Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa

Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa, Fatima Dahiru funtuwa@gmail. com, Lagos.

⚠️ Ka gwada karanta chapter 1 kawai... idan ka iya dainawa, sai ka fita. 😄📖ni na tabbata idan ka fara sai ka nemi na gaba, zan ajiye maku link din ArewaPen, duba Profile dina sosai, zakaga link din ArewaPen, ka bishi, domin morewa💃💃💃💃💃💃💃

Part    2ZUWA LAGOS BA KA JIN TURANCI WATA LUKUTAR MASIFA CE😂  Na kashe wayar na fara  had'a kaya na a ba'kar leda.     ...
19/08/2026

Part 2

ZUWA LAGOS BA KA JIN TURANCI WATA LUKUTAR MASIFA CE😂

Na kashe wayar na fara had'a kaya na a ba'kar leda.

Murna kuwa a wuri na ba'a cewa komai, ko banza dai zani babban birni, kuma dole inci abinci irin wanda yake ci.

Har dare ya sake kira na, yana kara shaida min

"Kada ki zo, don baki san yadda ake rayuwa a kudu ba ne, wahala kawai zaki sha, kin saba da zama a cikin gida cikin rufin asiri, yanzun in kinzo lagos kin san halin da zaki fad'a?"

Na ce "E na sani mana, ba ina tare da kai ba, in da wahala ake sha ai kaima da baka zauna ba, ai kasan can d'in yafi dad'i shiyasa kake tafiya kayi zamanka, in gaskiya kake fad'a ka dawo gida ka zauna mana."

Abin ma ya bashi haushi, ya ce "Binta kada ki kuskura ki zo! Ni ma duk inda na samu kwana nake."

Na ce "To aini na riga nayi niyya, kayi ha'kuri idan nazo za'asan ya za'ayi."

Ban jira ya 'kara cewa komai ba na kashe wayar.

Ranar da zan tafi kuwa saida na amshi rancen dubu biyu saboda kashewa a hanya, nace ina zuwa zai bani kud'in in turo.

Haka naje wurin hawa mota, duka mutanen da zamuyi tafiyar dasu maza ne, ni kad'ai ce mace a ciki.

Ana "Baiwar Allah ko a d'an samu ayi maki wuri daga ciki, tunda ke mace ce."

Na ce "A'a abarni a sama, ai zan mafi shan iska."

Haka muka d'auki hanya ana tafiya ana surutu, tafiya ta'ki 'karewa.

Tafiya ake-Tafiya ake har kud'i na s**a 'kare bamu kai ba, sai dai in wani ya sayi abinci ya sammin.

Har s**a fara tambaya ta "Wai ke ba zaki kira mujin ki bane, ki sanar da shi gaki nan, ya 'kara turo maki kud'in guzuri."

Na ce "Ai bana so ya san na tafo, so nake sai dai kawai yaganni, inyi mai safarayis, saboda bai san cewa yau ne tafiyar tawa ba, ai saidai kawai ya ganni."

Wani ya ce "Dama kin san inda yake ne? Hala kin ta'ba zuwa dama.?"

Na ce "A'a ban ta'ba zuwa ba, amma dai na san a lagos yake."

Ya ce "To idan kinje ki kira shi a waya ki shaida mai kin iso, sai yazo ya tafi da ke."

Na ce "To shikenan.

Kwana d'aya kwana biyu, munata tafiya, wahala dai ta gidan duniya na sha ta, tunda nake ban ta'ba tafiya mai nisa ba, na gaji.

Ga yunwa, abinci baya isa ta, sammin dama ake.

Ba anan tashin hankalin yake ba, muna fara shiga yankin lagos kowa na cikin motar ya koma turanci, ba wanda ya 'kara magana da Hausa.

Haka aka sauke mu gaba d'aya sauran wad'anda muka rage a cikin motar, domin wasu sun sauka tun a hanya.

Sai a lokacin na d'auki waya na kira shi.

Na ce "Gani nan fa na iso."

Cikin razana ya ce "Wai da gaske? To yanzun kina daidai ina?"

Na ce "Nima ban sani ba, ga shinan dai mun shigo inda kowa turanci yake, akwai mutane da yawa a wurin, amma ban san sunan wurin ba..... "

Ya zata kasance? Comment ✔️liking ✔️ sharing ✔️

Idan kuna son ci gaban labarin.

Share nace ayi mani ba copy and paste ba, kada ayi min copy ban amince ba

Fatima Dahiru Funtuwa Binta ✍️

ZUWA LAGOS BA KA JIN TURANCI WATA LUKUTAR MASIFA CE😂    Ina zaman zamana hankali na kwance, wata rana da yamma, ma'kabci...
18/08/2026

ZUWA LAGOS BA KA JIN TURANCI WATA LUKUTAR MASIFA CE😂

Ina zaman zamana hankali na kwance, wata rana da yamma, ma'kabciya ta ta shigo gidan, ta same ni zaune a tsakar gida.

Ta ce "Binta rushi nazo ki sammin, zan had'a wuta Ashana ta ta 'kare."

Na kalle ta nace "Ke kina da halin ma yin girkin, ni tun safe nake zaune a nan ina jiran ya turo kud'i amma shiru, har na gaji da jira, kinga murhun can; duk yau bai ga wuta ba."

Ta samu wuri ta zauna, ta ce "Ke ko Binta wannan wane irin abu ne haka? Ace muji kullun zai turo maki kud'i sai ya ja maki rai, yau in kinyi girki da wuri gobe ba haka ba, gaskiya ki nemar ma kanki mafita."

Na ce "Ke dai bari Halima, na rasa yadda zanyi, dubu daya ce fa zai turo, amma kin gani har yanzun, sai na gaji sannan zai turo."

Ta ce "Shi ko yana can lagos a rana d'aya saiya kashe dubu biyar, yaci wannan yaci wannan, ai inni ce ke binshi zanyi, ai saidai ya ganni a garin."

