Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa

Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa, Fatima Dahiru funtuwa@gmail. com, Lagos.

Sunana Fatima Dahiru Funtuwa, an haifeni a 1997, tun tasowata inada sha'awar rubutu, ina godiya ga Allah da yayini a marubuciya, Allah ya 'kara mani fasaha da juriya tare da sauran marubuta, ya kuma cika mana burinmu na Al-kairi

Page      30๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ                 FATIMA  DAHIRU FUNTUWA  BINTAPAGE    30๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ   Ko yau kika fara cin ...
30/05/2026

Page 30

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ




FATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA

PAGE 30

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ

Ko yau kika fara cin karo da posting dina daure kiyi min comment, ku kuma pans dina a daure ayi share, kunga wad'an nan abubuwan guda biyu to sune ci gaba na, (comment da share) don Allah a daure ayi mani
๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ

Ya wani yatsine fuska ya ce "Toh! Zan dai bi umarnin ki.

Nan take taji ranta kuma ya sosu, wani tsananin kishin mujin ta ya dirar mata, hakanan ta danne zuciyar ta, domin kawai tabi shawarar da 'kawarta Farida ta bata, domin yanzun gani take tamkar wani d'aukar fansa ne za'ayi mata, don haka take so ta kauda kanta, ta barsu suyi soyayya, domin Hauwa'u taji irin yadda taji ita ma, lokacin da akayi mata tata kishiyar.

Suna nan zaune suna firar su, har saida aka kira sallar magariba, sannan ya tashi.

Ta ce "To ni dai sai Allah ya kaimu, daga nan kada ka dawo min d'aki, ka wuce d'akin matar ka."

Ya ce "To shikenan." Sukayi sallama ya tafi masallaci, ita kuma nan tad'au key ta rufe d'akin, kawai sai ji tayi hawaye ya ziraro mata, wani irin tsananin kishin mujin ta take, amma to ya zatayi?

Bai dawo gidan ba sai wajen 'karfe goma na dare, a falo ya samu wuri yayi zaman shi, ita kuwa Habiba tana cikin d'aki zaune, ga barci ya isheta, jira take ya tashi ya fita ta rufe d'akin, don ba tayi tunanin anan yake shirin kwana ba.

Ta sanya kayan barcin ta riga da wando, harta fara gyangyad'i a zaune, inta le'ko saita ganshi zaune ba shida niyyar tafiya, har wajen sha d'aya.

Ta fito ta ce "Yaya Nasser ni dai zan kwanta, in ka tashi fita kayi min magana in rufe d'akin."

Ba tare daya kalleta ba ya ce "Ai ba inda zani."

Sannan ya mi'ke tsaye ya nufo d'akin, ya samu gefen gado ya zauna, ita kuma tayi tsaye bakin kofar d'akin.

Zuwa can dai ya tashi ya shiga wanka, ita kuma ganin yana shirin kwana d'akin saita koma falo tayi kwanciyar ta.

Saida ya fito yasa kayan barcin shi, ya kwanta, daga kwance yake kwala mata kira

" Habiba! Habiba!! "

Ta ce "Na'am." Tare dayin saurin zuwa d'akin ta ce "Gani." Don tayi tunanin wani abu yake nema yasa ya kira ta.

Sai cewa yayi "Me k**eyi a falo?"

Ta ce "Kwantawa nayi."

Ya ce "Kwantawa kuma? Me k**e nufi, can zaki kwana?"

Tayi shiru

Ya ce "Da Allah ni bana son gidadanci, kizo mu kwanta nima ai barcin nake ji."

Duk saita daburce, ta rasa to me yake nufi, duk fad'in gadon ta rasa shin inama zata iya kwantawa?

Yaga dai ba tada niyyar kwantawa,saiya tashi zaune ya dawo gefen gadon, ya ziro da 'kafafun shi 'kasa, sannan ya kalleta ya ce "zo nan na ce!"

Ta tafo a hankali, kafin ta 'karaso yasa hannu ya fizgo ta jikin shi, ya kuma d'aure fuska ya ce "Cire hijabin, wa zaki kwanta mawa da lullu'bi!"

Ya kuma kafe ta da ido yana jiran ta cire.

A hankali take cire hijabin k**ar tanajin tsoro, har yaga nawa ya fizge mata hijabin da 'karfi, had'e da hular barcin dake kanta s**a cire.

Ya ce "Ba dai aure k**e so ba? Ke kika za'ba da kanki ba ni na za'bar maki ba, ke kika guji karatu kikace aure ko?"

Wannan maganar ta 'bata mata rai, watakan to laifi ne don na za'bi aure akan karatu, da har yake min gorin na'ki karatu nace aure?"

Bata san lokacin da hawaye s**a zubo mata ba.

Ya d'ora yatsan shi akan la'b'ban shi, yanayi mata kashedi da cewa "Kul! Kikayimin kuka! Abinda kika za'ba ne akayi maki! Don haka inma zakiyi kuka ki kuka da kanki."

Sannan ya d'auke ta Cak! Ya d'ora akan 'kafafun shi, yana rungume da ita.

Ita kuwa 'kara farashin kukan ta takeyi, tana 'kara 'boye idon ta akan 'kirjin shi, shi kuwa yana fad'in "Yau sai naga idon mara kunya mai son Aure."

Tana 'kara 'boye fuskar ta, shi kuma yana 'ko'karin dole sai yaga fuskar.

Ya ce "Ki tsaya mana, ki daina yimin kuka, ko na bige ki ne? Wani abu nayi maki da zakiyimin kuka? Karki manta abinda k**e so ne fa, yaya zaki 'bata min riga da hawaye! In kika 'bata ke zaki wanke ta."

