Mustapha kamilu

Mustapha kamilu Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Mustapha kamilu, Grocers, Sabon Gari Zaria, Zaria.

HANYOYIN SAMUN SHIGA ALJANNAH (070).BIN ALLAH DA RIKON ZUMUNCI*********************************Hadisi daga Sayyiduna Abu...
29/07/2025

HANYOYIN SAMUN SHIGA ALJANNAH (070).

BIN ALLAH DA RIKON ZUMUNCI
*********************************
Hadisi daga Sayyiduna Abu Ayyub Al Ansariy (ra) yace :

"Wani Mutum yazo wajen Manzon Allah ﷺ sai yace "Ka nuna min wani aiki wanda idan nayishi zai kusantar dani zuwa ga Aljannah kuma ya nisantani daga wuta".

Sai yace masa : "KA BAUTA MA ALLAH KADA KA HADASHI DA KOMAI. KA TSAI DA SALLAH, KA BAYAR DA ZAKKAH, KUMA KA SADAR DA MA'ABOCIN ZUMUNCINKA".

Yayin da mutumin ya juya baya, Sai Annabi ﷺ yace : "Idan yayi riko da abinda aka Umurceshi, lallai zai shiga Aljannah".

Aduba Sahihu Muslim juzu'i na 1, shafi na 43.

BAYANI
********
_Wadannan ayyukan da aka lissafa acikin hadisin nan, ayyuka ne masu sauki ga duk wanda Allah ya saukaka masa. Amma suna da mutukar wahala ga mafiya yawan Mutane.

Ga misali :

1. TSARKAKE BAUTA GA ALLAH : Da yawan mutane (Har ma wasu Maluman) yanzu riya da son duniya da neman girma ya mamaye zukatansu. Tun daga Wa'azi ko Muhadharah zaka ga mutum Qarara yana son nuna cewa shi wane ne ta hanyar zagi ko cin mutuncin wadanda yake da sabanin ra'ayi dasu, koda sun girmeshi a ilimi da shekaru, koda bai yi zamani dasu ba.

2. SALLAH : Itama riya tayi katutu azukatan mutane game da ita. Kaga mutum yana sallah k**ar wanda cinnaka ke cizonsa (Idan shi ka'dai ne).

Amma idan agaban Jama'a ne sai kaga yafi yinta cikin nutsuwa!.

Kaga mutum yana sallah yana karairaya duk wai don ache "Ya iya". Mutane sun mance cewar ikhlasi Allah yake dubawa daga bayinsa ba wai yawan aiki ko kyawunsa a idon mutane ba.

3. ZAKKAH : Ita ma k**ar dai sallar ne. Masu kudin basu cika son fitarwa ba. Idan ma sun fitar da zakkar tasu, atsakanin junansu da iyalansu suke rarrabewa.

Kai ka fitar ka kawo ma iyalaina, nima idan na fitar na kaiwa iyalanka.. Ita ce siffar zakkar wasu masu kudin zamani.

Wani kuma idan ya tashi fitarwa haka zai rarraba Naira dari biyu ko dari biyar biyar.. Maimakon ya dunkule ya bayar.

4. ZUMUNCI : Shima yanzu mutane sunyi watsi dashi.

29/07/2025

ZAGI BA AIKIN ADDINI BANE :

Yanzu mun shigo wani zamani a Nigeria wanda saboda rashin tsoma bakin hukuma acikin al'amuran addini, kusan baka iya bambancewa tsakanin malaman addini da 'yan siyasa wajen cin mutunci da yin karya da yarfe da Qage da cin zarafin duk wanda yake da sa'banin ra'ayi dasu.

Shin 'Yan siyasa ne s**a zarce masu kiran kansu da Malamai wajen tara irin wadannan siffofin, ko kuwa Maluman ne s**a fisu iyawa??.

Shidai addinin nan namu an aikoshi ne ta hannun Annabin da ya zarce dukkan halittu wajen kyawun halaye da dabi'u. Kuma ya nuna mana cewar lallai kyautata halaye shine siffa mafi kyawu da daukaka ga dukkan mabiyansa na gaskiya.

Kamar yadda Allah ya yabeshi da mafi girman kalmomin yabo acikin littafinsa, Allah sai da ya karfafi maganar tasa da rantsuwa, yace : KUMA HAKIKA LALLAI KAI WALLAHI KANA KAN WASU DABI'U MASU GIRMA"..