Na ce "Yanzun nan Halima har dubu biyar yana iya cinyewa a rana?"

Ta ce "E mana ai dad'i suke ci, ba shi yasa s**a ma'kale ma kudun ba, abincin su ba irin namu bane, ai ina baki shawarar duk yadda za'ayi ki shirya ki tafi, duk abinda yake ci kuci tare."

Na ce "Aiko kin kawo shawara, bari in tara kudin mota."

Ta ce "Wane kud'in mota Allah ya kawo sau'ki, akwai wata mota da ake loda mutane har lagos kyauta, sai dai ki tanadi kud'in kashewa a hanya, kije ki hau motar WAJU har lagos kyauta, imma driver ya matsa ne zaice ku bashi dubu biyu."

Na ce "Na gane irin motar, wadda zakiga mutane a can sama, ai mutum ma zaifi shan iska, aiko tafiya zanyi duk abinda yake ci nima saina ci. "

Ta mi'ke tsaye har zata fita ta ce "Binta kinada gishiri ki sammin? Don Allah ki had'o min hada Ashana."

Na je na d'auko mata, ta tafi.

Zuwa can saiga kiran shi, ina d'agawa na ce "Ka kwantar da hankalin ka kwanan nan nima zan biyo ka, kaga ma ka huta da yomin aike, kud'in da kake kashewa kai kad'ai inna zo ya ishe mu muci tare."

Cikin mamaki ya ce "Ban gane kizo ba, me zaki zo yi?"

Na ce "Wurin ka zanzo, naji ance kana kashe har dubu biyar a rana, kuma idan nazo dubu biyar d'in ta ishe mu mu biyu."

Ya ce "Waye yace maki ina kashe dubu biyar?"

Na ce "Halimar gidan malam magaji......"

Ya ce "Gidan ubanwa taga ina kashe dubu biyar din? Kinga Binta yaudarar ki takeyi karki kuskura kizo, idan kinzo bansan yadda zanyi da ke ba, muma nan ko ina muka samu kwana muke, in kinzo ya zanyi da ke?"

Na ce "Ai ka bari kawai idan nazo duk yadda za'ayi ayi, yanzun nan zan fara hada kaya na."

Ya ce "Kinga Binta kada ki zo! Ban san inda zan ajiye ki ba, muma ko ina muka samu kwana muke, in kinzo ke ina zaki ri'ka kwana?"

Na ce "Ka bari kawai idan nazo duk yadda za'ayi - za'ayi. "

Na kashe wayar na fara had'a kaya na a ba'kar leda.

Kuna son jin yadda na kare? To kuyi min comment liking da share, kuji yadda na isa lagos bana jin turanci, kuma kowa turanci yake a garin

Fatima Dahiru Funtuwa Binta ✍️

Part   4KUN TA'BA JIN AN K**A MAYYA A GRA?    Cikin sauri  na d'auki Al-makashi, zuciya ta cike da kwarin gwiwa da rashi...
17/08/2026

Part 4

KUN TA'BA JIN AN K**A MAYYA A GRA?

Cikin sauri na d'auki Al-makashi, zuciya ta cike da kwarin gwiwa da rashin tsoro nayi waje.

To amma ta ina zan fara? Ina kuma zan ganshi kai tsaye yanzun? Domin dai dole kayan dake jikin shi sune zan yanka, sak**akon an shaida cewa su kad'aine kayan da ake ganin shi da su.

Hanya kawai na k**a naci gaba da tafiya a cikin layi, tare da waige-waige ko Allah zaisa in ganshi.

Cikin 'kudurar Allah kuwa na hango shi zaune kan wani kututturen icce, tare da wasu maza dattawa suna fira.

Hankali kwance ba wata fargaba ko jin tsoro na tunkari inda suke, saida naje daf! Da su sai na zagaya ta bayan su.

( Idan Allah ya nufe ka da samun mafita cikin sau'ki sai kayi mamakin yadda zai sau'kake maka Al-amurran ka.)

Zulumbuwar rigarshi naga ta bazo har baya, sai na tsugunna k**ar na yadda wani abu, cikin hikima a hankali nasa Al-makashi na yanki rigar ba tare daya sani ba, kuma har nabar wurin bai san abinda nayi ba.

Ganin na samu wannan nasara ba tare da wani tashin hankali ba, nayi godiya ga Allah na tafo gida.

Duka abinda na yanka a jikin rigar tashi bai wuce ga'bar d'an yatsa ba, ko shi ba lallai ya fahimci cewa yankar ta a kayi ba inya gani.

Na d'ora magani a wuta na dafa k**ar yadda mai magani ta bani, bayan ya dahu na tace na ba yaron ya sha, sannan nayi mashi wanka da sauran.

Ba'a fi minti talatin ba saiga yaro ya fara bud'e ido lafiya lau, har da fad'in "Inna zan sha ruwa."

Na ce "Alhamdulillahi yaro ka samu, rabon da aji yayi magana kusan kwana biyar kenan.

Zuwa yamma saiga yaro ya fara tashi zaune da kanshi har da mikewa tsaye.

Ya Allah kayi mana tsari da miyagun mutane, ka shiga tsakanin mu da makiyan mu

Fatima Dahiru Funtuwa Binta ✍️

Part   3KUN TA'BA JIN AN K**A MAYYA A GRA?    Haka na anso magani muka tafo gida.    Kamar yadda mai maganin nan tace ha...
16/08/2026

Part 3

KUN TA'BA JIN AN K**A MAYYA A GRA?

Haka na anso magani muka tafo gida.

Kamar yadda mai maganin nan tace haka na d'ora maganin nan a tukunya, na zauna bakin murhu ina jiran ya tafasa inga wane munafikin ne zai shigo.