Dai-dai nan ta bud'e idanun ta ta kalle shi, ta ce "E naji zan wanke."

Sai yayi dariya ya ce "Laaaa! Naga idon ki, ashe zaki iya magana, me kikaci yau?"

Ta ce "Shinkafa na dafa."

Ya ce "Shine baki bani ba."

Ta ce "Dama dai-dai tawa kawai nayi."

Ya ce "To shikenan daga yanzun a ri'kayi da ni.

Sannan ya ce " Habiba kin shirya kwana dani yau?"

Tayi shiru,

Ya ce " Don ma na tambaye ki, wallahi tausayin ki nake, kinada 'kananan shekaru, anya zaki iya jure mani? "

Ita dai ta kasa cewa komai, in banda kanta data d'ora akan kafad'ar shi, tana jin shi, don ya'ki bata damar ta sauka daga jikin shi.

Page      29๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ                 NAFATIMA  DAHIRU FUNTUWA  BINTAPAGE    29๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ Kuci gaba da  'karfaf...
28/05/2026

Page 29

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ


NA

FATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA

PAGE 29

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ

Kuci gaba da 'karfafamin gwiwa da comment d'in ku, ni kuma inci gaba da zazzage maku littafan Hausa novels.
Ko yau kika fara cin karo da posting dina daure kiyi mani comments da liking, hakan yakan sanyani farin ciki
๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ

Aini muji na idan yayi mani kishiya, kuma sai bai 'kara ta uku ba, to ni d'in ce bai iya zama dani ni kad'ai, inko ya 'kara na san halin shi ne aure-aure, ni innice uwar gida, idan akayo min ta biyu, to gara ayomin ta ukun, don ita ma tasan ba daga ita an rufe kofa ba.

Don haka ki 'kara k**a mujin ki, ki dage mai da soyayya irin wadda bakiyi mashi bama a baya, sannan saiki koma gefe kiga yadda kishiyar ki zatayi, ina 'kara baki wannan shawarar, sai anjima, naji shigowar muji na, ma 'karasa maganar anji ma, ko kuma sai nazo ganin amarya. "

Ta ce " To shikenan sai anjima. "

Sannan ta ajiye wayar ta fara tunanin had'a abinda zatayi breakfast da shi.

Misalin 'karfe shidda na yamma, Nasser na zaune tare da Suwaiba take tambayar shi "Wai da gaske ne Hauwa'u saita 'kara sati a tafiyar nan tata?"

Nasser ya ce "E haka take fad'amin d'azun da mukayi waya, wai Kawun ta ya ce ta bari ta 'kara sati."

Suwaiba ranta a 'bace ta ce "To kai me kace?"

Ya ce "To ya zance mata? Ce mata kawai nayi Allah ya kaimu."

Suwaiba ta ce "Gaskiya ni na tsani irin wannan! Ace kai bakada iko da matar ka sai su."

Ya ce "To ya zanyi? Kin san su masu kud'in nan, in kana tare dasu kawai saidai kaita ha'kuri, ka auri 'yar su amma har lokacin su keda iko da ita, ba halin kuma kayi magana, su nuna ai su sun isa, don haka kawai ni ido nake sa masu."

Suwaiba ta ce "Ta'b-d'i-jan! Allah ya kyauta."

A zuciyar ta kuwa ta 'kosa Hauwa'u ta dawo ta tarar da angon ta ya 'kara aure, taga yadda zasuyi, shiyasa taji 'karin satin nan da Hauwa'u zatayi duk bataji dad'in shi ba.

Sai ta ce "To Amaryar ka fa? Kaga ko jiya ya k**ata ace d'akin ta kake."

Ya ce "Don Allah Suwaiba ki daina yimin wannan maganar, ni ba ta ita nake ba, na fad'a maki, ni auren nan umarni nabi, ba wai ina son Auren bane, don haka ki daina yimin maganar ta, yauma anan wurin ki zan kwana."

Sai tayi jimm! Tana tunnin maganar Farida

***********
Ai ba ke akayima kishiya ba, Hauwa'u akayi mawa, aike an riga anyi maki taki, ki bari Hauwa'u ta dawo kiga yadda zasu kwashe
************
"Lallai kam gara in bashi dama yayi soyayya da wannan yarinyar, domin itama Hauwa'u ta d'and'ani irin zafin data haddasa mani, domin kuwa ni Habiba ba kishiya ta bace."

Sannan ta d'ago kai ta kalle shi, ta ce "Ka kasa bata kwanaki bakwai d'in ta na amarci."

Ya ce "Suwaiba wannan fa ba ruwan ki, na gaya maki Habiba ba za'bi na bace, ba na jin son ta a cikin zuciya ta."

Ta ce "Kaga Nasser kaji tsoron Allah."

Ta fad'a tana kallon fuskar shi, had'i da yi mai fari da idanun ta.

Ya ce "Koh? Tare da sa d'an yatsan shi ya lakuci kumatun ta..

Ya ce "Na gode da tunatarwar da kikayi mani, amma fa ki sani, nafi son ki."

Tayi dariya tare da fad'in "Naji dai kana cewa haka."

Ya ce "Baki yarda ba kenan? Ko sai na rantse maki?"

Ta ce "Na yarda, amma yanzun ka dai-daita da Amaryar ka, ka bata kwanakin ta na amarci."

Ya wani yatsine fuska ya ce "Toh! Zan dai bi umarnin ki.

