Media Yauri Tv

Media Yauri Tv Ahmed Sarkin Yaki Yauri

29/11/2025
Anyi jana'zan  Shehu Dahiru Bauchi a jiya Juma'a  Allah ya jiƙan sa da rahama.
29/11/2025

Anyi jana'zan Shehu Dahiru Bauchi a jiya Juma'a Allah ya jiƙan sa da rahama.

AN RANTSAR DA SABBIN SHUGABANNIN HAƊƊAƊIYAR GAMAYYAN  KUNGIYOYIN SHA UKU (13)  MASU HAƊA GIDA .Daga:- Ahmed Sarkin Yaki ...
19/10/2025

AN RANTSAR DA SABBIN SHUGABANNIN HAƊƊAƊIYAR GAMAYYAN KUNGIYOYIN SHA UKU (13) MASU HAƊA GIDA .

Daga:- Ahmed Sarkin Yaki Yauri.

Kungiyoyi Sha-Uku ne s**a dunkule s**a zama ƙungiya ɗaya don kawo sauyi a ɓangaren gine-gine waɗannan kungiyoyi da s**a fara daga masu ɗauko yashi zuwa har masu fenti wanda kungiyar ke zama irinta na farko a tarihin Masarautar Yauri na JAHAR KEBBI .

Bayan kammala rantsuwar k**a aiki Shugaban na riƙo Malam Isah Ibrahim yayi godiya ga al'umman da s**a jajirce wajan kafa wannan kungiya tare da godiya ga Shugaban ƙaramar hukumar mulki ta Yauri Hon Abubakar Sha'aibu Kauran Yauri da miƙa godiya ga Mai martaba Sarkin Yauri Dr Muhammed Zayyanu Abdullahi CON ya kuma yi kira da haɗikai don kawo sauyi hakazalika yayi godiya ga Shugabannin kungiyoyi Sha Uku (13) da s**a shiga wannan haɗaka .

Wakilin Ubandoman Yauri Malam Bello Baba Mak**an Ubandoma yayi kira da shugabanin su zama masu gaskiya da amana .

Shikowa Sarkin walda yayi kera da su zamo masu gaskiya a sana'arsu .

Sarkin Magina yayi jawabin maraba da baƙi tare da fatan Alhairi ga wannan kungiya.

A nasa ɓangare Chairman na Ƴan walda Sanusi Sarki yayi godiya ga Allah da ya kawo musu haɗikai kuma yayi fatan hakan ya zama alhairi ga Al'umma.

Injiniyoyin da s**a hallarci wajan sunyi kira ga Shugabannin su zama masu jajarcewa tare da riƙe gaskiya.

Barister Sharhabilu Jibrin ne ya jagoranci rantsar da dukkani Shugabannin wannan kungiya inda s**a jaddada cewa ba zasuyi aiki da son raiba ko ra'ayi na kashin kansu sai dai zasuyi aiki ba sani ba sabo dare da biyayya ga dokokin wannan kungiya kuma s**a nemi taimakom Allah akan haka.

Shugabannin dai sun haɗa da :-

Isah Ibrahim Chairman
Abdulfatahe Jegfde Vice Chairman .
Babangida Yari Secretary.
Shehu Abubakar LADPN Ass Secretary.
Basiru Abubakar Treasurer.
Zayyanu Abdullahi Fenancial Sec.
Dauda Ahmed PRO.
Jabir Ibrahim Welpere Sec.
Sanusi Hassan Org Secretary.
Abdulmalik Abubakar Auditor.
Ummaru Z***r Legal Adviser.
Aminu Haruna asst Auditor .
Safiyanu Labbo Judge One.
Labaran Aliyu Judge Two.
Abbas Abdullahi Judge Three.

An samu halartar manyan mutane da dukkani mambobi na masu sana'ar haɗa gida k**ar kafinta Magina masu fenti masu haɗa Wuta masu haɗa Ruwa Masu sarrafa ƙarfe masu Gambunan gilashi Masu walda masu Tifa Yashe Masu buga Bulo dadai sauran su.

Muna addu'an Allah ya taya su riƙo amin.

03/10/2025
SANARWA GA JAMA'A!!! MUSAMMAN MUTANE JAHAR KEBBI DA NAJERIYA BAKI ƊAYA.Ana sanar da cewa za a gudanar da gangamin allura...
15/08/2025

SANARWA GA JAMA'A!!! MUSAMMAN MUTANE JAHAR KEBBI DA NAJERIYA BAKI ƊAYA.