Zuwa can ruwa na fara tafasa, na d'auka zanga mayen ne ya shigo gidan kai tsaye, ko kuma a wani yanayi wanda damun ganshi zamu gane, ashe abin ba haka bane.

Kawai dai munji anyi sallama, kuma hankali kwance ba wadda zaka yima mutum wani zargi ba.

Koda a kayi sallamar yaro ya fita, sai mai sallamar ke tambayar shi "Baban ku nan?"

Shi kuma ya ce "Aa ba yanan."

Shikenan saiya wuce, shi kuma yaron ya shigo gida, bamu kawo wani abu akan mai sallamar nan ba, domin kuwa mu jira muke muga an shigo kai tsaye, tunda ance turaro shi za'ayi.

Ruwa har ya kusa 'konewa ba wanda ya shigo.

Hankali nafa ya tashi, to yanzun haka zamu ha'kura muna kallo yaron nan yayi mutuwar maita? A' ah zuwa can sai wani tunani ya fad'o mani, nacema yaron nan "Kai d'azun da akayi sallama waye?"

Ya ce min "Wane ne."

'Kirji na yace rass! Domin kuwa tabbas ana d'an zargin mutumin, kai na yayi wani nauyi, na ce "To tabbas maganin nan yayi! Mutumin nan shine."

Na kalli sauran 'yan uwana nace to yanzun ya za'ayi a samu a yanko kayan shi a dafa maganin? Tunda mu dai ba zuwa gidan shi muke ba, kaje kuma kai tsaye yace kayi mashi sharri, ku fara shari'ar da ba 'karewa take ba, yanzun ina shawara ya za'ayi?"

Cikin 'kan nai na wani ya ce "Wane tsoro! Haka za'a sa ido shi ya kashe mutum! Ai dama duk tsoron ne ke wahalar damu, aje a yanko rigar jikin shi, inma ta k**a a d'auko shi ayi mai d'an iskan duka a yanki kayan, indai yaro ya samu lafiya daga baya duk abinda za'ayi sai ayi."

Innar mu ta ce "A'ah gaskiya, kada aje a d'auko magana, yanzun dai in shirya inje gidan k**ar naje siyan wani abu, idan naga an shanya kayan maza in yanko, sai in kawo a dafa maganin, fa'kat! Hankali kwance ba tare da anyi tashin hankali ba."

'Kani na ya ce "Wannan duk ba mafita bace, to idan aka yanko kayan daba na shi ba fa? Shifa kayan shi kala d'aya ne, kuma kullun suna a jikin shi, dole dai kinga na jikin nashi dai za'a yanko, ba wani tsoro ko tsayawa shawara kuna ganin halin da yaron nan yake ciki, aje ayi duk mai yuwuwa, indai yaron ya samu lafiya, duk abinda zai biyo baya mai sau'ki ne.

Na 'kara kai kallo na akan yaron, naga halin da yake ciki, mutuwa ko yanzun😭, hankali na ya 'kara tashi, na ce "Indai abinda zanyi zaisa yaron nan ya samu lafiya, to kowace irin rigimace zan iya tunkarar ta, wannan ai zalunci ne! Na rantse da Allah ba rigar jikin shi ba, ko gashin kanshi akace in ciro yau saina ciro shi! Don haka ku jira ni."

Cikin sauri na d'auki Al-makashi, zuciya ta cike da kwarin gwiwa da rashin tsoro nayi waje................

Commente din dai😂 liking d'in dai🙈, sannan kuyi mana share, Allah abubuwan ne da yawa, shiyasa ban karasa ba, amma a 'kara hakuri dani.

Kuna son ci gaba? To inga ruwan comment da liking.

Au! To share din fa? Inga k**ar guda dari, in idasa maku wannan labarin daya faru a kaina da dana.

Fatima Dahiru Funtuwa Binta

Part   2KUN TA'BA JIN AN K**A MAYYA A GRA?       Da aka gama tashin iskokan abin dai ba sau'ki, sai aka yanke shawarar a...
15/08/2026

Part 2

KUN TA'BA JIN AN K**A MAYYA A GRA?



Da aka gama tashin iskokan abin dai ba sau'ki, sai aka yanke shawarar aje wurin malami a anso taimako.

Haka muka d'auki yaron nan, mukaje wurin wani malami, anan cikin unguwar mu.

Mukayi mashi bayanin abinda ya faru.

Nan dai yayi mashi addu'o'i, ya bashi ya sha, ya had'a duk abinda yake ganin zai iyayi don ganin ya taimaka, mukayi godiya sosai muka bashi abin sadaka.

Yaro ya samu sau'ki, har ya samu barci, hankali ya kwanta, kowa yayi barci.

Sai can cikin dare abu ya 'kara tashi, ya fara 'yan gane-gane, idan mage ya gani baya jin tsoron ta, sai dai muga ya kaima gidan sairo duka da yakushi, ya ce "Innar mu mage ce take shigowa! ."

Amma idan yaga wata halittar saiya tsorata, ya fasa 'kara, ya 'kan'kame ni.

Haka dai har gari ya waye bamu samu barcin kirki ba.

Washe gari irin 'yan zuwa dubiyar nan, wata ta ce "Gaskiya yaron nan ku kaishi gidan mai magani, wannan ciwon bana asibiti bane."

Mukace "To mu ina muka sani?"

Tayi mana bayanin gidan wata mata mai bada magani a wani 'kauye kusa damu.

Haka muka d'auki yaron nan ranga-ranga, idanu sun tutturo waje, ya datse harshen shi da ha'kori, yaro fa k**ar inka fita ba zaka dawo ka tarar da shi da rai ba.

Muna zuwa wurin mai magani muka aje mata yaro.