Page      28๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ                 NAFATIMA  DAHIRU FUNTUWA  BINTAPAGE    28Kina/kana karanta wannanittafin ko...
27/05/2026

Page 28

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ


NA

FATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA

PAGE 28

Kina/kana karanta wannanittafin ko kin/ka bari an barki a baya? To ko daga wannan page dinne waibar Allah fara karantawa,
๐Ÿ‘‡
๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ

"Yaya Nasser banyi tunanin zakayimin haka ba, ashe rashin son da kake yimin har ya kai haka, Wane iri zaman aure zanyi a gidan ka? Wayyo Allah Yaya Nasser kada ka cutar dani, wallahi ina son ka๐Ÿ˜ญ"

Haka taita sambatu ita kad'ai, da 'kyar barci ya d'auke ta.

Sai can farkin barci ta tashi tayi sallar nafila ta du'kufa Addu'a akan wannan aure nata.

***** Koda Nasser ya bud'e 'bagaren Suwaiba ya shiga, yadda ya barta haka ya same ta, ran nan nata a 'bace, tana zaune bakin gado.

Tana ganin shi ta mi'ke tsaye, tana fad'in

"Kana tunanin don ka rufe ni a d'aki shine zai hana in tafi gidan mu!? Nasser komai dare sai naje gida yau, wannan ai zalunci ne da cuta! A bugi mutum a hana shi kuka! Ai kai kanka kasan bakayi min adakci ba, to dom me zaka hana in tafi gidan mu?"

Ta d'auko gyalen ta ya fizge, yana fad'in "Suwaiba don Allah kiyi ha'kuri ki saurare ni mana, ya sha gaban ta ya mamu'ke ta da 'karfi, tana kici-kicin kwacewa.

Ya ce " Suwaiba ya k**ata ace a wannan halin da nake ciki, ki saurare ni, ki kar'bi uzuri na, ina tabbatar maki da cewa 'karin auren nan ba ra'ayi na bane, ni zamma iya ce maki bana son yarinyar nan, muje don Allah ki zauna."

Da 'kyar ya samu ya lallashe ta, sannan ta nunfasa, yana ri'ke da hannun ta, s**a zauna gefen gado.

Ta kalle shi ta ce " Me kake so kace mani? Dama can ba wani bikin Ibrahim da zaka, kana d'auke da shirin 'kara aure ne! "

Ya ce " Suwaiba wai ya za'ayi inta yi maki rantsuwa, amma kina d'aukar magana ta ba gaskiya ba, ya k**ata ace kin tsada tunanin ki wuri d'aya, wannan Al-amari da yake fatuwa a gare ni kad'ai ya isheki abin Al-fahari.

Duk cikin mata na da kuke ku uku, ke ce wadda na gani da kaina na ce ina son ki, ke kanki kin sani, ita ma wannan Habibar umarnin mahaifiya ta na bi, ba ra'ayi na bane, shin wannan kad'ai bai isheki abinda zakiyi fariya da shi ba?

Suwaiba duk cikin mata na nafi son ki, kema kuma kin san da haka, to don miye 'karin aure na zai tada maki hankali? Duk wata mace da zata shigo gidan nan bayan ki take, ba wai ina nufin bayan ki a shigowa gidan nan ba, a'a ba yanki a soyayya ma, duk wadda zan so bayan ki take, kada ki yarda wata 'ya mace ta 'kara tada maki hankali domin kuwa kafin ita ke na fara so, kuma ba zan ta'ba son wata mace fiye da yadda nake son ki ba.

Suwaiba ina son ki. " ya fad'a, dai-dai lokacin da ya 'kara janyo ta jikin shi ya rungume, yanayi mata wasa da hannayen shi a gadon baya.

" Suwaiba nayi missing dinki da yawa fa, soyayyar ki tana wahalar da ni idan nayi nesa dake, shine kuma na dawo kema zaki gasa ni?"

Ya canza muryar cikin sigar shagwa'ba, "Gaskiya ba zan yarda ba, kawai sai ki tafi gidan ku ki barni, na dawo ina d'okin inzo in kwanta da wannan daddad'an jikin naki."

Ya shafo gashin kanta, tare da 'kara kai hancin shi a kanta, yana sha'kar 'kamshin da yake cikin gashin kanta, yana yamutsa gashin da hannun shi, a hankali ya sauko da fuskar shi yana tafe yana yi mata kiss har zuwa 'kirjin ta.

Yana kai hannun shi a kan nonon ta ya d'an matsa ya tsotsi kan nonon.

Bata san lokacin data kaimai runguma ba, gaba d'aya yana neman ya dabur tata lokaci guda.

Dole ta mi'ka wuya ita ma taci gaba da aika mai sa'konni kala-kala a cikin jikin shi.

(Mai karatu ni dai nace Allah ya had'a ko wacce da muji na kwarai, wanda ya iya soyayya)

Washe gari misalin 'karfe tara na safe, Suwaiba ta tashi daga barci, a lokacin kuwa Nasser ya dad'e da tafiya wurin aiki, ko sallama baiyi ma Habiba ba ya wuce yayi tafiyar shi.

Wayar ta ta fara lalubowa ta kira number 'kawar ta Farida, tana bata labarin abinda ya faru.

"Wai Nasser ne ya 'kara aure."

Farida ta ce "Aure kuma?"

Suwaiba ta ce "Aure kuwa, daga zuwa bikin Abokin shi wai shima sai gashi da Amarya, wallahi farida jiya banyi niyyar kwana gidan nan ba, rai na ya 'baci sosai, nayi niyyar inyi yaji, shi ya bi duk hanyar da zaibi ya hana ni."

