Jarbeerou aleeyou alyaryasy

Jarbeerou aleeyou alyaryasy DEAR MY FOLLOWERS WELCOME TO LIKE MY PAGE

Tun ranar Alhamis mu ka saki Murja bisa umarnin kotu – inji kakakin gidan yariKakakin gidan gyaran hali na jihar Kano AC...
18/02/2024

Tun ranar Alhamis mu ka saki Murja bisa umarnin kotu – inji kakakin gidan yari

Kakakin gidan gyaran hali na jihar Kano AC Misbahu Kofar Nassarawa ya shaidawa DAILY NIGERIAN cewa sananniyar ‘yar Tiktok Murja Kunya ba guduwa ta yi daga gidan yari ba.

A cewar sa, tun ranar Alhamis takarda ta zo daga kotu don neman a sake ta, kuma gidan yarin ya sake ta a ranar.

Ya ƙara da cewa kotu ce ta kawo ta ajiya a wajensu, kuma kotu ce ta ce su sake ta.

YANZU-YANZU: Gwamnati ta toshe hanyoyin fitar da abinci ƙasashen waje domin rage tsadar kayayyaki a Najeriya Hukumar han...
18/02/2024

YANZU-YANZU: Gwamnati ta toshe hanyoyin fitar da abinci ƙasashen waje domin rage tsadar kayayyaki a Najeriya

Hukumar hana fasakwauri ta ƙasa, hukumar kula da shige da fice ta ƙasa, rundunar tsaro ta farin kaya, hukumar yaƙi da cin-hanci da rashawa sun bazama kan iyakoki domin hana fita da abinci ƙasashen waje daga Najeriya.

Matakin na gwamnati na zuwa ne a daidai lokacin da ƙungiyoyin ƙwadago s**a ayyana gudanar da zanga-zangar kwanaki biyu saboda matsalar tsadar rayuwar da ake ciki a Najeriya.

Majiya daga fadar shugaban ƙasa ta tabbatar da cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ne ya kafa rundunar aikin haɗin gwiwar domin su daƙile duk wata safarar fita da abinci daga Najeriya a duk kan iyakokin ƙasar dake Borno, Niger, Katsina, Sokoto, Kebbi, da Jihar Jigawa.

Wannan cigaba ya samu ne bayan kammala wani taron gaggawa a tsakanin shugaban ƙasa, da mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima da gwamnonin Jihohi a Abuja fadar shugaban ƙasa, a ranar Alhamis.

A taron, shugaban ƙasa Tinubu ya umarci babban mai ba shi shawara kan tsaro, shugaban ƴan sanda, shugaban rundunar tsaro ta farin kaya, DSS, da su tabbatar da cewa sun bankaɗo tare da rufe dukkan wani wuri da aka ɓoye abinci su yi duk abin da ya dace a kai tayadda za a magance matsalar tsadar abinci da ƙarancinsa a Najeriya.

13/09/2023

DA DUMI DUMINSA: Daga Yanzu Kun Daina koken Babu aikinyi A Nigeria Nan da lokaci kadan zan fitar da talakawa miliyan 136 daga Talauci, zan samar da aikin yi milyan 10 da izinin Ubangiji -inji ministar walwala, Betta bayan ta shiga ofis

Sabuwar ministar kula da walwala da jin dadin jama'a da rage radadin talauci, Dr. Betta Edu ta sha alwashin yin aiki tuƙuru domin sanya farinciki ga yan Najeriya milyan 136 cikin ƙanƙanin lokaci ta hanyar samar da ayyukan yi ga mutum milyan 10 a cikin watanni kadan masu zuwa,

Ministar ta fadi haka ne a lokacinda ta shiga ofis din ta jim kadan bayan ta sha rantsuwar k**a aiki,

Ta ce makasudin kafa ma'aikatar shine kula da walwala da jin dadin yan Najeriya da muka kawar da talauci kuma da izinin Allah shi za ta saka a gaba k**ar yadda shugaban kasa Bola Tinubu yayi wa yan Najeriya alkawari

Daruruwan Daraktoci da ma'aikatun hukumar ne s**a tarbi Misis Betta cikin fara'a da annashawa.