Ta ta'ba shi ta duba shi sosai, kawai saita girgiza kai, ta ce "Wannan yaron miyagu ne s**a k**a shi, kuma gaskiya sun ri'ke shi sosai, ba ko wane magani za'ayi mashi yasa su sake shi ba, yanzun mafita d'aya ce, akwai wani magani kasadin, wanda indai akayi shi duk bala'in maye, duk yadda ya ri'ke mutum saiya sake shi, amma gaskiya ana son mahad'in maganin da gaugawa.

Mahad'in maganin kuwa shine ( a yanki tufafin mayen, a dafa maganin da shi) ko yaya d'an 'kyallen yake, komin 'kan'kantar shi, in dai kayan da mayen yake sakawa ne, to a san duk yadda za'ayi a dan yanko shi, a hada da wannan maganin a dafa. "

'Kirjina fa ya buga, domin na tabbatar karshenta yaron nan sai dai ya mutu, tun da bamu san ma waye mayen ba.

Na ce mata, yanzun ba wani abu da za'a iya yi, tunda mu dai bamu san waye mayen ba, wata 'kila can wurin yawon shi ma ya had'u da shi."

Ta ce " Gaskiya babu, iya kar taimakon da zan iya yi kenan, kuma gaskiya yaron nan a hannu yake, in ba'ayi sauri ba zasu ida sa nufin su. "

Na ce " To yanzun ya za'ayi mu gane mayen? "

Ta ce "To Alhamdulillahi, zan baki wani magani, idan kinje gida, ki had'a wuta ta icce, ki zuba maganin a cikin tukunya, ki zuba ruwa, kada ki bar wurin, ki zauna ki had'a mai wuta sosai ya tafasa, to yana tafasa ki bude tukunyar tururin shi ya fito, a dai-dai wannan lokacin duk wanda yayo maku sallama shine mayen, ki kula duk wanda ya fara shigowa gidan a lokacin da tukunyar ta tausa, to Tabbas shine mayen, domin kuwa an turaro shi, duk inda yake dole sai yazo.

To daga nan dubara ta rage ta ku, duk yadda zakuyi ku yanko min kayan shi, komin 'kan'kantar 'kyallen, ni kuma zan baku magani ku had'a da 'kyallen ku dafa maganin, ku ba yaron yasha, kuyi mashi manka da maganin, to duk bala'in mayen sai ya sake shi. "

Haka na anso magani muka tafo gida...........

Gaskiya sai naga ruwan comment da liking da sharing sannan in fad'a maku yadda muka ' kare, idan naga ruwan comment zuwa dare inci gaba.

Fatima Dahiru Funtuwa Binta

KUN TA'BA JIN AN K**A MAYYA A GRA?     Wannan tambayar da taita yawo a social media ta sa na tuno da wani labari daya fa...
15/08/2026

KUN TA'BA JIN AN K**A MAYYA A GRA?

Wannan tambayar da taita yawo a social media ta sa na tuno da wani labari daya faru a kaina, wasu shekaru can baya da s**a wuce.

Yaro na ne ya fara rashin lafiya, zazza'bi haka da ciwon kai, aka bashi magani tsawon kwana biyu, jiki dai yana nan, sai aka kaishi kyamis, aka fara yi mashi allura, tsawon kwana uku, ciwo dai sai gaba yake, anata jiran sau'ki shiru.

Bayan yayi sati d'aya kwance, ciwon yaci jikin shi sosai, don har ma kanshi da harshen shi ya kare, baya iya magana, komai ma bai san yanayi ba, a lokacin yaron bai wuce shekara bakwai ba.

Da jiki yai zafi, sai mukace to a tafi asibiti, duk a tunanin mu idan akaje Asiti gado za'a bamu saboda yanayin yadda jikin yaron yayi sanyi.

Innar mu ta d'auki yaro ta goya a baya, zuwa can bayan azahar sai gata ta dawo, wai basu basu gado ba, Allurai s**ayi mashi da magunguna, har baban mu nata fad'a yana cewa "Wannan yaron ruwa ya k**ata a 'kara mashi, funda ko magungunan ma baya iya sha, don bai san ma inda kanshi yake ba, bai k**ata ace ba'a kwantar da yaron nan ba."

Zuwa can bayan la'asar jikin yaro fa yayi zafi, sai aka kira wani likita mai kyamis nan cikin unguwar mu yake, shima yana taimakawa sosai.

Yana zuwa kuwa ya ce "yaron nan ruwa yake bu'kata.

Aiko ya jona mashi ruwan nan, muna zaune muna gadin shi, ruwa nata tafiya.

Zuwa can gab! Da magari ba ruwa ya 'kare, a lokacin yaron ya iya bud'e idon shi ya d'an fara kuka.

Ai farkowannan da zaiyi, tunda dama k**ar ya suma ne, sai ya fara da gane-gane.

'Kanwata Shamsiyya na zaune ya kalle ta ya fara magana a hankali cikin zafin ciwo, ya ce "Aunty Shamsiyya ga wani tsofo nan ya ma'kale a jikin ki."

Shamsiyya ta ce "Mee!?"

Ya ce "Wani Aljani ne gashi nan a jikin ki tsofo."

Shamsiyya ta mi'ke tsaye ta daka tsalle, ta fasa ihu, tana innalillahi wai Aljani a jiki na! "

Kai! Abu fa k**ar wasa sai ya ce "Ga zomo nan zai shigo d'akin nan." zuwa can kuma "Ga mage nan ba'ka, ga bera nan ya shigo."

Irin dai kana nan abubuwa haka ya rika gani, zuwa can daya fasa wata kuwa, ya mi'ke a tsorace ya ce "Ga kura nan." ya rugo da gudu yana kankame mutane, abufa ya rikice sosai, muka fara yi mashi addu'o'i, Iklas- Fala'ki-Nasi-Ayatul kursiyyu, kowa na karanta abinda yazo bakin shi ana tofa mai, amma yaron nan bai daina gane gane ba.

Tun muna d'aukar abin k**ar wasa, har muma jikin mu yayi sanyi muka tsorata, ganin yadda yaron ya gigice da irin tsoron da ake ba shi.

