30/05/2026
Page 30
๐ฟ๐ฟ๐ฟKWATAR KAI๐ฟ๐ฟ๐ฟ
FATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA
PAGE 30
๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ
Ko yau kika fara cin karo da posting dina daure kiyi min comment, ku kuma pans dina a daure ayi share, kunga wad'an nan abubuwan guda biyu to sune ci gaba na, (comment da share) don Allah a daure ayi mani
๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ๐ฟ
Ya wani yatsine fuska ya ce "Toh! Zan dai bi umarnin ki.
Nan take taji ranta kuma ya sosu, wani tsananin kishin mujin ta ya dirar mata, hakanan ta danne zuciyar ta, domin kawai tabi shawarar da 'kawarta Farida ta bata, domin yanzun gani take tamkar wani d'aukar fansa ne za'ayi mata, don haka take so ta kauda kanta, ta barsu suyi soyayya, domin Hauwa'u taji irin yadda taji ita ma, lokacin da akayi mata tata kishiyar.
Suna nan zaune suna firar su, har saida aka kira sallar magariba, sannan ya tashi.
Ta ce "To ni dai sai Allah ya kaimu, daga nan kada ka dawo min d'aki, ka wuce d'akin matar ka."
Ya ce "To shikenan." Sukayi sallama ya tafi masallaci, ita kuma nan tad'au key ta rufe d'akin, kawai sai ji tayi hawaye ya ziraro mata, wani irin tsananin kishin mujin ta take, amma to ya zatayi?
Bai dawo gidan ba sai wajen 'karfe goma na dare, a falo ya samu wuri yayi zaman shi, ita kuwa Habiba tana cikin d'aki zaune, ga barci ya isheta, jira take ya tashi ya fita ta rufe d'akin, don ba tayi tunanin anan yake shirin kwana ba.
Ta sanya kayan barcin ta riga da wando, harta fara gyangyad'i a zaune, inta le'ko saita ganshi zaune ba shida niyyar tafiya, har wajen sha d'aya.
Ta fito ta ce "Yaya Nasser ni dai zan kwanta, in ka tashi fita kayi min magana in rufe d'akin."
Ba tare daya kalleta ba ya ce "Ai ba inda zani."
Sannan ya mi'ke tsaye ya nufo d'akin, ya samu gefen gado ya zauna, ita kuma tayi tsaye bakin kofar d'akin.
Zuwa can dai ya tashi ya shiga wanka, ita kuma ganin yana shirin kwana d'akin saita koma falo tayi kwanciyar ta.
Saida ya fito yasa kayan barcin shi, ya kwanta, daga kwance yake kwala mata kira
" Habiba! Habiba!! "
Ta ce "Na'am." Tare dayin saurin zuwa d'akin ta ce "Gani." Don tayi tunanin wani abu yake nema yasa ya kira ta.
Sai cewa yayi "Me k**eyi a falo?"
Ta ce "Kwantawa nayi."
Ya ce "Kwantawa kuma? Me k**e nufi, can zaki kwana?"
Tayi shiru
Ya ce "Da Allah ni bana son gidadanci, kizo mu kwanta nima ai barcin nake ji."
Duk saita daburce, ta rasa to me yake nufi, duk fad'in gadon ta rasa shin inama zata iya kwantawa?
Yaga dai ba tada niyyar kwantawa,saiya tashi zaune ya dawo gefen gadon, ya ziro da 'kafafun shi 'kasa, sannan ya kalleta ya ce "zo nan na ce!"
Ta tafo a hankali, kafin ta 'karaso yasa hannu ya fizgo ta jikin shi, ya kuma d'aure fuska ya ce "Cire hijabin, wa zaki kwanta mawa da lullu'bi!"
Ya kuma kafe ta da ido yana jiran ta cire.
A hankali take cire hijabin k**ar tanajin tsoro, har yaga nawa ya fizge mata hijabin da 'karfi, had'e da hular barcin dake kanta s**a cire.
Ya ce "Ba dai aure k**e so ba? Ke kika za'ba da kanki ba ni na za'bar maki ba, ke kika guji karatu kikace aure ko?"
Wannan maganar ta 'bata mata rai, watakan to laifi ne don na za'bi aure akan karatu, da har yake min gorin na'ki karatu nace aure?"
Bata san lokacin da hawaye s**a zubo mata ba.
Ya d'ora yatsan shi akan la'b'ban shi, yanayi mata kashedi da cewa "Kul! Kikayimin kuka! Abinda kika za'ba ne akayi maki! Don haka inma zakiyi kuka ki kuka da kanki."
Sannan ya d'auke ta Cak! Ya d'ora akan 'kafafun shi, yana rungume da ita.
Ita kuwa 'kara farashin kukan ta takeyi, tana 'kara 'boye idon ta akan 'kirjin shi, shi kuwa yana fad'in "Yau sai naga idon mara kunya mai son Aure."
Tana 'kara 'boye fuskar ta, shi kuma yana 'ko'karin dole sai yaga fuskar.
Ya ce "Ki tsaya mana, ki daina yimin kuka, ko na bige ki ne? Wani abu nayi maki da zakiyimin kuka? Karki manta abinda k**e so ne fa, yaya zaki 'bata min riga da hawaye! In kika 'bata ke zaki wanke ta."
Dai-dai nan ta bud'e idanun ta ta kalle shi, ta ce "E naji zan wanke."
Sai yayi dariya ya ce "Laaaa! Naga idon ki, ashe zaki iya magana, me kikaci yau?"
Ta ce "Shinkafa na dafa."
Ya ce "Shine baki bani ba."
Ta ce "Dama dai-dai tawa kawai nayi."
Ya ce "To shikenan daga yanzun a ri'kayi da ni.
Sannan ya ce " Habiba kin shirya kwana dani yau?"
Tayi shiru,
Ya ce " Don ma na tambaye ki, wallahi tausayin ki nake, kinada 'kananan shekaru, anya zaki iya jure mani? "
Ita dai ta kasa cewa komai, in banda kanta data d'ora akan kafad'ar shi, tana jin shi, don ya'ki bata damar ta sauka daga jikin shi.