Kuma Allah din ya horemu mu mabiyansa da cewa, duk wanda ke kaunar Allah da kuma dacewa aranar lahira, sai yayi koyi da wannan Mafificin Annabin ﷺ. Allah yace :

"HAKIKA MAFI KYAWUN ABIN KOYI YA KASANCE GAREKU ACIKIN (LAMARIN) MANZON ALLAH ﷺ GA WANDA YA KASANCE YANA KAUNAR ALLAH DA RANAR LAHIRA.... ".

Kuma Allah yace :

"IDAN KUN BISHI ZAKU SHIRYU"

Acikin Alqur'ani kuwa, a Suratun Nahl ayah ta 125 Allah ya umurci Annabinsa ﷺ da cewa :

"YI KIRA ZUWA GA TAFARKIN UBANGIJINKA CIKIN HIKIMA DA KYAKKYAWAN WA'AZI, IDAN HAR ZAKAYI JAYAYYA DASU, TO KAYI JAYAYYA DASU TARE DA MAFI KYAWUN KALMOMI. HAKIKA UBANGIJINKA SHINE YASAN WADANDA S**A 'BACE DAGA KAN TAFARKINSA, KUMA SHINE MASANIN WADANDA SUKE SHIRYAYYU"

Imamul Qurtubiy (rah) yace : Wannan ayar ta sauka ne agarin Makkah lokacin da akayi umurni da neman zaman lafiya da kafiran Quraishawa. Kuma Allah ya umurcemi Annabinsa ne yayi kira zuwa ga addinin Allah da bin dokokinsa cikin tausasa halaye da tausasa lafazi ba tare da kausasa halaye ko lafazi ba. To hakanan ya k**ata a yiwa Musulmai wa'azi (cikin irin wannan yanayin tausasawar) har izuwa tashin Alqiyamah.

Ibnu Kathee

29/07/2025

S.A.W

29/07/2025

SHIN ZAN IYA YIN ISTIKHARA?

TAMBAYA TA 3220
********************
Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Malam Ina wuni. Inaso na bar aikin da nikeyi yanzu ne. Zan iya yin salatul istikhara? Nagode

AMSA
*******
Wa alaikis salam wa rahmatulLahi wa barakatuhu.

Eh kwarai kuwa. Bisa Sunnah duk lokacin da Musulmi yayi niyyar yin wani muhimmin abu a rayuwarsa, yana da kyau ya fara yin istikharah ya nemi zabin Allah tukunna kafin ya fara gudanar da abun.

Sahabban Manzon Allah ﷺ sunce ya kasance yana koya musu wannan addu'ar istikharah din k**ar irin yadda yake koyar dasu surorin Alqur'ani..

Ga addu'ar istikharah din nan k**ar yadda tazo acikin Sahihu Muslim. Kuma ana yinta ne bayan anyi sallar nafila raka'a biyu, an yiwa Annabi ﷺ salati.

اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْتَخِيـرُكَ بِعِلْمَكَ، وَأسْتَقْدِرُكَ بِقُدْرَتِكَ، وَأَسْأَلُكَ مِنْ فَضْلِكَ الْعَظِيمِ، فَإِنَّكَ تَقْدِرُ وَلَا أَقْدِرُ، وَتَعْلَمُ وَلَا أَعْلَمُ، وَأَنْتَ عَلاَّمُ الْغُيُوبِ، اللَّهُمَّ إِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا الَأمْرَ (وَيُسَمِّي حَاجَتَه) خَيْرٌ
لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، فَاقْدُرْهُ لِي وَيَسِّرْهُ لِي ثُمَّ بَارِكْ لِي فِيهِ، وَإِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا الأَمْرَ شَرٌّ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، فَاصْرِفْهُ عَنِّي وَاصْرِفْنِي عَنْهُ وَاقْدُرْ لِيَ الْخَيْرَ حَيْثُ كَانَ ثُمَّ أَرْضِنِي بِهِ

Allahumma innee 'astakheeruka bi'ilmika, wa astaqdiruka bi qudratika, wa as'aluka min fadhtikal-'Azeemi, fa'innaka taqdiru wa laa 'aqdiru, wa ta'lamu, wa laa 'a'lamu, wa 'Anta 'Allamul-Ghuyubi, Allaahumma 'in kunta ta'lamu anna haadhal amra Khayrun lee fee deenee wa ma'aashee wa 'aaqibati 'amree, faqdurhu lee wa yassirhu lee thumma baarik lee feehi, wa 'in kunta ta'lamu 'anna haathal 'amra sharrun lee fee deenee wa ma'aashee wa 'aaqibati 'amree, fasrifhu 'annee wasrifnee 'anhu waqdur liyal khayra haythu kaana thumma 'ardhinee bihi.