Zuwa can ba sai masu iskokai s**a fara tashi ba, ni kaina ban san inada Aljanu ba sai ranar, yo tashin hankali ya'ki karewa.

Aljanu fa s**a hau, akai turanci-akai yarbanci - akai inyamuranci, yaron nan bai daina gane-gane ba, saima abinda yayi gaba.

Da aka gama tashin iskokan abin dai ba sau'ki, sai aka yanke sharar aje wurin malami a anso taimako.

IDAN NAGA RUWAN COMMENT DA LIKING DA SHARE INCI GABA DA BAKU LABARIN, IDAN BANGA NI BA KUWA GASKIYA SAI KUN JIRA.

Fatima Dahiru Funtuwa Binta

PART   3🤣🤣🤣 YO WA YA'KI BANZA🤣🤣🤣    Washe gari tunda nayi Sallar Asuba ban koma barci ba, na fara gyare-garen gida na, d...
13/08/2026

PART 3

🤣🤣🤣 YO WA YA'KI BANZA🤣🤣🤣

Washe gari tunda nayi Sallar Asuba ban koma barci ba, na fara gyare-garen gida na, domin kuwa jiya ban iya aikata komai ba, gajiyar da nayi, ga wahalar matsewa da na sha, jiki na gaba d'aya ciwo yake, ko abinci ban iya yi ba, sai dai wata ma'kabciya ta ta bani.

Shi yasa yau tunda na tashi gida kaca-kaca na hau aikin gyaran shi, ina fitowa wanka kuwa saiga Saude, tun wajen 'karfe bakwai.

Na ce "Ah ah! Saude tunda safe haka?"

Ta ce "E mana; ai gara muyi sammako ko ma samu wuri daga farko-farko, kinga dai jiya yadda ta kasance, ba samu nayi ba, yo wannan aiba sammako ba ne, wasu fa a can suke sallar Asuba, suna gama sahur suke tafiya, yo bacin ma watan Azumi ne, ai wasu har kwana suke wirin kar'bar sadaka, ke dai yi maza-maza ki tafo mu tafi, yanzun haka wurin na can ya fara cika da mutane."

Haka na d'auko hijabi na muka tafi.

Saida muka fara biyawa wurin mai shago, na amshi kud'i na dubu Talatin, sannan muka wuce, har ina cema Saude "Yanzun kud'in nan zan baki dubu biyar a ciki, tunda ke kika bada wannan shawara, idan mun amso Taliyar zan biya wurin mai kifi in siya, idan naje gida inyi taliya da miya, in sayi lemo na mai sanyi, ko na huce gajiya, inje in yanko katin Adashe, in fara zuba dubu goma, a hankali-a hankali idan yana d'an yimin aike, sai in ri'ka zubawa, sauran canjin kuwa in rika kashe abuna a hankali."

Saude ta ce "Aiko na gode, ai dama yanzun mata da haka suke wayau, sai kiga mace ta canza kayan d'aki, kuma bata sana'ar komai, to irin wannan dubarar ce, wata kuma kiga ta sayi abin sana'a, ballantana ke da mujin ki ma yake tafiya, ko da dai ba kud'in yake baki a hannu ba, ai kina iya siyar da kayan abincin, idan kinga sun d'anyi yawa, sai ki rage ki saka a kud'in Adashe."

Haka dai muna tafiya muna fira, har muka isa wirin sadakar.

Muntarar da mutane a wurin, haka muma muka samu wuri daga farko muka zauna, ana ta fira.

Can sai naji wasu mata na cewa :Waccen matar fa k**ar ta amshi sadakar nan jiya?"

Wata ta ce "Ta amsa mana, ba itace mai ihun nan ba? Wadda daga bata sadakar ne wuri ya hargitse, amma dayake mutane ba tsoron Allah gashi nan ta dawo, don ta 'kara tada hayaniya a bata, kuma wannan zalunci ne, ba ka bari amba wani ba kai kuma ka amsa sau biyu, don rashin tausayi."

Wata budurwa jibgegeyi na tsaye ta ce "Aiko in dai ta 'kara tada hayaniya irin ta jiya aka bata, sai mun kwace Taliyar, wa tafi iya munafinci?"

Saude na jinsu ta ce "Aiko naga ubanda ya isa ya kwace taliya a hannun wani! Duk wanda yakeda rabo zai amsa! Ai ba ita kad'ai bace aka ba jiya ta dawo yau! kowa ya san haka dama d'abi'ar take."

Aiko aka taso mata haya-hayah k**ar ayi dambe, da 'kyar dai abin ya lafa.

Alhajin nan bai fito ba saida muka gaji da zama, sai bayan Sallar Azahar sannan yazo raba zakkar, a yau hada wasu maza majiya 'karfi ya zo, basoda gudun hayaniya, kuma su ri'ka sama mutane layi.

Haka aka jeru aka fara rabon zakkar, kuma yau abin a natse, saboda mazan nan suna taimakawa, basu bari a hargitsa layi, kuma basu barin wanda aka ba ya sake dawowa, daki-daki ake ba kowa, mutane anata jin dad'i, domin kuwa da alama yau kowa saiya samu.

layi yazo kanmu, daga Saude dama saini, aka ba Saude, naje zan kar'ba, Alhajin nan ya kalle ni fuska a murtuke ya ce "Ke ba na baki ba jiya?"

Na girgiza kai na ce "Ba ni ba ce."

Saidai naji ya ba ni Fayauuu! Da bulala, ya ce "Ni zakiyima 'karya! In baki abin da hannu na kice min ba ke ba ce! Ai na gane ki da wannan JAN HIJABIN!! Wuce ki ba ni wuri!! ni na tsani mutum mai 'karya! Saboda rainin yawau harki bud'e baki kice min ba ke bace?"

Wuri fa ya kaure da murna da jin dad'i mutane sunata yimin dariya.

