA TANADI HUKUNCI MAI TSANANI GA MASU LAIFI.

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta amince da wani sabon kundin hukunta manyan laifuka wanda ya haramta hulɗa da auren jinsi ɗaya a karon farko, tare da tanadar hukunci mai tsauri ga duk wanda aka samu da laifin karya dokar.
Rahotanni sun bayyana cewa sabuwar dokar ta tanadi hukuncin daurin shekaru tsakanin biyar zuwa goma a gidan yari, tare da tara, ga duk wanda aka samu da laifin hulɗa tsakanin masu jinsi ɗaya.
Haka kuma, gwamnatin Nijar ta tanadi hukuncin daurin shekaru tsakanin 10 zuwa 20 a gidan yari ga duk wanda aka samu da laifin shiga ko gudanar da auren jinsi ɗaya.
Bugu da ƙari, dokar ta shafi duk wanda ya kafa, jagoranta, gudanarwa, tallafa wa ko shiga wata ƙungiya ko ƙawance da aka kafa domin masu hulɗar jinsi ɗaya, inda shi ma zai fuskanci hukunci mai tsanani idan aka same shi da laifi.
Masu sharhi na ganin cewa wannan mataki na daga cikin sauye-sauyen dokoki da gwamnatin Nijar ke aiwatarwa domin daidaita dokokin ƙasar da manufofinta na zamantakewa da al'adun al'ummarta.

Rahoto Yusuf Ibrahim Abdullahi Ɗanhassan.

DH Hausa TV

AN ZAƁI SABON SHUGABAN MARASA RINJAYE NA MAJALISAR WAKILAN NAJERIYA.An naɗa Fred Agbedi a matsayin sabon Shugaban Marasa...
11/06/2026

AN ZAƁI SABON SHUGABAN MARASA RINJAYE NA MAJALISAR WAKILAN NAJERIYA.

An naɗa Fred Agbedi a matsayin sabon Shugaban Marasa Rinjaye na Majalisar Wakilan Najeriya bayan murabus ɗin Kingsley Chinda. Agbedi ɗan majalisar ne mai wakiltar mazaɓar Sagbama/Ekeremor ta jihar Bayelsa kuma fitaccen jigo ne a jam’iyyar PDP.
Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya bayyana cewa mambobin ɓangaren marasa rinjaye sun cimma matsaya kan sababbin naɗe-naɗen shugabanninsu, lamarin da ya kawo ƙarshen takaddamar da ta dabaibaye zaɓen wanda zai maye gurbin tsohon shugaban marasa rinjayen.
Ana sa ran sabon shugabancin zai ƙara ƙarfafa haɗin kai tsakanin jam’iyyun adawa tare da inganta ayyukan majalisar a watanni masu zuwa.

Daga Yusuf Ibrahim Danhassan

.

Address

Danhassan Town Kura Local Government
Kano

Telephone

+19065386265

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DH Hausa Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to DH Hausa Tv:

Share