Farida ta ce "Yaji kuma? A-kul-d'in-ki! Karki kuskura, miye naki a ciki? Ai ba ke aka yima kishiya ba, Hauwa'u aka yima kishiya, ai ke an riga anyi maki, ki bari Hauwa'u ta dawo kiga yadda zasu kwashe, ba abinda ya dame ki, kishiya ba taki bace ta Hauwa'u ce, aike gara da akayi, itama taji abinda kikaji, ki k**a mujin ki gam! Ki ri'ke, mujin ki fa yana son ki Suwaiba.

Don haka kina jina ko? Kishiya ba taki bace ta Hauwa'u ce, tunda ke anyi maki ai gara itama ayi mata, taji abinda kikaji, don ta daina tunanin ko daga ita an rufe 'kofa, ta d'auka anfi son ta, to itama gashinan! Ki koma gefe kiyi kallo.

Aini muji na idan yayi mani kishiya, kuma sai bai 'kara ta uku ba, to ni d'in ce bai iya zama dani ni kad'ai, inko ya 'kara na san halin shi ne aure-aur

27/05/2026

Don soyayyar ka da Annabin rahama SAW kada ka wuce baka yima d'a na Addu'a ba, a cikin wannan rana mai d'inbin falala.

Allah sarki rayuwa, wata Tara kenan rabon mu da kai Abdul-baseer๐Ÿ˜ญ ya sabunta rahama a gare ka.

Page      27๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ                 NAFATIMA  DAHIRU FUNTUWA  BINTAPAGE    27๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKuci gaba da  'karfafa...
26/05/2026

Page 27

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ


NA

FATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA

PAGE 27

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ
Kuci gaba da 'karfafamin gwiwa da comment din ku, ni kuma inci gaba da zazzage maku littafan Hausa novels.
Ko yau kika fara cin karo da Posting d'ina, daure kiyi comment da liking hakan yakan sanya ni farin ciki
๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ

Saida ta natsu, Sannan ya ce "Suwaiba, a matsayin ki na musulma, wadda tayi imani da 'kaddara mai kyau da akasin ta, ina fatan zaki rungumi ko wane irin Al-amari ne ya tunkare ki a yanzun, kiyi imani da cewa Allah ne ya hukunta hakan saita faru gare mu."

Ta ce "Ka fito fili ka sanar dani cewa kai ka siya mata motar!"

Ya ce "Bani na sayi motar ba, wani Al-amari ne ya faru gare mu, wanda ni bansan yadda zaki d'auke shi ba.

Umarnin mahaifiya ta nabi, kawai domin in faranta mata rai, Aure tace in 'kara kuma na 'kara, a yanzun haka da matar na tafo."

A razane ta ce "Aure Nasser!? Duka yaushe ma kayi auren da har zaka 'kara auro wata? Kaih! Haba! Wasa dai kake."

Ya ce "Suwaiba wallahi bada wasa nake ba, da gaske nakeyi, amaryar ma tana waje cikin mota na baro ta, domin in sanar da ke."

Ta ce "Nasser tayaya za'ayi kazo min da wannan maganar sannan kace hankali na ba zai tashi ba! Wai Nasser me kake so ka zama ne? Shikenan kai ko wace kucakar mace ma burge ka take, ka auro ta ka kawo ta cikin gidan ka? Kai ko wace mace tayi maka! Kai kuma irin naka ci gaban kenan? "

Ya ce " Suwaiba ina so ki fahimce ni, ba ra'ayi na bane..."

Tayi sauri cewa " Ohoo! Ma'kala maka ita akayi kenan? Kace min auren dole akayi maka! Nasser ka daina yimin wannan 'boye-'boyen mata hud'u dama kake so ka had'a a cikin gidan ka, to wallahi ba za'ayi wannan kwamacalar da ni ba! Muna a mu biyun ma ka kasayin adalci a tsakanin mu, shine har kake hangen wata! Yaya ka iya damu?"

Ya ce "Don Allah Suwaiba ki saurare ni kiji."

"Me zan saurara inji bayan ka riga ka gama aikata abinda kake so! Ni ba abinda zaka gaya min yanzun."

Fuuuuh! Tayi cikin d'aki da sauri tana fad'in "Saidai ka zauna da mata biyu ni bazan iya ba! Gidan mu zan tafi."

Nan da nan fa ya daburce, ganin abinda take shirin yi, ya rasa mema zaiyi ganin bai bari ta tafi gidan su ba, domin ya lura da yadda ranta ya 'baci lallai gidan nasu zata tafi.

Don haka cikin sauri ya bita d'akin, cikin sa'a kuwa yaga d'an makullin shashin ta, ya d'auko yayo waje da sauri ya rufe ta a ciki, sannan ya koma wajen Habiba, da take cikin mota kwance barci ya d'auke ta.

Yana zuwa bubbuga marfin motar yayi tare da fad'in "Habiba!"

Firgigit! Ta farka ta ce "Na'am."

Ya ce "Taso muje."

Ta fito daga motar sannan ya rufe, yayi gaba tana biye da shi.

'Bangaren Hauwa u ya nufa da ita, ya bud'e mata d'ayan bedroom din, ya ce "Shiga ciki akwai duk abinda k**e bu'kata a ciki."

Shi kuma ya dawo falo ya zauna tare dayin tagumi da hannayen shi guda biyu, yana tunanin wannan matsala data tunkaro shi, duk da dai yayi imani da cewa komai mu'kaddari ne daga Allah, tunanin shi a yanzu shine yaya zaiyi ya shawo kan Suwaiba? Kafin kuma Hauwa'u ta dawo.