Haka muka tafo nida Saude, har tana cemin "Kiyi ha'kuri kawai, abinda kikayi niyya karki fasa, ai akwai gidajen sadakar da yawa, akwai indama abinci ake badawa da kunu."

Na ce "Ni dai gaskiya na ha'kura, ba inda zan kara zuwa, zan kira muji na a waya ince mai ya sake turomin kud'in kayan abinci, wad'an can kayan abincin da aka siya 'barayi sun sace, nasan dai dole zai kara turowa, kici gaba da zuwa neman sadakar ki ke kad'ai, barci na ya fiye min Al-kairi, kuma hankali na yafi kwanciya."

'Karshe

Comment d'in ku-Liking d'in ku-Sharing d'in ku, shine abinda yake 'karfafamin gwiwa, don haka inga ruwan Liking k**ar guda dubu, Comment d'ari biyar, share d'ari biyu da hamsin, hakan zai 'kara sawa in tabbatar ana tare dani.

Fatima Dahiru Funtuwa Binta✍

Part     2🤣🤣🤣YO WA YA'KI BANZA🤣🤣🤣   Haka dai muma muka ja sahu akaci gaba da fira.    Wata tsohuwa dake zaune kusa damu ...
13/08/2026

Part 2

🤣🤣🤣YO WA YA'KI BANZA🤣🤣🤣

Haka dai muma muka ja sahu akaci gaba da fira.

Wata tsohuwa dake zaune kusa damu ta ce "Gaskiya wannan karon mutane sunyi yawa, Allah yasa munada rabo bana, bara ba'ayi yawan haka ba."

Saude ta ce "Yo me zai hana ba za'a samu ba Baba? ki dubi fa girman sito d'in can cike yake da taliya, kuma duk raba ta za'ayi, ai komin yawan mutane kowa zai samu."

Tsohuwar ta ce "Mutanan ne ba suda adalci, masu 'karfi a jiki sai su amsa sau biyu sau uku, idan an ba su su koma layi, suci harda rabon wani, mu kau da muke tsofaffin nan sai ai ta ture mu, kar kiga fa irin turereniyar da akayi bara wurin kar'bar zakkar, wasu duk ba su samu ba, amma akwai yarinyar da tace ta samu kwali biyar, ai kokowa ake yi ne a wurin kar'bar zakkar, mata ba natsuwa, amma da ace layi za'abi kowa zai samu, amma san kan mutane yayi yawa."

A zuciya ta na ce (Ba wani bin layi, yau duk yadda za'ayi nima saina amshi kwali ko uku ne, yadda na siyar da kayan abinci na a banza d'in nan, ai naji haushin mai shagon nan, shege d'an san banza, azzalumi, ni gaskiya ya cuce ni, wad'annan uban kayan abincin amma a dubu Talatin, amma ba komai, tunda dai nima inada 'karfi a jiki na, zanyi turereniya in samu kwalin taliya ko uku ne)

Alhajin nan bai fito ba, sai can har mun gaji da zama, rana ta gama dukan mu, sai gashi ya fito.

Sannan yayi sanarwa yana mai ro'kon mutane

"Kowa ya natsu! insha Allahu ba wanda zai bar wurin nan saiya samu, don haka kuyi ha'kuri ku ja layi, banda kokoyi, kowa zai samu.

Sannan aka ja layi aka fara rabawa a natse, zuwa can wuri ya fara yamutsewa aka fara rigima, saboda wad'anda aka ba; sun sake dawowa layi, kuma 'yan uwansu na bud'a masu wuri suna cin layi.

Da naga dai wurin zai yamutse nima na shiga rububi, saboda in samu, saboda naga abin ya fara zama na masu 'karfi.

A kayi turereniya-A kayi turereniya har wasu na fad'uwa, ni kuwa wasu mata masu 'kiba s**a sakani a tsakkiya, s**a matse ni, gashi an take min 'kafa, naji azaba, ga zafin rana ga matsewa numfashi na na neman d'aukewa.

Haba! Na ji dai wuya tayi wuya na fara ihu ina kuka, ina fad'in "Hannu na😭 hannu na! wayyo Allah za'a kashe ni! an matse ni, jama'a an karya min hannu! Wayyoooo ni Binta wannan wane irin tsautsayi ne😭😭 a kawo min dauki!! Zan mutu."

Na cika masu wuri da ihu, har aka d'an saurara da hayaniya, ni ko na 'kara 'bare bakin kuka, har Alhajin nan ya jiyo, ya fara magana,

"Wacece nan aka matse? Ku bata wuri tazo a sallame ta, karku ja ai min kisan kai, ku bata hanya ta zo ta amsa."

Aiko aka bud'a min hanya na wuce salun-alun ina d'angyashi na amso taliya ta kwali d'aya, har Alhajin yanayi min sannu, ya ce in samu wiri in zauna in huta.

Aiko ganin an bani wannan Taliya, layi na bai zo ba, sai wuri ya 'kara hargitsewa, wai anyi zalunci, layi na bai zo ba an bani, mata sai surutu, aka fara kokoyi harda dambe, shi kan shi Alhajin akayi kanshi ana neman a danne shi, wata fa sabo da 'karfin hali har rigar shi ta jawo ta yage, ba arzi'ki ya rufe sito d'in, ya koma gida, yace an gama sai kuma gobe.

Ita kanta Saude da muka tafi tare da ita bata samo ba, take cewa

"Ai ke Allah ya taimake ki, da ace ba kiyi kuka ba, da ba zaki samu ba, yanzun dai yace sai gobe zaici gaba da rabawa, Allah ya kaimu saimu zo da wuri."

Na ce Aiko gobe ma haka zanyi..........