13/09/2023

*WAJABCIN YIWA LIMAMI BIYAYYA ACIKIN SALLAH;*
-
"Zaka samu acikin masallatan mu da dama wasu mutanen suna saɓawa limaninsu acikin sallah, sai kaga mamu ya riga limami ɗagowa, ko kuma ya rigashi tafiya sujjadah, kodai wani abu mak**ancin hakan, sun manta da cewa lallai shi limami ana yi masa biyayya ne idan ba ya wuce ƙa'idah bane acikin sallah"
-
"An sami ruwaya daga anas bin malik (r.a) yace: Manzon Allah ﷺ, yace: lallai abin sani shine; an sanya limami ne domin ayi koyi dashi, idan yayi kabbara, to kuma kuyi kabbara, idan yayi ruku'i, kuma kuyi ruku'u, idan ya ɗago, kuma sai ku ɗago, kuma idan yace sami-Allahu-liman hamidahu, ku kuma kuce; Rabbana walakal-Hamdu"
Sahih Al-Bukhari (1114)
-
"Mamu kala uku ne:
💧Akwai yayan limami.
💧Akwai abokin limami.
💧Akwai ƙanin limami.
-
"Yayan limami shine wanda yake riga limami aiwatar da aiki a cikin sallah, bayan kuma limamin shine jagoransa, wannan kuskure ne"
-
"Abokin limami shine wanda yake aiki bai-ɗaya da limami, yana riƙe masa bamba, wato suna aikata komai a tare acikin sallah, wannan kuskure ne"
-
"Ƙanin limami shine wanda yake jiran limami saiya aiwatar da wani abu a cikin sallah sannan sai shima ya bishi, wannan shine daidai"
-
-
Biyo Instagram ɗinmu 👇
https://instagram.com/hausa.islamic.pictures.quotes?igshid=11g6c9k6osqg5
-
-
Telegram chennel 👇
https://t.me/hausaislamicpicturesquotes

*SAI DA YA AURETA**YAN MATA KU KARANTA WANNAN LABARIN MAI MUHIMMANCI*Wani dan uwane yake bamu wannan labarin a majalisin...
13/09/2023

*SAI DA YA AURETA*

*YAN MATA KU KARANTA WANNAN LABARIN MAI MUHIMMANCI*

Wani dan uwane yake bamu wannan labarin a majalisin karatun Malaminmu Malam Mansur Muhammad (Hafizahullah).
Saurayi da budurwarsa suna zance sai wani abuna saurayin ya faɗi ƙasa,sai ta sunkuya domin ta dauko wannan abin,koda ta dauko saita riƙe wannan abin a hannunta tana masa wasa taƙi bashi abinsa,sai ya riƙeta domin ya karɓi abinsa, koda ya riƙe ta sai ta wanka masa mari,danme sai taɓa mata jiki.
Mutumin nan yayi tunani a ransa wannan ba matar da za'a bari ta kubce bace.
Akarshe dai saida yasan yadda akai ya aureta.
*Wannan labarin akwai darasi a cikinsa dazaku dauka yan mata.*
-Na farko duk wani wanda kika bari yake taɓa miki jikinki to wannan ba maganar aure ne ya kawo shi bah.
Na biyu karkice dan kin hanashi taɓa jikinki zai rabu dake,koda ya tafi sai ya dawo,idanma bai dawo ba Allah zai kawo miki wanda ya fishi.
Na uku muddin zaki bari saurayinki ya dinga taɓa miki jikinki to bakida wata daraja a gurinsa,kiyi iya bakin kokarinki wajan toshe wannan kofar.
Na karshe duk wanda ya kiyaye dokokin ubangiji toh Allah zai kawo masa mafita.

Allah ya shiryemu

~White~ ✍️

Address

TUDUNWADA YARYASA
Tudun Wada

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jarbeerou aleeyou alyaryasy posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category