Duk da dai yana ganin k**ar Hauwa'u zatafi sau'kin kai da fahimta.

Ta ke ya sauya tunanin shi da cewa k**arni ace inada mata uku! Yayi wuri da yawa, a 'kananan shekaru na haka.

Ya dad'e zaune yana tunanin yadda zai shawo kan Uwargidan shi Suwaiba, domin ya lura tayi fushi sosai, tana iya tafiya gidan su, shi kuma baya son irin wannan matsalar ta fara faruwa a gidan shi, ace ya kaiga matsayin da zai 'bata ma mace rai har tayi fushi ta tafi gidan su, shin yanzun da wad'anne kalamai zanyi amfani dasu domin shawo kanta? Ganin bata aikata abinda tayi niyyaba, ya dad'e yana wannan nazari.

Misalin 'karfe Tara na dare ya shigo wurin Habiba, zaune ya same ta tayi shirin kwanciya barci, tana sanye da kayan barci masu kyau sosai, duk da ba wata kwalliya tayi sosai ba.

"Sannu da dawowa Yaya Nasser." Ta fad'a tare da 'karasowa inda yake, ta kar'bi jakar dake hannun shi.

Ba tare daya amsa ba yaci gaba da cewa "In kin gama ki rufe d'akin ki zan shiga wurin Suwaiba."

Mamaki ne ya k**ata sosai, hakan yasa ta 'kara kallon shi, k**ar zatayi magana, sai kuma ta fasa, a zuciyar ta tana tunanin wannan wane irin aure ne? Ace har zamu kwana uku da muji na ko hannu na bai ta'ba k**awa ba, watakan ni bama tani yake ba kenan? Ta matar shi yake, shikenan yana nufin kwana bakwai d'in amarcin ma ya haramta mani su kenan?

Bata san lokacin da bakin ta ya su'buce ba ta ce "Zuwa zakayi ka dawo ko?"

Koda ta kalli inda yake ba kowa, ashe ya dad'e da fita d'akin ๐Ÿ˜‚ kawai saita fashe da kuka tana fad'in

"Yaya Nasser banyi tunanin zakayimin haka ba, ashe rashin son da kake yimin har ya kai haka, Wane iri zaman aure zanyi a gidan ka? Wayyo Allah Yaya Nasser kada ka cutar dani, wallahi ina son ka๐Ÿ˜ญ"

Haka taita sambatu ita kad'ai, da 'kyar barci ya d'auke ta.

Page      26๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ                 NAFATIMA  DAHIRU FUNTUWA  BINTAPAGE    26๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKuci gaba da  'karfafa...
25/05/2026

Page 26

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ


NA

FATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA

PAGE 26

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ
Kuci gaba da 'karfafamin gwiwa da comment din ku, ni kuma inci gaba da zazzage maku littafan Hausa novels.
Ko yau kika fara cin karo da Posting d'ina, daure kiyi comment da liking hakan yakan sanya ni farin ciki
๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ

Ya gaji dai da halin da suke ciki, ya ce "Wai lafiya? Naga kina ta kallo na, ko ruwa baki kawo min ba

Ta ce "Humf! Hakane fa, bari in kawo maka."

Ta tashi amma hankalin ta da idanun ta suna kanshi, duk da shima ita d'in yake kallo, ta d'auko ruwan ta kawo mashi, ta ce "Kasha sannan muyi magana."

Rass! Yaji gaban shi ya fadi, hakanan dai ya daure ya sha ruwan, tasa hannu ta kar'bi kofin daga hannu shi, har lokacin idanun ta na kanshi, ta girgiza kai tare da fad'in "Namiji kenan."

Jikin shi yayi sanyi sosai a wannan lokacin, cikin taushin murya ya ce "Wai ni yau wane irin kallo ne k**e yi mani ne?"

Ta ce "Ai kaima ka sani, ka kuma san ma'anar shi, Nasser yaushe ka zama haka? Yau she ne ka daina so na? Don Allah idan ka daina so na ka sanar dani, ba wai ka ri'ka cusa min ba'kin ciki a rayuwa ta ba, kana zagayewa kana cin amana ta, ko ka d'auka cewa ba zan sani ba?"

Cikin rawar murya da nuna alamar rashin gaskiya ya ce " Wallahi Suwaiba nima ba laifi na bane, ba yadda na iya, umarnin mahaifiya ta ne kawai nabi. "

Tayi saurin 'kara kallon shi a firgice, ta ce " Mahaifiyar ka kuma? A ina ma ta santa? Da har zata baka umarnin ka siya mata mota.?"

Ta d'aga mashi hannu a lokacin da yake so yayi magana, ta ce "Kaga Nasser! Don ka tashi cin amana ta shine zaka fake da umma ce ta saka? Ni naga bata ma ta'ba ganin Hauwa'un nan ba! Amma taya za'ayi tasa ka sai mata mota?"

Cikin rikicewa da rashin fahimtar inda kalaman ta s**a nufa ya ce "Wace irin mota kuma? Waye na saima mota?"

Ta mi'ke tsaye tana fad'in "Nasser karka maida ni sakarya mana! Al-halin ni ban dace da mota ba! Hauwa'u ce ta dace da ita! Shine nan kun had'a baki, kunyi tafiya tare, ka siya mata mota, ka kira ni kana wani fad'a min kawun ta ne ya siye ta, saboda ka d'auke ni ba nida tunani!!"