Comment-liking-sharing idan kuna so muci gaba , amma idan banga ruwan comment ba to gaskiya sai kun jira

Fatima Dahiru Funtuwa Binta✍

🤣🤣🤣🤣YO WA YA'KI BANZA🤣🤣🤣🤣       Idan watan Azumi ya k**a, bayan nayi sallar Asuba nayi Addu'o'i na, komawa nake in kwant...
09/08/2026

🤣🤣🤣🤣YO WA YA'KI BANZA🤣🤣🤣🤣

Idan watan Azumi ya k**a, bayan nayi sallar Asuba nayi Addu'o'i na, komawa nake in kwanta in sha'ki barci na, sai Azahar in tashi, inyi sallah in d'anyi abinda zanyi na ibada, abinci kuwa sai wajen 'karfe biyar da rabi nake d'orawa saboda ni kaid'ai ce, abinda naga dama shi zanyi.

Wata rana, mun d'auki Azumi na bakwai, ina kwance ina barci, misalin 'karfe tara na safe, naji ana bubbugo min 'kofar gida, na tashi na nufi 'kofar gidan na bud'e.

Wata 'kawa ta na gani tsaye da buhu a hannun ta.

Na ce "Saude ina kuma zaki haka da safe hada buhu?"

Ta ce "Ke dai muje ciki, buta zaki bani in shiga bayi, hanya ce ta biyo dani ta nan, nace bari in shigo mu gaisa."

Na bata buta ta zagaya, bayan ta fito ta ce "Kin ganni da buhu ko? Wani Alhaji ne akace zaiyi rabon zakka, dama duk Azumi yanayi, wannan karon ma ance kwali-kwalin taliya zai raba, to shine fa kikaga na shirya zani."

Na ce "Kwali-kawalin taliya fa kika ce!?"

Ta ce "E mana, ko bara ma haka ya raba, ai ni tunda Azumin nan ya k**a banga ta zama ba, kullun saina fita, yo abu dai daga bana sai bad'i, gara kad'an raruma ka samu rabonka."

Na ce "Yo ni kice ashe barcin banza nake! inda ace dani aka fara zuwa bar'bar zakkar nan; aida na tara kayan abinci, kinga kayan abincin can, ana saura kwana biyu Azumi ya turo ma mai shago kud'i aka had'a min su, to don Allah inda ace maza suna bada had'in kai, aida ni ya turo ma kud'in, kinga ba sai na sayi kayan abincin ba, idan na samo na zakkar nan ya ishe ni, to amma ba zai gane ba, kullun gani yake cutar shi zanyi, shifa bai yarda ya aiko min da kudi kai tsaye ba, ya gwammace ya tura ma mai shago kud'i akawo min kayan abincin, in dai kinga kud'in shi sun shigo hannu na to shine yayi niyyar bani kyauta, amma don Allah wannan gara'basar Azumin aida na tara kud'i, amma duk da haka muje zan biki yau."

Ta ce "Ah! Hada ku ma masu maza?"

Na ce "YO WA YA'KI BANZA, Ai yanzun nan zan wanke ido na mu wuce, ana samun irin wannan Al-kairin."

Ta ce "To ya zakiyi da wad'ancan kayan abincin? idan ya dawo ya tarar da kayan abinci da yawa fa?"

Na ce "To Saude ko dai muje a siyar da su, tunda dai wasu za'a samo?"

Ta ce "To ai nima dai haka na gani, ki d'auko muje akwai wani mai shago akan hanya, yana siye, in kika saida sai ki adana kud'in ki, ai mazan yanzun ba su kaunar mata suyi arziki."

Na ce "Aiko wannan karon sai nayi, asusu ma zan bude ko kuma in shiga zubi d'an kati."

Haka ta taya ni muka zuba kayan abincin nan a buhu muka d'auka, muka tafi.

Haka mukaje shagon nan ashe banza yake siyen kaya, duk ya karya mana darajar kayan abincin, hakanan na ha'kura na siyar tunda dai ai na kyauta zamu samo, don haka ba fad'uwa ba ne, kuma yace ba shida kud'i yanzun, mu bari zuwa anjima idan yayi ciniki sai muzo mu amsa, haka mukayi tafiyar mu wirin kar'bar sadakar.

koda mukaje wurin amsar sadakar nan mata ne tunjum! Haka muka zauna muka ja layi muma, anata fira k**ar gidan biki, tunda har lokacin Alhajin ma bai fito ba, wai sai 'karfe sha biyu yake fitowa, amma kar kaga yadda mutane s**a cika kofar gidan.

Haka dai muma muka ja sahu akaci gaba da fira........

Comment💖Laking💖Sharing, idan kuna so muci gaba, inga ruwan comment k**ar guda dubu, inga sharing k**ar guda dari biyar, liking kuwa in kasa kirgawa😀 yauwa! To saimu dawo muci gaba.

MASU COPY SU DORA A PROFILE DIN SU BAN AMIN CE BA.

Ka danna wurin sharing kawai, kafin kayi posting daga sama zakaga inda kaima zakayi naka rubutun, saika rubuta abinda kake so sannan kayi posting.

Fatima Dahiru Funtuwa Binta✍

Page    7WATA SAKAYYAR............             NAFATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA PAGE    7🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀  Bana cikin marubutan ...
07/08/2026

Page 7

WATA SAKAYYAR............


NA

FATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA

PAGE 7

🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀

Bana cikin marubutan dake siyar maku da littafi 1k-1500-2k, comment da sharing d'inku kawai nake so.

Wanda yayi min comment 🥀wanda yayi min liking 🥀wanda yayimin share 🥀 to wannan shine ya biya ni kudin littafi na.

Idan kuwa har za'ayi min adalci to inga ruwa comment da sharing

🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀

Fa'iza ta ce "Allah ya sau'ke! Ai bamma tsaya sauraren shi ba, kada in saurare shi ya 'bata min tunani na, yace min Asiri akayi mani , yasa inzo inta hasashen ko wane ne-ko wane ne, ya gur'bata min tunani na, ya sanya min zargin mutanan da ba suyimin komai ba, a 'karshe kuma ba zai iya yimin maganin ba, tunda dai kince muje wurin Malam Shehu Mai Al-majira, sai mu jarraba ,ai shi malami ne.