Ana sanar da cewa za a gudanar da gangamin allurar rigakafin kyanda da ciyon ƙanwar dusa (Rubella) a Jahar Kebbi, wanda aka tsara farawa daga 4 ga watan Oktoba zuwa 13 ga watan Oktoba, 2025. An shirya gangamin ne don yara masu shekaru daga watanni 9 zuwa ƙasa da shekaru 15, da nufin kare su daga cututtukan kyanda da Ƙanwar susa (rubella), waɗanda dukansu cututtuka ne masu saurin yaɗuwa kuma suna iya haifar da mummunar illa.

Ana sa ran gangamin allurar rigakafin zai yi tasiri sosai ta hanyar hana cututtuka masu barazana ga rayuwa, rage mace-macen yara, da kuma hana yaɗuwar annoba mai girma. Haka kuma, zai kare masu rauni ciki har da jarirai da mata masu juna biyu da kuma mutanen da ke da raunin garkuwar jiki, yayin da yake ƙarfafa tsarin kiwon lafiyar jama'a da kuma bayar da gudunmawa ga manufofin kiwon lafiya na duniya.

Za a ba da allurar kyauta don tabbatar da daidaito wajen samun damar yin allurar da kuma yaɗuwar ta. Wannan shiri ya shafi duk yaran da s**a cancanta, ba tare da la’akari da inda suke ba, asalinsu, ko matsayinsu na zamantakewa. Haɗin gwiwa ne tsakanin NPHCDA, UNICEF, WHO, da sauran abokan haɗin gwiwa, tare da goyon baya mai ƙarfi daga Gwamnatin JAHAR KEBBI da shugabannin al’umma.

A lokacin gangamin, za a yi allurar ne a cibiyoyin kiwon lafiya da aka keɓe da kuma wuraren wucin gadi k**ar gidan shugaban ƙauye ko na shugaban al'umma. Babban abin da gangamin ya fi mayar da hankali a kai shi ne wayar da kan jama'a game da ciwun ƙanwar dusa (rubella) da haɗarinta, musamman ga mata masu juna biyu da jariran da ba a haifa ba.
Haka kuma, gangamin zai yi aiki don kawar da bayanai marasa inganci game da allurar rigakafi da kuma gina amana ta hanyar tattaunawa da al'umma da kafofin watsa labarai. Sanarwar ta ƙare da cewa haɗin gwiwa yana da matuƙar mahimmanci don kare lafiyar yara.

Ku ingata lafiyar Iyalan ku don Samun gobe mai kyau.

Daga:- Ahmed Sarkin Yaki Yauri
Ambassador, National Primary Health Care Development Agency, Kebbi State.

GANGAMIN WAYAR  DA KAI KAFIN  FARA ALLURAR RIGAKAIN CIYON KYANDA DA KANWAR DUSA (RUBELLA) A JAHAR KEBBI .Daga :- Ahmed S...
14/08/2025

GANGAMIN WAYAR DA KAI KAFIN FARA ALLURAR RIGAKAIN CIYON KYANDA DA KANWAR DUSA (RUBELLA) A JAHAR KEBBI .

Daga :- Ahmed Sarkin Yaki Yauri

An gudanar da wani gangamin shirye-shirye na allurar rigakafin kyanda da Kanwar Dusa (Rubella).
kashi na farko a ranar Laraba 13 ga watan Agusta, 2025. Wannan shirin na allurar rigakafin an shirya shi ne don farawa daga 4 zuwa 13 ga watan Oktoba, 2025, kuma an yi shi ne don Yara masu shekaru tsakanin watanni tara 9 zuwa kasa da shekaru goma sha biyar 15.

Ciwo Kanwar Dusa (Rubella) wata cuta ce mai tsanani da ke k**a mata masu juna biyu, inda take da damar haifar da matsala k**ar lahani a zuciya, makanta, lalacewar kwakwalwa, ɓarin ciki, da kuma kurmanta Yara .

Babban burin wannan gangami shi ne magance matsaloli a cikin al'ummomi, dakatar da yaɗuwar cututtukan shan inna, kyanda, da ƙanwar Dusa ( Rubella) tare da ƙarfafa garkuwan jikin yara da kuma ƙarfafa ayyukan rigakafi na yau da kullun.

UNICEF ce ke aiwatar da wannan shiri tare da haɗin gwiwar Hukumar Bunkasa Kiwon Lafiya a Matakin Farko ta Ƙasa, reshen jihar Kebbi.

Bugu da ƙari, ana sa ran Ma'aikatun Watsa Labarai, Lafiya, Ilimi, Tsaro, da sauran masu ruwa da tsaki za su taka rawa wajen tabbatar da nasarar wannan aiki.

Wakilan kafofin yaɗa labarai na gwamnati da masu zaman kansu da jami'ai daga Ma'aikatun Lafiya da Watsa Labarai da ma'aikatan UNICEF da Social Media da sauran abokan hulɗa sun halarci taron.

Address

Yauri
Yelwa
7037

Telephone

+2348061216732

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Media Yauri Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Media Yauri Tv:

Share

Category