Yasa hannu ya cire hular shi ya ajiye bisa kujera, gaba d'aya tunanin shi ma yana neman ya rikice, ga wani zafi da yake jin yana wani tsatstsafo mashi

Cikin dusashewar murya ya ce "Innalillahi wa innailaihirrajiun, wannan wace irin masifa ce? Suwaiba ya za'ayi kiyi tunanin cewar zan iya siyama Hauwa'u mota ke ban sai maki ba?"

Tayi saurin cewa "Gashi kuwa kayi! Tunda gashi ka sai mata! Duk wata dubara da wani kwane-kwane da zakayi min nacewar ba kai ka sayi motar nan ba ba zan yarda ba! Saboda ita yanzun ita amarya ce, ita kake ji da ita, ni kuma ka gama yayi na! A ganin ka haka d'in da kayi adalci ne? Kana ganin ka siyo zaman lafiya ka kawo cikin gidan ka? Dama na dad'e da sanin cewar idan gida ya gyaru daga irin adalcin mai gidan ne! Idan kuma ya 'baci, to mai gidan ne da kanshi ya hargitsa shi! Wallahi Nasser ka d'auko abinda zaka hargitsa gidan ka da kanka! Domin dai ba zan iya sa ido ina kallon wannan wula'kancin ba!!"

Ya d'ago idanun shi ya kalleta, da har sun kad'a jajur, hawaye sun cika idanun, ya ce "Suwaiba ya zakice na saima Hauwa'u mota? Wallahi ba ni na siye ta ba, yama zakiyimin.................

Ta katse shi da cewa "Yama za'ayi in yarda? Idan har Kawun ta ne zai sai mata mota, meyasa bai tashi sai mata ba sai a irin wannan lokacin? Lokacin da ku kayi tafiya tare da ita!"

Saita rage 'karfin sautin muryar ta ta ce "Nasser ka daina yimin 'boye-'boye, ka fito ka nunamin cewa ka canza daga yadda na sanka! Ka sauya hali daga Nasser din dana sani a baya, kada kayi tunanin cewa zan ha'kura, wallahi ba zan ha'kura ba! Daga kai har Hauwa'u jiranku nake." Sannan ta saurara.

Shi kuma ya samu damar da yace mata "Suwaiba na ta'ba yi maki 'karya?"

Ta ce "Aa, amma yanzun gashi kana shirin yi, saboda ka wanke kanka daga cin amanata da kayi."

Ya ce "Yanzun ma ba 'karyer nake yi maki ba, kuma ko 'karya nake yi maki kinsan ba zanyi maki rantsuwa a kanta ba, Suwaiba don Allah ki yarda dani."

Dai-dai nan hawayen da suke narke cikin idanun shi s**a ziraro.

Ya ce "Suwaiba tunda muka rabu da Hauwa'u a gida, bamu kara had'uwa ba, sai dai a waya, Don Allah๐Ÿ™Don Allah๐Ÿ™Don Allah Suwaiba ki yarda dani๐Ÿ˜ญ Wallahi ban saima Hauwa'u mota ba, nima haka ta fad'a min cewa kawun ta ya siya mata, bama yadda za'ayi in sai mata mota, ke ban sai maki ba. "

Humf! Tayi ajiyar numfashi, ta ce " To shikenan, inma dai mutum yayi da kyau ya sani, inma ya 'bata yafi kowa sani, idan ka 'boye min ai bazaka 'boye ma Allah ba. "

Ta gama gungunan ta, yana dai sauraron ta, domin shi bai mayi zaton wannan maganar ce a bakin ta ba, iya tunanin shi ya d'auka cewar taji zancen 'karin auren shi ne.

Saida ta natsu, Sannan ya ce "Suwaiba, a matsayin ki na musulma, wadda tayi imani da '

Page      25๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ                 NAFATIMA  DAHIRU FUNTUWA  BINTAPAGE    25๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKuci gaba da  'karfafa...
23/05/2026

Page 25

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ


NA

FATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA

PAGE 25

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ
Kuci gaba da 'karfafamin gwiwa da comment din ku, ni kuma inci gaba da zazzage maku littafan Hausa novels.
Ko yau kika fara cin karo da Posting d'ina, daure kiyi comment da liking hakan yakan sanya ni farin ciki
๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ

Domin kuwa ya tabbatar dole ne yayi ma matan shi babban laifn da shi kanshi bai san yadda zai wanke kanshi daga gare su ba.

Suna isa Abuja ya tsaya wurin siyar da gasassun kaji, ya sai mata guda d'aya, sannan ya sai mata madara da lemo.

Ya ce "Sai kuma me k**e so in sai maki? Tunda naga kin gama kukan sai kici abinci."

Ya fad'a ba tare daya kalle ta ba, kuma fuskar shi ba cikin fara'a ba.

Ta ce "Ba komai."

Dai-dai sanda take 'kara bin garin da kallo ta glass d'in motar.

Ya mi'ka mata ya ce "Gashinan."

Ta sa hannu ta kar'ba tare da kallon fuskar shi, wadda har lokacin babu wata fara'a a tare da shi.

Lokaci d'aya kuma abinda ya faru tsakanin ta dashi daren farko na amarcin ta ya dawo mata cikin kwakwalwarta, tana jinshi tamkar yanzun ne yake faruwa.

***** ***** ***** ***** ******

Tana zaune ne cikin tsakiyar gadon d'akin su, (wanda ya kar'ba tsawon kwanaki biyun da zasuyi kafin su wuce Abuja)

Ya shigo d'akin, ya daiyi sallama, sannan ya fad'a wanka, bayan ya fito kuwa ko ta kanta baibi ba, ya hau shirya jikin shi, saida ya gama tsaf! Sannan ya nemi wurin kwanciya, a lokacin ne ya d'ago ido ya kalle ta.