Allah yasa mu dace acikin kowanne lamari, ke kuma Allah ya zaba miki abinda yafi alkhairi gareki duniya da lah

25/07/2025
25/07/2025

SADAUKIN SADAUKAI ﷺ
**************************
Limamin Mala'iku, Jagoran Annabawa da Manzanni, Jarumin Jarumai.. Gwarzon Gwaraza ﷺ.

Kowa yana da gwaninsa, mu kam Kaone namu gwanin, domin kai kadai ne Gwani awajen Allah.

Aranar da kowa ke karbar takardun sak**akon aikinsa, kai kuma tutar Yabo Rabbu yake baka. Tunda kaone kayi jihadi ka tabbatar da kalmar Allah, ka zartar da nufinsa acikon halittunsa.

Ka kora arna daji aranar Hawazinu, bauan yin farko ka karyasu aranar Badar da Hunainu.. Ka watsasu aranar Uhudu da Ahzabu.

Ka Fidda Yahudawan Khaibara sun rushe gidajensu da hannayensu don dole don tsoronka.

Banul Mustalak, da banu Qainuqa'a da Banun Nadheer da Banu Quraizah sun kasa barci saboda razana.. yayin da s**a ci amanar Allah sai takobin Allah yayi aiki akansu.

Hamra'ul Asad da Banu Sulaim da Gatfaana sun gudu sun bar gidajensu da dukiyoyinsu saboda tsoron haduwa dakai.

Abu Jahal da Abu Lahab da Waleedu 'dan Mugheerah da Aasi 'dan Wa'ilu da Ibnu Abi Mu'aitin sun ja dakai sun fadi.

Umayyah da Ubayyu 'ya'yan Khalaf sun sha Qasa agabanka. Kamar yadda Amru 'dan Abdu Wuddin yasha kaifin takobi agabanka.

Abu Rafi'in da Ka'abu 'dan Ashrafu sun shirya maka makirci amma ka magancesu. Babu su babu labarinsu.

'Yan uwa mu gaida Manzon Allah ﷺ jarumin da bashi da tamka.

Assalamu alaika Ya Nabiyyal Awwab. Assalamu alaika Ya Nabiyyal Malahim. Assalamu alaika Ya Nabiyyat Taubati. (sallal Laahu alaika wa 'ala aalika wa sallam).

25/07/2025

ABUBUWAN DAKE TAUYE ALBARKAR DUKIYA :

Kasancewar 'Yan kasuwa da yawa suna yawan rubuto tambayoyinsu zuwa ga Zauren Fiqhu akan wai dukiyarsu tana lalacewa, Jarinsu yana rushewa, shi yasa naga ya k**ata in miko 'Yar nasiha takaitacciya wacce zata kunshi gargadi game da wasu daga cikin abubuwan dake kawo rashin albarkar dukiya.

Abubuwan dake kawo ma mutum rashin albarkar dukiya suna nan da yawa. Amma ga wasu nan daga ciki domin ka kiyaye :

1. Rashin fidda hakkin Allah na wajibi, wato Zakkah. Mutukar mutum ba ya fidda zakkar dukiyarsa, to sai yayi ta fama da asara da rashin albarkar abinda ya tara.

2. Rashin kyautata ma mahaifa : Mutukar kana da wadata amma baka kyautata ma mahaifanka, to dukiyar ba zatayi albarka ba.

3. Rashin kula da Zumunci : Manzon Allah (saww) yace "Duk wanda yake so ajinkirta masa cikin kwanakinsa kuma a yalwata masa cikin arzikinsa, to ya rika sadar da zumuncinsa".

Ashe kenan duk wanda ya watsar da zumuncinsa zai iya haduwa da rariyar hannu.

4. Rashin yin sadaqah ko Kyauta ko ciyar da dukiya domin Allah : Sadaqah takan sanya dukiya ta ninninka kuma tayi albarka. Hakanan yin kyauta ga Ma'abota kusanci shima babban ginshiki ne wajen albarkar dukiya.

5. Yin rantsuwa acikin ciniki : Mutukar Dan Kasuwa zai rika yin rantse-rantse acikin kasuwancinsa tp sai Allah ya tauye albarkar dukiyarsa. Kamar yadda yazo cikin hadisi.