Maman Hafsat ta ce "To Allah yasa mu dace."

Bayan kwana uku kuwa s**a shirya s**aje wurin Malam Shehu, bayan anyi Sallar Isha'i, s**a same shi a d'akin shi, yayi masu izinin su shigo.

Bayan sun zauna s**a gaishe shi.

Ya ce "Bayin Allah meke tafe daku?"

Maman Hafsat ta ce "Malam wurin ka mukazo, domin a taimaka a taya mu da Addu'a, tunda ga Al-majirai a tare da kai, bamu san inda za'a dace ba."

Ya ce "Hakane meke faruwa?"

Fa'iza ta ce "Na ta'bayin aure, haihuwata Hud'u da muji na sannan muka rabu, to tunda muka rabu na dawo gida inata zawarci shiru har yau shekara goma kenan, koda wasa wani namiji bai ta'ba cewa yana so na ba, tun abin baya damuna har ya fara d'agamin hankali, duk da inayin Addu'a amma dai har yanzun shiru."

Malam Shehu ya ce "Ikon Allah, shin ba'a ta'ba zuwa ance ana son ki bane koko dai ana zuwa dawowa ne ba'ayi?"

Ta ce "A'a ba'a ta'ba zuwa bane."

Ya jinjina kai ya ce "To shikenan, wannan duk me sau'ki ne, muji dai ko, insha Allahu za'a nemo shi, ee ki kwantar da hankalin ki babu abinda ya gagari Allah, kici gaba dayin Addu'a ba'a sarewa, nima nan zansa ayi saukar Al-'kur'ani a gani, sai kuma za'ayi sadaka, insha Allahu komai zaizo da sauki, wannan ai abune me sau'ki a wurin Allah, ba komai Allah yana sane da halin da bawan shi yake ciki."

Fa'iza ta ce "To nawa ne za'a bayar."

Ya ce "A'a ai abin sadaka ne kawai zaki bayar, duk abinda Allah ya h**e, da safe za'a sayi 'kuli-'kuli ko fanke ayi sadaka dashi, sai kuma saukar Al-'kur'ani dana ce maki, sai kuma wasu magunguna da za'a rubuta wasu ayoyi daga cikin Al-'kur'ani, a wanke sai a ji'ka maganin da wannan rubutun, idan ya bushe zansa a daka, idan kika dawo zan baki shi, sannan in fad'a maki yadda zakiyi amfani da shi, Allah yasa mu dace, amma muji kam za'a nemo shi.

Fa'iza ta d'auki kud'i dai-dai 'karfin ta ta bashi, ta ce "Gashinan ayi sadakar da kuma abinda za'a nema na had'in maganin."

Yasa hannu biyu ya kar'ba tare da fad'in "Allah ya kar'ba, Allah kuma ya biya bu'kata."

S**a amsa da "Amin, sannan s**a taho gida, tare da fatan Allah yasa anyi a sa'a.

Nan s**azo suna ba Maman Fa'iza d'in labari.

Ta ce "To yaya za'ayi? Ai nema ya zama dole, Allah ya kawo maki iyakar abin, ai bazan hana ba, dole ne mutum ya tashi ya nema, wannan zama ai ya isa haka, Allah yasa a dace, amma ace kaita rayuwa a haka, tunda auren ta ya mutu ba wani, ai dole ne ka neman ma kanka mafita.

Ranar wata Juma'a, ranar zasu koma wurin Malam Shehu, Fa'iza tayi wanka ta shirya, ta fara biyama Maman Hafsat .

Tana shiga ta ce "Keh! Maman Hafsat yau naga abin mamaki!"

Maman Hafsat ta ce "Meya faru?"

Fa'iza ta ce "Majalisar nan ta 'yan sa idon 'kofar gidan ku, kinga yadda suke kallo na kuwa? Hada wani cemin saikin dawo, ni da ada har inbar wurin ba wanda yake d'aga ido ya kalle ni, amma shine yau harda yimin magana."

Maman Hafsat ta ce "To aiko inaga wata lakurar gareki, wadda tasa maza ko kallon ki basuyi, ballan tana s**e suna son ki, keeh!Wannan abu dame yayi k**a? Amma insha Allahu komai yazo 'karshe, kice har magana s**ayi maki?"

Fa'iza ta ce "Hummf! Ke dai bari, ni har abin mamaki ya bani, tunda nake wucewa ta gaban su ko d'ago kai basuyi su kalle ni, amma wai yau harda yimin magana, ke dai shirya mu wuce wuri Malamin nan."

Maman Hafsat ta d'auko hijabinta, basu biya ko ina ba sai wurin Malam Shehu mai Al-majirai.

Bayan sun zauna s**a gaishe shi, yayi masu sannu da zuwa, sannan yaci gaba da cewa "Nasa anyi ro'kon Allah sosai an sauke Al-'kur'ani, anyi sadaka, da izinin Allah kuma zamuga Hasken abin, sannan Fa'iza kina yin mafarkin ruwa ko iska, ko kuma kina tafiya amma kin kasa kaiwa gida ko kin bace?"

Ta ce "A'a amma lokacin da ina budurwa nayi fama da irin wad'an nan mafarkan, da kuma lokacin da inada aure, amma gaskiya yanzun banayi, tunda yake ina amfani da Addu'o'i sosai."

Ya ce "To shikenan, ba matsala, kin san abinda ke faruwa dake?"

Fa'iza tayi sauri d'ago kai ta kalle shi don taji abinda zai ce .

Ya ce "Gaskiya DUHU

Address

Fatima Dahiru Funtuwa@gmail. Com
Lagos

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share