Ya ce "Kindai ci abinci ko?"

Har lokacin fuskar ta a rufe take, ta kasa amsa mai tambayar da yayi mata, don a lokacin ita a tsorace ma take.

Da yaji tayi shiru ya ce "Magana fa nake yi maki Habiba."

A hankali ta girgiza kanta, duk da dai ya gani.

Dole ce tasa ta fad'a mashi gaskiya, domin kuwa hayaniyar biki data 'kawaye bata barta ta sake taci abinci sosai ba, don haka lallai a wannan lokacin tana jin yunwa.

Sai ya d'auki wayar shi ya kira 'kanin shi, yake cemai :Don. Allah idan akwai sauran abinci gida a d'auko a kawo mashi. "

Yayi saurin cewa me zakayi da shi Yaya Nasser?"

Ya ce cikin zafin murya "Nine zanci! Wani abu!? Kayi sauri ka kawo mani."

Sannan ya yenke kiran, ya kalli Habiba ya ce "Gashinan, za'a kawo maki abincin."

Sannan ya fita waje yana jiran kanin nashi ya kawo abincin.

Zuwa can sai gashi ya shigo d'auke da kular abinci a hannun shi, ya ce "Habiba ga abincin nan, ki tashi ki ci."

Shi kuma ya samu wuri bisa gadon yayi kwanciyar shi.

Dai-dai lokacin da take saukowa daga gadon.

'Dauko abincin kawai tayi ta fito falo.

Tunanin da take shine, ta tabbatar abincin nan tun na rana ne, kilama ya gama hucewa, amma ya ta iya tunda tanajin yunwa, don haka ta zauna ta hau bud'e kular.

Tuwon shinkafa ne da masa, shiya sa ma ta iya cin su sosai, bayan ta gama, ta wanke hannun ta, ta dawo falo tayi tsaye, tana Tunanin abinyi.

Kawai sai tayi kwanciyar ta busa kujera, har barci ya d'auke ta, bataji fitowar Nasser din ba, shiyasa tayi barcin ta sosai, amma tayi.......................

***** ***** ***** ***** *****

"Mun kawo gidan sai ki zauna a cikin motar, kafin in shiga in fito"

Naganar Nasser d'in ce ta katse mata tunanin da takeyi, lokaci d'aya kuma ta 'kara kallon gidan, ta ce "Laaah Yaya Nasser nan ne gidan ka?"

Yayi shiru bai amsa mata ba, sannan ya ce "Ki zauna cikin motar zan shiga in fito, sai mu shiga tare.".

Ta ce "To.

Shi kuma ya fito cikin motar, fuskar shi cike da tsoro da fargabar tashin hankalin da yake hangen zai 'b***e a cikin gidan shi.

Yana fita ta bud'e ledar naman ta fara ci, tana fad'in " Ikon Allah ni kuma tawa kazar amarcin a mota zan cita. ".

Ta fad'a da 'karfi, k**ar tana fad'a ma wani, sannan taci gaba da ci, saida ta 'koshi ta sha madara, kawai dama ta gaji, barci ya fara d'aukar ta, ta zame ta kwanta cikin motar.

Hakanan ya 'kir'kiri 'karfin hali dana zuciya ya tunkari 'bagaren Suwaiba, tunda dama har lokacin Hauwa'u bata dawo ba.

Yayi sallama ya shiga.

Tana tsaye 'kofar d'akin tana shirin fitowa, s**ayi karo da juna, cikin ' karfin hali ya ce "Inata Sallama."

Ta ce "Ai naji ka, shi yasa na fito, sannu da zuwa, Bissimillah, muje falo mu zauna, kasha hanya."

Ya ce "Sosai ma kuwa."

Ya samu kujerar dake cikin falon ya zauna.

Ita kuma ta zauna bisa hannun kujerar da yake zaune Daf! Dashi tana kallon shi, tana so ta fahimci yanayin da yake ciki.

Hakan shine yasa shi kuma ya 'kara jin duk ya tsargu da kan shi, ya kuma tabbatar da cewa lallai Suwaiba taji labarin 'kara auren nan da yayi, duk sai ya daburce, don bai san ta yadda zata d'auki abinba.

Ya gaji dai da halin da suke ciki, ya ce "Wai lafiya? Naga kina ta kallo na, ko ruwa baki kawo min ba

Page      24๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ                 NAFATIMA  DAHIRU FUNTUWA  BINTAPAGE    24๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKuci gaba da  'karfafa...
23/05/2026

Page 24

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟKWATAR KAI๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ


NA

FATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA

PAGE 24

๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ
Kuci gaba da 'karfafamin gwiwa da comment din ku, ni kuma inci gaba da zazzage maku littafan Hausa novels.
Ko yau kika fara cin karo da Posting d'ina, daure kiyi comment da liking hakan yakan sanya ni farin ciki
๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ๐ŸŒฟ

Gaba d'aya ma shi yasa Nasser ya 'kir'kuri wannan tafiya Funtuwar da wuri, ashe sunsan abinda s**a shirya, suna can tare suna soyayyar su harda siya mata mota

Farida ta ce "A'a Suwaiba yana iya yuwuwa ba shi ya sayi motar ba, ai soyayyar da kikayi da shi a baya tafi wadda sukeyi yanzun, kinga da tuni ke ya sai maki kenan."