6. Tauye Hakkin Wadanda ke Qasa dakai : Mutukar zaka rika tauye hakkin yaranka na kasuwa ko iyalanka, Ko wulakantar da Musulmai, to tabbas arziki ba zai yi albarka ba. Ko kayi gaba sai ka dawo ba.

7. Aikata Manyan Kaba'irori : Irin su Zina, Luwadi, Cin kudin ruwa, Tsafi, Chamfi, da sauransu. Duk mai yinsu ba zai ga albarkar abin hannunsa ba. Har sai ya tuba ya dena.

8. Qarancin Istighfari : Rashin yawaita istighfari da Salatin Annabi (saww) shima yana kawo ma mutum rashin albarkar dukiya. Amma idan ka yawaitasu sai kaga budi ya samu, Arziki kuma ya yawaita.

9. Wulakanta Sallah : Mutukar dan kasuwa zai rika wulakantar

23/07/2025

HUKUNCIN ZUBAR JINI BAYAN ZUBEWAR CIKI :

TAMBAYA TA 3218
********************
Assalamu alaikum. Allah ya kara wa malam lafiya.
Tambaya: Idan mace tana zubar ciki zata iya yin ibadarta k**ar sallah Azumi Jima'i da sauransu ko akwai adadin kwanaki.

AMSA
*******
Wa alaikumus salam wa rahmatulLah.

Shi jinin dake biyowa bayan zubar ciki, kala biyu ne. Kuma yana dangantuwa ne da yanayin abinda aka haifa ko aka zubar ne.

MISALI :

- Idan abinda aka zubar din ya fito da siffar dan Adam sosai, to jinin da ya biyo bayansa za'a daukeshi ne amatsayin jinin haihuwa. Kuma za'a dena sallah da sauran ibadu kuma za'a kaurace wa jima'i har sai bayan daukewarsa.

- Kuma makurarsa awajen Malaman Malikiyyah ita ce kwanaki 60. Wasu maluman kuma aciki har da wasu daga almajiran Maliku sun tafi akan kwanaki 40 ne.

- Idan kuma bari ne akayi wanda bai wuce na wata daya ko biyu ba, wato irin wanda mace ke zubar da jini zalla ko gudajin jini ko tsoka-tsoka wanda bai yi k**a da siffar Dan Adam ba, to wannan za'a daukeshi ne amatsayin jinin rashin lafiya, wato Istihadha. Don haka wannan ba zai hanata yin sallah ko kusantar mijinta ba.

WALLAHU A'ALAM.

23/07/2025
23/07/2025

HUKUNCIN ZUBAR JINI BAYAN ZUBEWAR CIKI :

TAMBAYA TA 3218
********************
Assalamu alaikum. Allah ya kara wa malam lafiya.
Tambaya: Idan mace tana zubar ciki zata iya yin ibadarta k**ar sallah Azumi Jima'i da sauransu ko akwai adadin kwanaki.

AMSA
*******
Wa alaikumus salam wa rahmatulLah.

Shi jinin dake biyowa bayan zubar ciki, kala biyu ne. Kuma yana dangantuwa ne da yanayin abinda aka haifa ko aka zubar ne.

MISALI :

- Idan abinda aka zubar din ya fito da siffar dan Adam sosai, to jinin da ya biyo bayansa za'a daukeshi ne amatsayin jinin haihuwa. Kuma za'a dena sallah da sauran ibadu kuma za'a kaurace wa jima'i har sai bayan daukewarsa.

- Kuma makurarsa awajen Malaman Malikiyyah ita ce kwanaki 60. Wasu maluman kuma aciki har da wasu daga almajiran Maliku sun tafi akan kwanaki 40 ne.

- Idan kuma bari ne akayi wanda bai wuce na wata daya ko biyu ba, wato irin wanda mace ke zubar da jini zalla ko gudajin jini ko tsoka-tsoka wanda bai yi k**a da siffar Dan Adam ba, to wannan za'a daukeshi ne amatsayin jinin rashin lafiya, wato Istihadha. Don haka wannan ba zai hanata yin sallah ko kusantar mijinta ba.

WALLAHU A'ALAM.

DAGA ZAUREN FIQHU (25/01/1447 20/07/2025).

Address

Sabon Gari Zaria
Zaria

Telephone

+2349060862007

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mustapha kamilu posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mustapha kamilu:

Share

Category