To bari kiji Farida! In duk jiki na kunne ne bazan ta'ba yarda cewar ba Nasser ne ya sayi motar nan ba! Yanzun fa namiji baka gane halin shi sai ya 'kara aure!"

Farida ta ce "To ki dai bi abin a hankali, kisa ha'kuri domin ki gane gaskiya abin........."

Wai wane irin ha'kuri zakita bani ne? Kullun abu sai 'kara 'baci yake! Gaba d'aya mani jiki na har tsuma ya ke, na 'kosa su dawo, saura kwana uku Nasser d'in ya dawo, to bari kiga, ba zasu dawo rana d'aya ba, sai sun bambanta tafiyar don su 'kara 'batar dani.

Humf! Ki jira kawai kiga yadda zamu 'kare da su, nan da kwana hud'u ki dawo, zakiji abinda nake gaya maki gaskiya ne, ni na tabbatar shi ya sayi motar nan. "

FUNTUWA

Amarya Habiba ta sha gyara sosai, na had'in sinadarai kala-kala na gyaran jiki da fata, na sha dana shafawa, musamman aka d'auko mai gyaran Amarya tayi mata shiri sosai, duk da auren an sanya shi a 'kurarren lokaci, amma ita kanta tasan ta canza, yadda ta 'kara kyau, jikin ta yayi lumi-lumi sai she'ki yake, musamman idan ta 'kara yima kanta kallo a madubi, ta kanyi mamakin kyawun da tayi.

Bayan kuma sinadaran gyaran jiki da akayi mata, an had'a mata kayan mata masu kyau da inganci, wanda suma aka d'auko mai had'in sinadarin tayi mata, kota ina an gyara Amarya, anata shirin biki k**ar yadda ya k**ata.

Tayi gaiyatar 'kawayen ta, duk da ba wani da yawa tayi ba, kasancewar yadda lokacin auren ya kasance, amma dai komai na tafiya dai-dai.

Har cikin zuciyar ta tana son Yaya Nasser, tayi kuma imanin shima yana son ta, sai dai nuna 'kin abin da yakeyi tafi danganta shi da cewa bai shirya bane, don haka kuma idan ta shiga gidan shi komai zai zama dai-dai, domin duk da yake gani na da 'karancin shekaru, saina bashi mamaki, sai na nuna mai abinda yake tunani a kaina ba haka bane.

Shi a tunanin shi 'karancin shekaru na shine zai nuna mai bazan iya kula da muji na ba, aiko zan bashi mamaki.

Tayi Al-'kawarin yi mashi biyayya a duk halin data same shi, zata kula dashi k**ar yadda ko wanne masoya ke kula da juna, zata karantar da shi babi-babi na soyayya irin wanda ada bai san da shi ba ๐Ÿ˜€ (ita a ganin ta) maganar kishiyoyi kuwa aiba zaman su taje yi ba, ko wacce TA KWACI KANTA.

Ni dai zan kula da muji na yadda ya k**ata.

Misalin 'karfe goma sha biyu na rana, Nasser na tare da abokin shi Ibrahim wanda zasu angonce rana d'aya, sunyi shirin su sosai domin kuwa 'karfe d'aya da rabi za'a d'aura auren, sunyi kyau gaba d'ayan su.

Nasser ya ce "Ibrahim wannan shine d'aurin aure na na uku, ko wanne an d'aura mani shi ina cikin farin ciki, amma wannan za'a d'aura mani shi ina cikin fargaba da tashin hankali, Ibrahim idan nace maka bana son auren nan zaka yarda?"

Ibrahim ya ce "Tayaya za'ayi in yarda? Al-halin nasan ka so Habiba tun yarin ta, yanzun idan kace min baka son ta, dole zan tambayi ina dalili?"

Nasser ya girgiza kanshi, cike da damuwa, ya ce "Ina son Habiba, amma yanzun bada aure nake son ta ba, duk da cewa ada akwai Al-'kawarin aure a kanmu, amma yanzun inda za'a barshi da yafimin kwanciyar hankali a cikin gida na, ba yadda za'ayi in sanar da mata na wannan Al-amarin ta waya, don bansan yadda zasu kar'be shi ba, na fi so saina same su mun zauna, sannan muyi magana ta fahimtar juna. "

Ibrahim ya ce " Nasser ka kwantar da hankalin ka, komai zaizo maka da sau'ki in Allah ya yarda, ka wuce muje waje, na tabbatar yanzun abokai na can suna jiran mu. "

Sannan s**a fito baki d'aya, akaci gaba da hidindumin d'aurin aure.

Misalin 'karfe d'aya da rabi aka d'aura auren Nasser Isa da Habiba Saidu, da kuma na Ibrahim wanda aka d'aura 'karfe biyu dai-dai.

Maganar siyen kayan Amarya kuwa cewa yayi don Allah ayi ha'kuri a bashi kud'in idan yaje can zai siya, domin kuwa baya so basu san da zancen Amarya ba, kawai suga ana shigo da kaya, tunda shidai bai sanar da su ba.

Kuma koba komai d'aukar kaya irin wannan tun daga Funtuwa har Abuja, shidai da an barshi idan yaje can ya siya.

Don haka iya kar bikin su anan Funtuwa, aka kai amarya d'akin ta, (anan cikin garin kar'bi d'aki, wanda bayan anyi kwana biyu dayin bikin zai dauke ta su wuce abuja.)

Ranar da zasu tafi daga shi sai ita s**a wuce domin kuwa duk masu biki sunyi nasu sun gama

Address

Fatima Dahiru Funtuwa@gmail. Com
Lagos

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share